Mawallafi Dr. Abd Ar-Rahman bin Abd Al-Kareem Ash-Sheha د. عبد الرحمن بن عبد الكريم الشيحة



Yüklə 277,39 Kb.
səhifə39/44
tarix07.01.2022
ölçüsü277,39 Kb.
#80427
1   ...   36   37   38   39   40   41   42   43   44
MENENE ALQURANI??

shine zancen allah mala'ika jibrilu ne ya sau'ko da shi zuwa ga annabi (s.a.w), ya sha ban-ban da sauran litattafan da aka sau'kar da abubuwa masu zuwa (wato dalilan da zamu lissafo): shine na qarshen littafan sama, saboda haka ne allah yayi alqawarin karesa don ya wanzu ga mutane har zuwa tashin qiyama tun daga lokacin manzo (s.a.w) har zuwa lokacin mu, allah yana cewa: " lallai mune muka sauqar da ambato (alqur'ani) kuma lallai mu masu kiyayewa ne gare shi." suratul hijri aya ta 9.

kuma yana cikin abinda karanta sa ibada ne, wannan shi ne dalili babba na kiyayesa daga qari da ragi da chanzawa, manzon allah yana cewa: " wanda ya karanta harafi daga littafin allah yana mai kyautata shi yana da misalin lada goma, kada kuce aliflammim harafi ne, sai dai alifun harafi ne, lamun harafi ne, kuma mimun harafi ne." tirmizi ne ya ruwaito 2910.

kuma ana bautawa allah ta hanyar haddace sa a qirji, manzon (saw) yana cewa: lallai duk wanda babu wani acikinshi na daga qurani bai zama komai ba face kaman gida rusasshe. Imam ahmad da tirmizi suka ruwaitoshi kuma yace hadisi ne ingantacce kuma mai kyau.: ana bautawa allah ta hanyar karesa da kuma bada mahimmanci garesa, manzon allah (s.a.w) yana cewa: " mafi alkhairinku shine wanda yasan alqur'ani kuma ya sanar dashi." bukhari ya ruwaito 4739.

ya qunshi dukkanin shari'o'i wanda suke daidaita alumma, wanda yin wannan shari'o'in ya qunshi dacewa ga alumma, allah yana cewa: kuma mun saukar maka da littafi domin bayanin komai da komai da komai……suratun nahli 35.



kuma an 'dauke sa a matsayin tarihi amintacce da yake bayyana yadda addanin annabawa suka sau'ka a layi, da kuma abin da ya faru a garesu tare da mutanensu tun daga adam (a.s) har zuwa tiqewa da annabi (s.a.w): allah ya sau'kar da shi saboda 'dan adam baki 'daya ya samu dacewa, allah yana cewa: " littafi ne mun sauqar zuwa gare ka domin ka fitar da mutane daga duhu zuwa ga haske da izinin ubangijinsu zuwa ga tafarkin mabuwayi, abun godewa." suratul ibrahim aya ta 1


Yüklə 277,39 Kb.

Dostları ilə paylaş:
1   ...   36   37   38   39   40   41   42   43   44




Verilənlər bazası müəlliflik hüququ ilə müdafiə olunur ©muhaz.org 2024
rəhbərliyinə müraciət

gir | qeydiyyatdan keç
    Ana səhifə


yükləyin