Mawallafi Dr. Abd Ar-Rahman bin Abd Al-Kareem Ash-Sheha



Yüklə 241,3 Kb.
səhifə27/29
tarix05.01.2022
ölçüsü241,3 Kb.
#66966
1   ...   21   22   23   24   25   26   27   28   29
KOMAWA ZUWA GA ASALI:

Yana cikin abunda da kayi ittifaki akai kuma tabbatacce shine komai fa yanada asali, sannan kuma duk wani abu da aka kirkiro yana da farko saboda haka mutum asalin su guda ne kuma baban su daya ne Adam amincin Allah ya tabbata a gareshi shine baban mutane baki daya daga tsatson shi ne aka fara halittan mutu har sukayi yawa suka yadu cikin kasa, Allah madaukaki yace yana me bayyana wannan hakikanin: " yaku mutane kuji tsoron ubangijin ku wanda ya halicce ku daga mutum daya ya kuma halitta masa mata daga jikin say a kuma yada daga tsakanin su maza da mata, kuji tsoron Allah wanda kuke rokon sa da kuma sada zumunta domin sa, lallai Allah ya kasance me sa ido akanku (1)" suratun nisa'i.

Hankali yana cewa tunda dai asalin daya ne to ya kamata a dabi'ance ya zama cewa akida daya wacce itace tauhidi da bautan Allah shi kadai ba tare da masa tarayya ba da wani kasancewar haka itace akida da addinin baban mu Adam amincin Allah ya tabbata agareshi ya kasance a kan tauhidi tatacce da bautan Allah, Allah madaukaki yace: " mutane basu kasance ba face al'umma daya sai suka rabu, badan Kalmar ubangijinka ba data gabata da an yanke masu hukunci a tasakanin su cikin abunda suke sabani acikinsa (19)" suratu yunus.

Wannan sabanin kuwa ya samo asali ne daga banabancin tunani da rayuwa da kuma yare kamar yadda Allah madaukaki yace: " daga cikin ayoyin sa shine halittan sammai da kasa da kuma banbancin yarukan ku da fatar ku, lallai cikin haka akwai ayoyi ga masana (22)" suratul rum.

Kuma daga cikin dabi'a ne har wayau wannan sabanin ya haifar da canzawar akida da addini kamar yadda muke gani na banabantan addinai da akidu da bauta kala kala a fadin duniya, ya kasance wajibi ga ko wani mutum da ya koma zuwa ga asali cikin bauta da addininsu na gaskiya wanda suka kansa gabanin shedanu su canza su wanda shine tauhidi tsantsa ga Allah da kuma mika wuya gareshi da jayuwa gareshi da masa biyayya da tsarkaka daga shirka, kuma suyi hukunci da dukkanin abunda ya umurce su dashi cikin rayuwan su baki day aba tare da kebance wani abu ba idan sun kasance sunason tsrira da daukaka da karamci da rayuwa me kyau idan kuma ba haka ba rayuwa zatayi daci a nan duniya da lahira, Allah yayi gaskiya: " alif lam mim, wannan littafin mun saukar maka dashi ne domin ka fitar da mutane daga duhu zuwa haske da izinin ubangijinsu zuwa ga hanyar mabuwayi me godiya (1)" suratu Ibrahim.


Yüklə 241,3 Kb.

Dostları ilə paylaş:
1   ...   21   22   23   24   25   26   27   28   29




Verilənlər bazası müəlliflik hüququ ilə müdafiə olunur ©muhaz.org 2024
rəhbərliyinə müraciət

gir | qeydiyyatdan keç
    Ana səhifə


yükləyin