Mawallafi Dr. Abd Ar-Rahman bin Abd Al-Kareem Ash-Sheha د. عبد الرحمن بن عبد الكريم الشيحة



Yüklə 277,39 Kb.
səhifə42/44
tarix07.01.2022
ölçüsü277,39 Kb.
#80427
1   ...   36   37   38   39   40   41   42   43   44
MATSAYAR MUSULUNCI AKAN DUKIYA

Dukiya acikin musulunci hakkin Allah ce kuma amana ce da Allah y aba bawanshi kuma abin tambaya ce akanshi, kuma ya wajaba ya ciyar da ita ta hanyar da ya dace a shariance, sannan kuma ya sarrafata acikin alamuran da suke sun halatta, manzan Allah yana cewa: kafafuwan wani bawa bazasu gushe ba ranar qiyama har sai an tambayeshi game da rayuwarshi me ya aikata, sannan iliminshi me yayi dashi, sannan dukiyarshi ta wace hanya ya sameta kuma ta wacce ya ciyar da ita, sannan a tambayeshi game da jikinshi ta yaya ya tafiyar dashi, sunan tirmizy 2417.

Musulunci ya kwadaitar da musulmai wajen neman kudin da zai rike kanshi kuma ya ciyar da kanshi da wanda suke karkashinshi, kuma ya nemi taimakonta akan alamuran rayuwarshi kuma ya zama sababin neman ayyukan lada a lokacin sarrafata, kuma ya watsa ta hanyar alkhairi, manzan Allah yana cewa: mumini mai karfi shine mafi alkhairi kuma mafi soyuwa a wajan Allah sama da mumini mai rauni, amman dukkansu suna da alkhairi, k adage wajen neman abinda zai amfaneka sannan ka nemi taimakon kuma kada ka gaza, idan wani abu ya sameka kada kace da ace na aikata abu kaza da kaza, amman abinda ya kamata kace shine lallai abinda Allah ya qaddara shine kuma abinda yaso shike aikatawa, domin fadin dama yana bude kofar shaidan, sahihu muslim 2052.

Akwai wasu hakkokin da ban banda zakkah, abinda yake wajibi akan musulmi shine ya sarrafa cikin abinda zai iya kawomai abin amfani acikin rayuwarshi ta duniyarshi da lahirarshi, Allah yana cewa: ka nema lahira acikin abinda Allah ya baka, amman kada ka manta rabonka na duniya, sannan ka kyautata ma mutane Kaman yadda Allah ya kyautata maka, kuma kada ka nemi yin taaddanci acikin qasa, lallai Allah baya san yan taadda, suratu qasas, sannan manzan Allah yana cewa: madalla da dukiya mai kyau ga bawa na kwarai, sahihu ibn hibban 3210.

Musulunci ya haramta almubazzarancin dukiya, Allah yana cewa: kada kuyi almubazzanci, domin lallai masu yin hakan sun kasance abokan shaidanu ne, shi kuma shaidan ya kasance mai kafircewa ubangijinshi ne, suratul israi 26-27.


Yüklə 277,39 Kb.

Dostları ilə paylaş:
1   ...   36   37   38   39   40   41   42   43   44




Verilənlər bazası müəlliflik hüququ ilə müdafiə olunur ©muhaz.org 2024
rəhbərliyinə müraciət

gir | qeydiyyatdan keç
    Ana səhifə


yükləyin