Mawallafi Dr. Abd Ar-Rahman bin Abd Al-Kareem Ash-Sheha


HANYA ZUWA GA BAUTAN ALLAH NA HAKIKA



Yüklə 241,3 Kb.
səhifə18/29
tarix05.01.2022
ölçüsü241,3 Kb.
#66966
1   ...   14   15   16   17   18   19   20   21   ...   29
HANYA ZUWA GA BAUTAN ALLAH NA HAKIKA:

Lallai hanya na dabi'azuwa ga bautan Allah na hakika shine rashin hadashi da wani cikin zatin sa da sunayen sa da siffofin sa ko kuma cikin umurnin sa da hanin sa domin rayuwan ka ta kasance gabaki dayanta karkashin abubuwan da Allah yake so, saboda bauta ta ginu ne akan so da jayuwa da kuma biyayya, Allah madaukaki yace: " kace lallai sallata za yanka ta da rayuwa ta da mutuwa ta ga Allah ne ubangijin talikai (162)" suratul an'am.

Idan aka rasa daya daga cikin hakabauta bata zama hakikani bag a Allah, Allah madaukaki yace: " daga cikin mutane akwai wanda suke rike koma bayan Allah alloli kishiyoyi suna sonsu kamar son da sukema Allah, wanda sukayi imani suna tsananin so ga Allah, da za'aga wanda sukayi zalumci a lokacin da zasuga azaba lallai karfi ga Allah yake baki dayanshi kuma lallai Allah me tsananin azaba ne" suratul bakara ayata 165.

Wannan shine abunda Allah ya halicci halittun sa akai baki dayan su, suna masa tasbihi da gode masa zuma jayuwa da dabi'ar su zuwa gare shi kamar yadda ya bada labarin haka madaukakin sarki cikin fadin sa cewa: " sammai guda bakwai da kasa da abunda ke tsakaninsu suna masu tasbihi ga Allah, babu wani halitta face yana yima Allah tasbihi sai dai bakwa fahimtar tasbihin su, lallai ya kasance me yawan hakuri me gafara (44)" suratul isra'i.

Tana masa bauta da kankai dakai a gareshi cikin son zuciyar ta ko kuma ta dole, Allah madaukaki yace: " ga Allah ne dukkanin abunda suke cikin sammai da kasa suke sujjada a cikin son ransu ko kuma ta dole da kuma inuwar su safe da maraice ( 15)" suratul ra'ad.

Abun takaicin shine sauran halittu na dabbobi da tsuntsaye suna jayuwa zuwa ga fidirar su ta halitta suna kin yin shirka da bautawa wanin Allah, Sulaiman dan Dawud Allah ya bashi mulki irin wanda ba'a taba bama wani taliki ba irinsa, Allah ya mallaka masa iska da aljanu, Allah madaukaki yace: " mun mallakawa sulaiman iska me saurin tafiyan wata daya safe da maraice, muka kuma narkar masa da dalma, daga cikin aljanu akwai masu aiki a karkashin sa da izinin ubangijin sa, duk wanda ya kangare cikinsu daga umurnin mu zamu dandana masa azaba da wutan sa'ir (12) suna masa aikin da yake so na gina masallaci da mutum butumi na dabbobi da mutane da gilasai da tukwane manya, kuyi aiki yaku iyalan gidan dawud domin godiya, kadan ne cikin bayina suke da godiya (13)" suratu saba'i.

Kuma Allah ya bashi har wayau fahimtar yarukan kwari da maganar tsuntsaye, Allah madaukaki yace: " sai sulaima ya gaji dawud, sai yace yaku mutane lallai an sanar damu maganar tsuntsaye kuma anbamu komai, lallai wannan falalce bayyananne (16)" suratun namli.

Annabi sulaiman ya kasance me matukar kwadayi na ganin be rasa daya daga cikin rundunan sa da abubuwan da suke karkashin kulawarsa wanda suke yawo a doron kasa gabas da yamma suna zuwa masa da labarinta, Allah madaukaki yace: " mun hadama sulaiman rundununsa daga mutane da aljanu da tsuntsaye daki bayan daki (17)" suratun namli.

Wata rana ya rasasu bega wani tsuntsu ba alhuda-huda a majalisar sa sai yayi inkarin fashin san a rashin zuwan sa yayi alkawarin zai azabtar dashi akan fashinsa indai babu wani uzirin daya jawo hakan, ana nan sai sagshinan yazo masa da labara me girma, sai yayi inkarin labarin be yarda dashi ba inda yake ce masa yaga wata sarauniya ta kasar saba'a da mutanenta suna yima Allah shirka, wannan shine abunda da sulaiman be yarda dashi ba kuma baya tabbatar dashi, Allah madaukaki yace: " sai ya rasa wani tsuntsu a cikin majalisan sa sai yace me yasa banga alhuda-huda bane ko dai ya kasance cikin masu fashi ne (20) sai na azabtar dashi azaba me tsanani ko kuma na yanka shi ko kuma yazomun da dalili bayyananne (21) bayan lokaci kadai sai gashinan yace masa naje wani wurin da baka taba zuwa ba sannan nazo maka da wani labara na gaskiya daga garin saba'a (22) lallai na samu wata mata wacce take mulkan su kuma anbata komai kuma tanada kujera me girma (23) na same ta da mutanen ta suna yima rama sujjada koma bayan Allah kuma shedan ya kawata masu ayyukansu sai ya kange su daga hanya kuma su ba shiryayyu bane (24) bazasuyi ma Allah sujjada ba wanda yake samar da ruwa daga sama ya fitar da tsirrai daga cikin kasa ya kuma san abunda suke boyewa da abunda suke bayyanawa (25) Allah shi kadai yake babu abun bauta da gaskiya bisa cancanta sais hi, ubangijin al'arshi me girma (26)" suratun namli.


Yüklə 241,3 Kb.

Dostları ilə paylaş:
1   ...   14   15   16   17   18   19   20   21   ...   29




Verilənlər bazası müəlliflik hüququ ilə müdafiə olunur ©muhaz.org 2024
rəhbərliyinə müraciət

gir | qeydiyyatdan keç
    Ana səhifə


yükləyin