Mawallafi Dr. Abd Ar-Rahman bin Abd Al-Kareem Ash-Sheha د. عبد الرحمن بن عبد الكريم الشيحة



Yüklə 277,39 Kb.
səhifə15/44
tarix07.01.2022
ölçüsü277,39 Kb.
#80427
1   ...   11   12   13   14   15   16   17   18   ...   44
YANAYIN HALITTAR ADAM A.S:

Allah madaukaki ya baiyana cewa ya halicci Adam ne daga asalin qasa, wanda ya baiyanata da Qasa, Allah madaukaki yace: “Lallai Misalin Isa wajen Allah kamar misalin Adam ne, Ya halicceshi daga qasa, sai yace masa ‘kasance' sai ya kasance”

Ko daga Tabo bisa sabawar yanayinsa wajen laushi, Allah yace: “Shne wanda ya halicceku daga tabo sannan ya hukunta wa'adi, da kuma wa'adi na musamman a wajensa, amma sai gashi kuna tantama (2)

Ko bushewa, Allah yace: “Ka tambayesu, shin sune sukafi tsananin wahala wajen halitta ko kuma wadanda muka halitta? Lallai mun haliccesu daga tabo busashshse”.

Kokuwa biyarwa bisa lokuta, daga yunbu zuwa kasko, Allah yace: “Ya Halicci mutum daga yunbu kamar kasko (14)



Kokuma daga baqar qasa, Allah yace: “Kuma haqiqa mun halicci mutum daga baqar qasa….(26)

Duka dai a dukkan yanayin yanakomawane ga tushe daya, Allah madaukaki ya halicceshine daga tabo, daga nan yabi wasu matakai, sannan ya dauki lokacinda Allah yaso ya dauka, sannan sai ya hura masa ruhinsa, Allah madaukaki yana cewa: “Ka tuna sanda Ubangijinka yacewa Mala'iku: ‘Lallai ni zan halicci mutun daga yunbun baqar qasa (28) idan na daidaitashi kuma na hura masa ruhina sai ku fadi kuna masu sujada gareshi (29) sai Mala'iku sukai sujada dukansu (30) sai dai Iblis shine bai kasance cikin masu sujada ba (31)

Sannan sai ya sanya yaduwar mutane daga abinda yake fita daga gadon-bayansu, (wato) daga ruwa abin wulaqanci (maniyyi), bisa wannan haqiqar ne Allah ke cewa: “Shine wanda ya kyautata halittar kowane abu, kuma ya soma halittar mutum daga qasa (7) Sannan ya sanya yaduwarsa daga wani ruwa wulaqantacce (8) sannan ya daidaitashi kuma ya hura masa ruhinsa cikinsa, sannan yasanya maku ji da gani da zuciya, kadanne daga cikinku ke iya godewa (9)

Kuma kamar Yanda asalin mutum yake daga qasa, wanda shine baqar qasa, hakanan makomarsu gareshi ne, kuma mafitarsu daga garetane ranar qiyamah, Allah yace: “Daga cikinta muka halicceku, kuma cikinta zamu maisheku, kuma daga gareta zamu tasheku wani lokaci na daban (55)

KAMANNINSA A.S:

Annabi s.a.w ya baiyana kamannin Annabi Adam a.s, yace: “Allah ya halicci Annabi Adam tsawonsa zira'I 70 ne, sannan yace: tafi kayi sallama ga wadancan mala'ikun, ka saurara, abinda suka gaisheka dashi shine gaisuwarka da zuriyarka, sai yace: “Assalamu alaikum (aminci ya tabbata gareku) sai sukace: Assalamu alaikum warahmatullah (Aminci da Rahmar Allah su tabbata garku) sai suka qara masa ‘da amincin Allah', duk wanda zai shiga Aljannah a bisa kamannin Adam zai shigeta, halittu basu gushe suna tauyewa ba har hanzu (daga kamannin Adam a.s)

GAISUWARKA

Ai abinda zasu gaisheka dashi shine gaisuwarka da gaisuwar zuriyarka abayanka. (SUNA TAUYEWA) ta fuskar tsayi, har hakitta ta daidaita bisa wannan kamanni da aka sani yanzu*.


Yüklə 277,39 Kb.

Dostları ilə paylaş:
1   ...   11   12   13   14   15   16   17   18   ...   44




Verilənlər bazası müəlliflik hüququ ilə müdafiə olunur ©muhaz.org 2024
rəhbərliyinə müraciət

gir | qeydiyyatdan keç
    Ana səhifə


yükləyin