Mawallafi Dr. Abd Ar-Rahman bin Abd Al-Kareem Ash-Sheha د. عبد الرحمن بن عبد الكريم الشيحة



Yüklə 277,39 Kb.
səhifə31/44
tarix07.01.2022
ölçüsü277,39 Kb.
#80427
1   ...   27   28   29   30   31   32   33   34   ...   44
RUKUNAN MUSULUNCI:

KALMAR SHAHADA GUDA BIYU: sune "shaidawa babu abin bautawa sai dai allah, da kuma shaidawa annabi muhammadu (saw) bawansa ne kuma manzon sa ne" wannan shine mubudin shiga musulunci wanda sauran rukunai suke ginuwa akansa, ma'anar "la ilaha illallah" -babu mahalicci ga wannan duniya sai allah. babu mamallaki da kuma mai juya alamura a wannan duniya sai allah.

-babu abin bautawa wanda ya chanchanci ibaba da chanchanta sai dai allah. ma'anar "shaidawa annabi muhammad manzon allah ne" qudurcewa shi bawan allah ne da kuma manzonsa ne allah ya saukar masa da wahayi kuma ya umarcesa da isar da shi ga mutane baki daya da shi ne kuma aka rufe manzanci babu annabi kuma babu manzo bayansa wannan yana hukunta yin biyayya acikin abinda ya umarta da kuma gaskata shi acikin abinda ya umarata da kuma nisantar abinda ya hana.

SALLAH: shine gani tsakanin bawa da ubangijinsa, duk lokacin da musulmi ya tsunduma cikin dadin duniya hasken imani a zuciyarsa ya fara raunana sai ladan ya kira sallah sai hasken nan na imani ya kunnu sai ya kasance cikin ganawa da ubangijinsa ko wane lokacinsa, su ne salloli guda biyar a dare da wuni musulmai suna yin su cikin jama'a a masallaci sai dai in da wani uzuri, sai su san junansu kuma soyayya ta qarfafa a tsakaninsu da kuma hadin kai kuma suna tuntubar halayen sashensu, idan dayansu bai da lafiya sai su je duboshi, idan dayansu na cikin buqata sai su taimakeshi, wanda yake cikin baqin ciki a cikinsu sai su debe masa kewa, wanda yake cikin halin qasqanci sai su nusar da shi, acikin yin wannan abubuwan akai toshe rabuwar kai na alumma, musulmai za su taya bakidayansu ma su zabi ne sashe zuwa sashe babbansu da qaraminsu mai kudinsu da talakansu mai girma acikinsu da kuma marar girma za su zamto daya acikin qanqan da kai ga allah da kuma tsayuwa a gabansa, masu fuskantar alqibilarsa ita kaida kuma a lokaci daya.

ZAKKA: shine wani adadi na dukiya da musulmi mai arziqi yake badawa cikin dadin rai ga yan uwansa talakawa da masakai da kuma masu buqata saboda toshe buqatunsu da kuma wadatarsu daga qasqancin roqo sabo da cika umarnin allah, wajibi ne akan dukkan musulmi da dukiyarsa ta kai adadin zakka ya bada ta, saboda fa'din allah: " kuma ba a umurce su da komai ba, face bautawa allah, suna masu tsarkake addinin gare shi, masu karkata zuwa ga addinin gaskiya, kuma su tsaida sallah kuma su bada zakkah, kuma wannan shine addinin wa'danda suke akan hanyar qwarai. suratul bayyinah aya ta 5.

Duk wanda ya musa su to hakika ya kafirce domin ya hana maabota buqata Kaman masu rauni da talakawa da miskina, kuma wannan ba zakkah bace. kamar yada wasu wadanda basu san musulunci ba suke riyawa cewa- ita zakka wani amfani ne ne da daular musulunci suke karba ga dukkanin wadanda suke qarqashin kulawarta, da haka abin yake to da an wajabtawa kowa da yake rayuwa qarqashin daular musulunci musulmi ne shi ko kuma ba musulmi ne ba ya bayar, kuma abu ne sananne cewa na daga sharadanta bata wajaba ba akan wanda ba musulmi ba.


Yüklə 277,39 Kb.

Dostları ilə paylaş:
1   ...   27   28   29   30   31   32   33   34   ...   44




Verilənlər bazası müəlliflik hüququ ilə müdafiə olunur ©muhaz.org 2024
rəhbərliyinə müraciət

gir | qeydiyyatdan keç
    Ana səhifə


yükləyin