Mawallafi Dr. Abd Ar-Rahman bin Abd Al-Kareem Ash-Sheha


FARKON FITOWAR SHIRKA A DORON KASA



Yüklə 241,3 Kb.
səhifə20/29
tarix05.01.2022
ölçüsü241,3 Kb.
#66966
1   ...   16   17   18   19   20   21   22   23   ...   29
FARKON FITOWAR SHIRKA A DORON KASA:

Farko mutum ya kasance ne akan addini ta fidira da tauhidi tun daga kan Adam amincin Allah ya tabbata agareshi shirka bata bayyana ba akan wannan doron kasa sai zuwa zamanin mutanen Nuhu Amincin Allah ya tabbata agareshi sakamakon wuce gona da sukayi wurin girmama bayin Allah salihai da waliyyai, hakika mutanen sun sunyi gum aka domin su rika tunantar dasu ibada irinta mutanen su salihai bayan tsawon zamani na jikokin su sai shedan yayi masu wasiwasi dacewa lallai iayayensu basu yi hotun sub a sun ajiyesu sai domin albarkansu da matsayin su, daganan sai mutanen da suka zo bayan su suka bauta masa, sai Allah madaukaki yace: " sai sukace kada kubar allolinku kuma kada kubar wadda da suwa'a da yagusa da nasra (23)" suratu Nuhu.

Ibn abbas kogin ilimin wannan al'umma kuma masanin fassarar alkur'ani Allah ya kara masu yarda yana cewa: wannan gumaka sunayen mutanen kwarai ne salihai na cikin mutanen Nuhu, bayan an halaka su sai shaidan yayi masu wahayi cewa suyi hotunansu su ajiye a wuraren zaman su sais u rika kiransu da sunayen su domin su rika tunawa dasu, sia suka aikata hakan amma ba'a bauta masu ba har sai da wannan mutane suka mutu aka kuma shafe ilimi akan asalin wannan hotuna kafin aka bauta masu koma bayan Allah. Buhari ne ya rawaito shi.

Samuwar shirka ne a duniya ga mabanbanta bauta yana daga cikin dalilai masu kwari akan bukatar mutum ga Allah wanda zai rika bauta mawa kasancewar farkon mutane akan tauhidi suke sai dai bayan tsawon lokaci da nisan su da annabawan su da manzannin su sai shedan ya kawata masu wasu ayyuka wanda suka kasance hanyar bautawa wani abu koma bayan Allah, bautan wani abu koma bayan Allah ya karkasu zuwa ga surori dayawa daga cikin su akwai:



Bautan waliyyai da bayin Allah na kwarai kamar yadda mutanen Nuhu suka aikata, Allah madaukaki yace: " sai sukace kada kubar allolinku kuma kada kubar wadda da suwa'a da yagusa da nasra (23)" suratu Nuhu.

  • Bautan duwatsu da bishiyoyi da mutum butumi da kuma gumaka: kamar yadda mutanen Ibrahim amincin Allah ya tabbata a gareshi suka akata na sassaka dutse da katako su mayar dashi alla suna bauta masa koa bayan Allah, Allah madaukaki yace: " sai yace yanzu zaku rika bautamawa abunda kuka sassaka da hannun ku bayan Allah shine wanda ya halicce ku da abunda kuke aikatawa" (suratu safat ayata 95-96).

  • Bautan taurari da rana da wata kamar yadda mutanen sarauniyar saba'a na zamanin Sulaiman amincin Allah ya tabbata agareshi wanda alhuda huda ya bashi labara akai kamar yadda muka ambata a baya, Allah madaukaki yace: " na same ta da mutanen ta suna yima rana bautama koma bayan Allah kuma shedan ya kawata masu ayyukan su ya kange su daga hanya lallai su ba shiryayyu bane (24)" suratun namli.

  • Bautar mutum kamar yadda mutanen fir'auna suka aikata, Allah madaukaki yace: " fri'auna yace yaku taron mutane shin na sanar daku wani allah ne bayana, ya hamana hadamun tsani ka tayar mun dashi zuwa sama naje na tarar da Allamn Musa lallai ina tsammanin shi cikin makaryata (38)" suratul kasas.

  • Bautan dabbobi kamar yadda mutanen Musa amincin Allah ya tabbata agareshi sukayi, Allah madaukaki yace: " sai ya fitar masu da dan maraki wanda ya kera me yin sauti sai sukace wannan shine allanku da musa wanda ya manta ya fada maku hakan (88) shin basa ganin cewa baya amsa masu Magana sannan kuma baya cucar dasu komai ko kuma amfanar dasu da komai ba (89) kuma hakika Haruna yace masu gabanin haka yaku mutanena lallai an jarabe ku ne da wannan lallai ubangijin ku shine Allah me rahama saboda haka ku bini kuma kumin biyayya cikin umurni na (90) sai sukace bazamu daina bauta mas aba har sai musa yadawo (91)" suratu daha.

  • Bautan annabawa da manzanni kamar yadda yahudawa batattu da kiristoci suka aikata, Allah madaukaki yace: " yahudawa sunce Uzairu dan Allah ne, suma kiristoci suka ce mahihu dan Allah ne, wannan maganar su ce kawai da bakunan suna maganane irin maganar kafiran da suka gabace su, Allah ya tsine masu dan me suke bacewa hanyar gaskiya suke komawa hanyar karya (30)" suratu taubah.

  • Bautan bishiyoyi kamar yadda mutanen shu'aibu amincin Allah ya tabbata agareshi suka aikata, Allah madaukaki yace: " mutanen madyana sun karyata manzanni (176) lokacin da shu'aibu yace masu shin bazakuji tsoron Allah ba (177) lallai ni manzo ne zuwa gare ku amintacce (178) kuji tsoron Allah kumun biyayya (179)" suratul shu'ara'i.

  • Bautan duwatsu da bishiyoyi da mutum butumi da gumaka kamar yadda mushrikan larabawa suka aikata, Allah madaukaki yace: " shin bakuga lata ba da uzza (19) da mana na ukun su (20) shin ku kuke da mazaje shi kuma yake da mata (21) lallai kam wannan rabo ne na zalumci (22) basu kasance ba face sunane kawai wanda suka rada masu kuke kiransu dashi ku da iyayen ku wanda Allah be saukar da wani dalili ba akan haka, babu abubda suke bi illa kawai zato da son zuciyar su, kuma hakika shiriya yazo masu daga wurin ubangijin su (23) suratun najmi.

Kenan asalin dukkanin mutanen da suka gabata shine tauhidi fadawa cikin shirka ya samo asali ne daga girmama salihan bayin cikin su, sai suka riki hotunan su da sassaka su saboda tunawa dasu na abunda suka kasance a ciki na ayyuka na kwarai da dabi'u masu kyau, wannan shine abun da manzon Allah Muhammad s.a.w ya bayyana ma Ummu Habiba da Ummu salma lokacin da suka ambata mashi cocin da suka gani a kasar habasha wand aake kira mariya, a cikin su akwai hotuna, sai manzon Allah s.a.w yace: " wa'innan sun kasance idan wani mutumin kwarai cikin su yam utu sai su gina masallaci akan kabarin sa, sai kuma su yi masa wannan hoto, wannan sune mafiya sharrin mutane a wurin Allah ranan alkiyama" sahihu muslim.


Yüklə 241,3 Kb.

Dostları ilə paylaş:
1   ...   16   17   18   19   20   21   22   23   ...   29




Verilənlər bazası müəlliflik hüququ ilə müdafiə olunur ©muhaz.org 2024
rəhbərliyinə müraciət

gir | qeydiyyatdan keç
    Ana səhifə


yükləyin