Mawallafi Dr. Abd Ar-Rahman bin Abd Al-Kareem Ash-Sheha د. عبد الرحمن بن عبد الكريم الشيحة



Yüklə 277,39 Kb.
səhifə23/44
tarix07.01.2022
ölçüsü277,39 Kb.
#80427
1   ...   19   20   21   22   23   24   25   26   ...   44
MENENE RUHI

ruhi wani abune da mukai imani dashi saidai bama iya ganinshi amman dai muna shaidawa da akwai shi, kuma ruhi yana daga cikin manyan hujjojin da suke nuna akwai allah tare da raddi ga wadanda suke ganin lallai akwaishi domin suna ganin amfaninshi, shi wani sirri ne daga cikin sirrikan allah madaukakin sarki. Allah madaukaki yana cewa: kuma suna tambayarka game da ruhi, kace, ruhi daga al'amarin ubangijina ne, kuma ba a baku (komai) ba daga ilimi face ka'da (63)

imam raghibul asbahani yake cewa itace wadda ake siffanta gangan jiki da itadomin samun rayuwa, ko ilimi, koko banbance abubuwa masu kyau daga marasa kyau, kuma ya kasance ya kyautata, rashin wadannan abubuwa kuma zai hatfai da duhun kau, kuma itace matattarar duk wani abinda ya shafi ruhi dan adam- kuma yana kasancewa acikin wannan matakin ya zama qasusuwa, sannan a tufatar da nama akan qasusuwan, allah madaukaki yana cewa:" sannan muka halitta tsokar ta zama qasusuwa sannan muka tufatar da qasusuwan da wani nama

kuma allah madaukaki yana cewa cikin qissar uzairu: " kuma ka duba zuwa ga qasusuwa yadda (64) muke motsar dasu, sannan kuma mu tufatar su da (65) nama, to a lokacin da (abin) ya bayyana agare shi, (66) yace: ina sanin cewa lallai allah akan komai mai ikon yine (67) . jaririn yana ci gaba da girma har yakai lokacin da Allah ya qaddara mai fitowa duniya allah madaukaki yana cewa: " zuwa gare shi ake mayarda sanin sa'a, kuma wa'dansu 'ya'yan itace basu fita daga kwasfofinsu kuma wata mace bata yin ciki kuma bata haihuwa face da saninsa, kuma a ranar da yake qiran su (yace) ina abokan tarayyata? sai suce mun sanar da kai babu mai bayar da shaida da hakanan daga gare mu.

hakika Allah madaukakin sarki ya bayyana mana matakan da mutum ke wucewa ta cikinsu yayin halittarshi tin farkonta har zuwa karshe kuma ahakan yana bayyana mana buwayarshi ta alqurani wanda ya saukar dashi akan annabi muhamad tsira da aincin Allah su tabbata a gareshi tin kafin shekara dubu daya da dari hudu kuma hakan ya nuna gaskiyar manzancin da aka aikoshi dashi.

" kuma baya yin magana daga son zuciyarsa.* (maganarsa) bata zamo ba face wahayi ne da ake aikowa(68) .allah madaukaki yace: " kuma lallai ne haqiqa mun halitta mutum daga wani tsantsa daga laka.* sannan muka sanya shi 'digon maniyyi acikin matabbata natsattsiya.* sannan muka halittashi gudan jini sannan muka halitta gudan jinin tsoka, sannan muka halitta tsokar ta zama qasusuwa, sannan muka tufatar da qasusuwan da wani nama, sannan muka qagashi wani halitta dabam, saboda haka albarkun allah sun bayyana, shine mafi kyawun masu halitta.* sannan kuma ku bayan wannan lallai ne masu mutuwa ne.* sannan kuma lallai ku a ranar qiyama za'a tayar da ku(69) .

kuma allah mai tsarki da daukaka acikin wani aya ta daban yake cewa: yaku mutane! idan kun kasance acikin shakka a tashin qiyama to lallai ne mu mun halitta ku daga tur'baya, sannan kuma daga gudan jini, sannan kuma daga tsoka wadda ake halittawa da wanda ba a halittawa domin mu baytana muku, kuma muna tabbatar da abunda muke so acikin mahaifa zuwa ga wani ajali ambatacce, sannan kuma muna fitar daku kuna jarirai sannan kuma domin ku kai ga cikar qarfinku, kuma daga gare ku akwai wanda ke mutuwa, kuma daga cikinku akwai wanda ake mayarwa daga mafi qasqancin rayuwa domin kada yasan komai a bayan sani, kuma kana ganin qasa shiru sannan idan muka sauqar da ruwa akanta, sai ta girgiza kuma ta kumbura kuma ta tsirar da tsiri daga ko wani nau'i mai ban sha'awa.* wancan ne domin lallai allah shine gaskiya, kuma lallai shi yake rayar da matattu, kuma lallai shi mai ikon yine akan komai.* kuma lallai sa'ar tashin qiyama mai zuwa ce, babu shakka acikinta, kuma lallai allah yana tayar da wa'danda suke acikin kaburbura(70) .

kuma allah mai girma yayi gaskiya da yake cewa: " zamu nuna musu ayoyin mu acikin sansanni da kuma acikin rayukansu har ya bayyana agare su cewa lallai (aqur'ani) shine gaskiya, ashe kuma ubangijinka bai isa ba ga cewa lallai shi halartacce ne akan kowani abu ba(71) .

Farfesa kis acikin littafinshi kuma mallamine na ilimin jarirai a wata jamia da take Canada alittafinshi; na ribaci annabi muhamad kuma ban asarar da almasihu ba, na dr abddul mudia addaalati; bana samun wata wahala wajen yadda da cewa lallai qurani maganan allah ne, domin siffofin jarirai da aka ambata cikin qurani baya yuwuwa wani ya sansu a qarni na bakwai, abin da zaa iya samowa mai kyau shine lallai wadannan abubuwan da annabi ya fada cikin qurani lallai wahayinsu aka yimai daga allah.


Yüklə 277,39 Kb.

Dostları ilə paylaş:
1   ...   19   20   21   22   23   24   25   26   ...   44




Verilənlər bazası müəlliflik hüququ ilə müdafiə olunur ©muhaz.org 2024
rəhbərliyinə müraciət

gir | qeydiyyatdan keç
    Ana səhifə


yükləyin