Mawallafi Dr. Abd Ar-Rahman bin Abd Al-Kareem Ash-Sheha د. عبد الرحمن بن عبد الكريم الشيحة


DALILAN TASHI BAYAN MUTUWA A CIKIN ALQUR'ANI



Yüklə 277,39 Kb.
səhifə28/44
tarix07.01.2022
ölçüsü277,39 Kb.
#80427
1   ...   24   25   26   27   28   29   30   31   ...   44
DALILAN TASHI BAYAN MUTUWA A CIKIN ALQUR'ANI:

alqur'ani ya kwa'daitar da mutum a cikin ayoyi da yawa daga cikinsa akan yin tinani akan asalinsa, wanda ya samar da shi kafin ya kasance wani abu mai iko ne akan dawo da shi bayan ya kasance, allah yana cewa: " kuma mutum yana cewa, shin idan na mutu lallai ne haqiqa da sannu za a fitar dani ina mai rai? * shin kuma mutum bazai tuna ba cewa lallai ne mun halittashi a gabanni, alhali kuwa bai kasance komai ba." suratul maryam aya ta 66-67.

yin tunani akan raya qasa bayan mutuwarta ta hanyar fitar da tsirrai a cikin ta, allah yana cewa: " kuma akwai daga ayoyinsa cewa lallai kai kana ganin qasa qeqasashshiya, to idan mun sauqar da ruwa akanta sai ta girgiza kuma ta kumbura, lallai wannan da ya raya ta haqiqa mai rayar da matattu ne, lallai shi mai ikon yine akan dukkan komai." suratul fussilat aya ta 39.

tunani acikin halittar sammai da qassai wanda sun fi halittar mutum girma, allah yana cewa: shin kuma basu gani ba cewa lallai allah wanda ya halitta sammai da qasa, kuma bai kasa ga halittarsu ba, mai ikon yi ne a kan rayar da matattu?, na'am lallai shi, mai ikon yi ne akan kome." suratul ahqaf aya ta 33.

yin tunani a cikin baccin mutum da kuma farkawarsa wanda daidai yake da rayuwa bayan mutuwa, ana kiran wannan da qaramar mutuwa, allah yana cewa: " allah ne ke kar'bar rayuka a lokacin mutuwarsu, da wa'dannsn da basu mutu ba acikin barcinsu, sannan ya riqe wanda ya hukunta mutuwa akansa, kuma ya saki gudar, har zuwa ga ajali smbatacce, lallai acikin wancan, haqiqa akwai ga mutane wa'danda suke yin tunani." suratul zumar aya ta 44.



kuma wannan aas 'dan wa'il yazo wajen manzon allah (saw) sai yace: ya muhammadu shin allah zai tashi wannan bayan ya rididdige? sai yace: eh allah zai tashi wannan, zai kashe ka kuma ya tashe ka sannan ya shigar da kai wutar jahannama, sai aka saukar da ayoyi: " ashe, kuma mutum bai ga (cewa) lallai mu, mun halitta shi daga maniyyi ba, sai gashi mai yawan husuma, mai bayyanawar husuma. * kuma ya buga mana wani misali kuma ya manta da halittarsa, yace, wane ne ke rayar da qasusuwa alhali kuwa suna rududdugaggu? * kace, wanda ya qaga halittarsu tun farkon lokaci shike rayar dasu kuma shi game da kowace halitta mai ilimi ne. * wanda ya sanya muku wuta daga itace kore, sai gaku kuna kunnawa daga gare shi. * shin, kuma wanda ya halitta sammai da qasa bai zama mai ikon yi ba da ya halitta kwatankwacinsu? eh, zai iya! kuma shi mai yawan halittawa ne mai ilimi. * umurninsa, idan yayi nufin wani abu sai yace " ka kasance " sai yana kasancewa (kamar yadda yake nufi) * saboda haka, tsarki ya tabbata ga wanda mallakar ko wane abu take ga hannayensa, kuma zuwa gare shi ake mayar daku." suratul yasin aya ta 77,78,79,80,81.82-83. hakeem ne ya ruwaito kuma zahabi ya inganta shi.


Yüklə 277,39 Kb.

Dostları ilə paylaş:
1   ...   24   25   26   27   28   29   30   31   ...   44




Verilənlər bazası müəlliflik hüququ ilə müdafiə olunur ©muhaz.org 2024
rəhbərliyinə müraciət

gir | qeydiyyatdan keç
    Ana səhifə


yükləyin