Mawallafi Dr. Abd Ar-Rahman bin Abd Al-Kareem Ash-Sheha د. عبد الرحمن بن عبد الكريم الشيحة



Yüklə 277,39 Kb.
səhifə12/44
tarix07.01.2022
ölçüsü277,39 Kb.
#80427
1   ...   8   9   10   11   12   13   14   15   ...   44
HALITTAR MALA'IKU:

Halittu ne daga Halittun Allah, ya haliccesu daga Haske, Manzon Allah s.a.w yace: “An halicci mala'iku daga Haske, kuma an halicci aljanu daga harshen wuta, kuma an halicci Adamu daga abinda aka sifanta muku ((wato daga tabo/laaka) Muslim ne ya rawaitoshi.

Al-Maarij: na nufin harshen wuta wandake chakude da baqinta.

Allah ya haliccesu don wasu ayyuka da aka jingina masu su, Allah yace: “Babu wani daga cikinmu face yanada wani matsayi sananne (164) kuma lallai mune masu sahu sahu (165) kuma lallai mune masu tasbihi (166)

Allah madaukaki ya ambaci wasu daga cikinsu, kamar Jibril da Mika'il da Israfil, Allah madaukaki yace: “Duk wansa ya zama maqiyi ga ga Allah da Manzonsa da jibril da mika'il, to lallai Allah mai qiyayya ne ga kafirai (98).

Jibril a.s shine ke sauko da wahayi ga Manzanni don su isar da shari'ar Allah ga Al-ummominsu, Allah madaukaki yace: “Kuma lallai shi (Qur'ani) saukar war Ubangijin talikaine (192) ruhi amkntacce ne ya saukar dashi (193) a zucoyarka don kazo daga cikin masu gargadi (194).

Shi kuma Mika'il a.s shine aka wakiltawa tairrai da ruwa, Israfil kuma busa cikin qaho, busa uku, busan firgici, Allah yace: “Kuma sai akai busa cikin qaho, sai wadanda ke sammai da qassai suka firgita…” da Kuma busar sumewa da ta mutuwa, Allah Madaukaki yace: “Kuma sai akai busa cikin qaho, sai wadanda ke sammai da qassai suka face wadanda Allah ya nufa, sannan aka sake busa ta daban sai gasu suna miqe suna masu kallo (68)

Daga cikinsu akwai Mala'ikan Mutuwa da mataimakansa, Allah yace: “Kuma shine marinjayi akan bayinsa, kuma yana aiko da masu kiyayewa gareku har al'amarinmu yazo, sai Manzanninmu su kasheshi kuma su basu sabawa (61) sannan sai a maidasu ga Allah majibincinsu na gaskiya, ku saurara, gareshi hukunci yake kuma shine mafi saurin masu hisabi (62).

Daga cikinsu akwai masu riqe da Al-arshi, daga cikinsu akwai mala'iku makusanta, Allah yace: “Masihu dan Maryam bazai qi ga zamowa bawan Allah ba hakama Mala'iku Makusanta…”

Daga cikinsu akwai wadanda aka wakilta ga Aljannah, daga ciki kuma akwai wadanda aka wakilta ga wuta, Allah yace: “Yaku wadanda sukai Imani, ku tsamar da kanku da iyalanku daga wuta, itatuwanta sune mutane da duwatsu, akanta akwai Mala'iku masu tsanani masu qarfi, basu sabawa Allah abinda ya umarcesu, kuma suna aikata duk abinda aka umarcesu”.

Daga cikinsu akwai wadanda aka wakilta ga kiyaye bayi, Allah madaukaki yace: “Yanada masu kula dashi agabansa da bayansa suna kiyayeshi daga Umarnin Allah..”

Daga cikinsu kuma akwai wadanda aka wakilta bisa kiyaye ayyukan bayi, Allah madaukaki yace: “Kuma lallai gareku akwai masu kiyayewa (10) Masu karamcine marubuta (11) Suna sanin abinda kuka aikata”

Allah ya haliccesu ne don bautarsa, Allah yace: “Kuma wadanda ke sammai da qassai nasa ne, kuma wadanda ke wajensa basa girman kai bisa ga bautarsa kuma basa gazawa (19) Suna Tasbihi safiya da maraice basa dainawa”

Babu wansa yasan adadinsu sai Allah, Allah yace: “Babu wanda yasan rundunonin Ubangijinka face shi”

Wanda keson qarin bayani sai ya koma ga kebantattun littafai da sukai bayani akan Mala'iku da ayyukansu, ta hanyar Qur'ani da ingantacciyar Sunnah.


Yüklə 277,39 Kb.

Dostları ilə paylaş:
1   ...   8   9   10   11   12   13   14   15   ...   44




Verilənlər bazası müəlliflik hüququ ilə müdafiə olunur ©muhaz.org 2024
rəhbərliyinə müraciət

gir | qeydiyyatdan keç
    Ana səhifə


yükləyin