Mawallafi Dr. Abd Ar-Rahman bin Abd Al-Kareem Ash-Sheha د. عبد الرحمن بن عبد الكريم الشيحة


KASAWAR MUTUM WAJEN JUJJUYA WANNAN DUNIYAR



Yüklə 277,39 Kb.
səhifə9/44
tarix07.01.2022
ölçüsü277,39 Kb.
#80427
1   ...   5   6   7   8   9   10   11   12   ...   44
KASAWAR MUTUM WAJEN JUJJUYA WANNAN DUNIYAR: shima wannan daliline akan samuwar Allah wanda ke jujjuya abubuwa, Allah yana cewa: shin bakaga wanda yayi jayayya da annabi Ibrahim acikin imani da ubangijin shi, dan yaga Allah ya bashi muli, shine annabi Ibrahim yake cemai ubangijina shine mai kashewa kuma mai rayawa, shima yace yana kashea kuma yana rayawa, sai annabi Ibrahim yace mai lallai ubangijina shine mai fito da rana daga gabas, kai kuma ka fito da ita daga yamma, sai wanda ya kafirta aka kureshi, lallai Allah baya shiryar da mutanen da suke azzalumai, suratul baqara aya ta 258.

Ba mamaki daga cikin dalilai akan samuwar Allah shine kure mutane da yayi akan cewa su kawo wani qurani Kaman wannan duk da cewa shine littafi na karshe da aka saukar daga sama, kuma wannan kuren yana nan har tashin kiyama, Allah yana cewa: kace musu da mutane da aljanu zasu taru domin suzo da kwatankwacin wannan quranin to bazasu taba iyawa ba koda kuwa sashinsu zai taimakwa sashi, suratul israi aya ta 88.

Duk mai shakkar smuwar Allah ko yake shakkar annabcin annabi to yazo da wannan kuren da akayi, ko yazo da irin qurani, duk da cewa akwai masu fasaha da balaga da sanin larabci cikin wadanda aka saukar da quranin da yarensu sunyi kokarin hakan amman sun kasa domin kwadayinsu da batar da qurani, kuma kuren da akayi a qurani ya taho ne daki-daki ga wadanda suka musa wannan abin kuma suna ganin cewa shi din maganar mutum ce, Allah yana cewa: ko suna tinanin ka kirkiroshi ne, kace musu suzo da surori guda goma kikirarrukuma ku kira wadanda suke tsaya muku koma bayan Allah indai kun kasance ku masu gaskiya ne, suratu hood aya ta 13.

Allah yana cewa: I kuna cikin shakku game da abinda muka saukar akan bawansu to kuzo da sura daya kumaku kira masu muku shaidah indai kun kasance cikin masu gaskiya, suratu baqara aya ta 23.

Wannan quranin maganar Allah ce wadda ya saukar ga babu karya acikinshi, Allah yana cewa: kuma wannan quranin bai zama kirkirarre daga wanin Allah ba shidai ba komai bane face gasgatawa abinda ke hannunshi kuma ya bayyana abinda ke cikin littafin babu shakka kuma acikinshi kuma saukakkene daga wajen Allah, suratu yunus aya ta 37.

Da ace qurani maganar mutum ce da hakan ya bayyana zahiri cikin tifka da warwara da zaa samu a ayoyinshi, Allah yana cewa: shin basa kula da qurani ne, da ace daga wajen wanin Allah yake da an samu sabani da yawa acikinshi, suratun nisai aya ta 82.

Wannan me zai zama farkon abinda zamu fara tattaunawa akanshi cikin wannan littafin ta bangaren farkon halittar mutum da kuma karshanshi, Allah yana cewa: Allah shine mahaliccin komai da komai, kuma shine wakili akan komai, shine yake da mallakin komai na qasa da sammai, suratuz zumar aya ta 62.


Yüklə 277,39 Kb.

Dostları ilə paylaş:
1   ...   5   6   7   8   9   10   11   12   ...   44




Verilənlər bazası müəlliflik hüququ ilə müdafiə olunur ©muhaz.org 2024
rəhbərliyinə müraciət

gir | qeydiyyatdan keç
    Ana səhifə


yükləyin