Mawallafi Dr. Abd Ar-Rahman bin Abd Al-Kareem Ash-Sheha


ALAKA TAKAI TSAYE TSAKANIN BAWA DA UBANGIJIN SA



Yüklə 241,3 Kb.
səhifə16/29
tarix05.01.2022
ölçüsü241,3 Kb.
#66966
1   ...   12   13   14   15   16   17   18   19   ...   29
ALAKA TAKAI TSAYE TSAKANIN BAWA DA UBANGIJIN SA:

Bauta ga Allah matsayi ce ga rai wacce ta take yantata daga bautan wanin Allah, da it ace aka samun ganawa kai tsaye tsakanin bawa da mahaliccinsa madaukaki, babu wani shamakiko kuma dan tsakiya tsakanin su, kofa tana bude a ko wani lokaci a ko wani wuri kuma cikin kowani yanayi, babu wani me tsaron kufar wanda zai bar wanda yakeso ya shiga ya kuma hana wanda yake so shiga, ka shigar d akanka cikin wannan kofa tunda haka ne ka kuma roki bukatunka da kuma shinfida kukenka da kuma neman taimakon sa akan biya maka su, ka tambaye sa duk abunda kake so ya kuma kwanta maka a rai, saboda kyautar sa bata da iyaka kamar yadda Allah madaukaki ya fada: " idan bayin na suna tambayanka game dani kace masu ina kusa dasu, ina amsa rokon duk wanda ya tambaye ni idan ya tabbaya, to su rokeni kuma suyi imani dani koda zasu shiryu (186)" suratul bakara.

Duk yadda zunubanka sukayi yawa, duk yadda kakai da aikata barna baka da bukatar wani ya zaman maka shamako dan tsakiya tsakanin ka da Allah domin neman gafaran sa, hanyar tsadarwa tsakanin ka da sama abude yake abunda akeso a gareka kawai shine gaskiya da ikhlasi game da hakan, Allah madaukaki yace: " duk wanda yake aikata sabo ko kuma yake zalumtar kansa sa'annan ya nemi gafarar Allah, to hakika zai samu Allah me yawan gafara ne da rahama (110)" suratun nisa'i.

Kuma duk yadda bukatunka suka yawaita da burukanka lallai shine wanda zai yaye maka su da addu'o'inka gareshi da neman bukatuwar ka da kaskantar da kanka a gabansa, Allah madaukaki yace: " ku kira ubangijin ku da rokonsa kuna masu Kankan dakai kuma a boye, lallai bayason masu wuce iyaka (55)" suratul a'araf.

Arzikinsa da yalwar sa basa karewa, sannan kuma kyautun sa basa yankewa, baya hana kowa hanawa daga falalar sa, sannan kuma baya hana kowa kyautar sa, Allah madaukaki yana cewa cikin hadisin kudusi: " yaku bayina! Hakika na haramta zalumci a gareni na kuma sanya shi haramun a tsakanin ku kada kuyi zalumci, yaku bayina! Lallai kuna sabo dare da rana kuma ina gafarta zunubbai baki dayan sa bana damuwa saboda haka ku roki gafarata zan gafarta maku, yaku bayina! Dukkanku masu yunwa ne sai wanda ya ciyar dashi, saboda haka ku nemi ciyarwa ta zan ciyar daku, yaku bayina! Cucarwan ku bazai isa gareni ba bare ku cucar dani haka kuma amfanarwan ku bazai isa gareni ba bare ku amfanar dani da wani abu, yaku bayina! Da ace farkon ku da karshen ku aljanunku da mutanen ku zasu hadu a zuciyar mutum mafi sabo da barna a cikin ku hakan bazai ragemun komai ba cikin mulki na kwatankwacin kwayar zarra, yaku bayina! Da ace farkon ku da karshen ku aljanunku da mutanen ku zasu hadu a wuri daya sais u rokeni dukkanin sun aba kowa abunda ya rokeni a cikin su hakan bazai ragemun komai ba cikin abunda yake wurina sai kamar yadda idan an tsoma allura cikin ruwan kogi aka cirota irin abunda zata rage cikin wannan ruwan kogi, yaku bayina! Lallai ayyukan ku ne yake dawo maku dasu, duk wanda ya samu alheri to ya gode mani wanda kuma ya samu wanin haka to kada ya zargi kowa sai kansa. Hadisi ne ingantacce, muslim ne ya rawaito shi.

Abun bauta na gaskiya bashi da bukatar a samu wani shamako dan tsakiya tsakanin sa da masu bauta masa, lallai yafi kowa sanin su da halin su yana jin maganganun su sannan kuma yasan sirrin su da abunda suka tattauna a tsakanin su cikin a kebance, kuma yawan bukatuwar su bazai hade masa ba tare da banbancin yarukan su da banbantan bukatuwar su, bashi da wata bukata na cewa sai wani ya mika masu bukatuwar su zuwa gareshi, Allah madaukaki yace: " ubangijin ku yace ku kirani zan amsa maku, lallai wanda suke girman kai game da kirana da rook n azan shigar dasu wutan jahannama suna kaskantattu (60)" suratu gafir.

Wannan shine abunda Allah ya bayyanawa bayin sa domin su guje yan fashi madamfara wanda suke son su shiga tsakanin Allah da bayin sa, Allah madaukaki yace: " ku saurara kuji ga Allah ne addini yake tsarkakakke wanda suka riki wanin sa waliyyai suna cewa bama bauta masu si dan su kusantar damu ga Allah kusa, lallai Allah zai masu hukunci a tsakanin su cikin abunda suka kasance na sabani a tsakanin su, lalli Allah baya shiryar da duk wanda ya kasance me yawan karya da kafirci (3)" suratul zumar.


Yüklə 241,3 Kb.

Dostları ilə paylaş:
1   ...   12   13   14   15   16   17   18   19   ...   29




Verilənlər bazası müəlliflik hüququ ilə müdafiə olunur ©muhaz.org 2024
rəhbərliyinə müraciət

gir | qeydiyyatdan keç
    Ana səhifə


yükləyin