Mawallafi Dr. Abd Ar-Rahman bin Abd Al-Kareem Ash-Sheha د. عبد الرحمن بن عبد الكريم الشيحة



Yüklə 277,39 Kb.
səhifə41/44
tarix07.01.2022
ölçüsü277,39 Kb.
#80427
1   ...   36   37   38   39   40   41   42   43   44
MATSAYAR MUSULUNCI GAME DA ILIMI

Addinin musulunci yayi kwadaitarwa akan neman ilimi da kuma kwadaituwa wajen zargin jahilci sannan kuma yayi tsawatarwa daga gareshi, Allah madaukakin sarki yana cewa: kace shin da mai ilimi da wanda baida ilimi zasu yi daidai ?? suratu zumar aya ta 9.

Sannan Allah madaukakin sarki yana cewa Allah yana daukaka masu imani acikin amman kuma masu ilimi suna da wasu darajoji, suratul mujadala aya ta 16, kuma Allah yayi kwadaitarwa wajen neman ilimi, Allah yana cewa: kace ya ubangijina ka karamin ilimi, suratu Daha aya ta 114.

Hakika musulunci ya girmama ilimi kuma ya bashi hakkinshi sannan ya bayyana matsayinshi alokacin da annabi Muhammad yace: bashi daga cikin alummata wanda baya girmama babba kuma baya tausayin karami, kuma ya bayar wa da duniya hakkinta, musnad na imam ahmad 22807.

Musulunci ya irga neman ilimi da kuma koyar dashi cewa wani sababi ne daya ke mutum ga shiga aljannah, manzan Allah tsira da amincin Allah yana cewa: wanda ya rike wata hanya yana neman ilimi acikinta to Allah zai sawwakemai hanyar zuwa aljannah, sannan malaiku suna shinfida mai fuka-fukansu domin yarda da dalibin ilimi, kuma lallai mai ilimi duk wani abinda yake sammai da kassai yana neman mai gafara har kifaye acikin ruwa, kuma falalar mai ilimi akan mai ibada Kaman falalar wata ne a ranar cikar haskenshi akan sauran taurari, lallai mallamai sune magada annabawa su kuma annabawa lallai basu bar zinari ba ko dirhami ba,sun bar ilimi ne, duk wanda ya daukeshi ya dauki rabo babba, sahihu ibn hibban hadisi mai lamba 88.


Yüklə 277,39 Kb.

Dostları ilə paylaş:
1   ...   36   37   38   39   40   41   42   43   44




Verilənlər bazası müəlliflik hüququ ilə müdafiə olunur ©muhaz.org 2024
rəhbərliyinə müraciət

gir | qeydiyyatdan keç
    Ana səhifə


yükləyin