Mawallafi Dr. Abd Ar-Rahman bin Abd Al-Kareem Ash-Sheha



Yüklə 241,3 Kb.
səhifə28/29
tarix05.01.2022
ölçüsü241,3 Kb.
#66966
1   ...   21   22   23   24   25   26   27   28   29
KIRA DA WA'AZI:

Daga nan ga kira zuwa ga wand aba musulmai ba masu fahimtar cikin su da hankali kan karatun fassarar ma'anar alkur'ani me girma kundin tsarin mulkin musulunci da sannu zasu samu mafita ga dukkanin matsalolin su da matsalolin duniya na siyasa da tattalin arziki dana zamanta kewa da dabi'u, sai dai yana bukata daga gare su da suyi amshe shi su kuma yi nazari akan sa suna masu nisanta daga son zuciyar su da kabilanci na addini saboda kasancewar sa kundun tsarin mulki kuma ansanya shine domin mutane baki dayan su har zuwa tashin alkiyama bawai na larabawa bane kawai kamar yadda wasu suke ikirarin haka, hukunce hukunce sa da dokokin sa sun game komai na bangaren rayuwa kuma yayi daidai da ko wani irin zamani da wuri, kuma da sannu zasu samu a cikin sa dukkani amsoshi gamsassu game da tambayoyin da yake bijiro wa cikin zukatan mutane da yawa wand aba musulmai ba akan rayuwa da mutuwa da abunda ke bayan sa, ( a shirye muke mu kara maka taswiri na alkur'ani idan kana bukata), dukda kasancewar karshen sakonni cikin littattafai ya kasance littafi ne me girmama sauran addinai na yahudawa da kiristoci kuma yana hani game da barin zagin akidun wasu addinan mutane na daban, Allah madaukaki yace: " kada ku zagi abunda suke bautama wanin Allah ai su zagi Allah saboda zalumci da rashin ilimi, da Kaman haka ne muka kawatama ko wace al'umma aikin ta sa'annan zuwa ga ubangijin su zasu koma yaba su labarin abunda suka kasance suna aikatawa (108)" suratul an'am.

A yayin nazari cikin wannan alkur'ani zasu same shi me bi a sannu sannu cikin maganganun sa me saukin shiga zuciya da gamsar da hankula cikin shari'ar sa da hukunce hukuncen sa, ALllha yayi gaskiya cikin fadin sa cewa: " shin bazasuyi nazari ba cikin alkr'ani da ace daga wurin Allah yake da sun samu sabani da yawa acikin sa (82)".

Maganar ta sallamawa ce da aiki da ita, kasan wanene Allan ka na gaskiya wanda zaka natsu da bautan masa kuma ka rika jin dadin munajati dashi domin samun natsuwa da kwanciyar hankali cikin nan duniya da kuma dammawa cikin aljanna me dawwawa a lahira, ka nisantar da kanka daga jahilci da makauniyar koyi wacce bataji kuma take rafkanar da zuciya wacce bazata taba barinka b aka amshi gaskiya kuma zuciyar ka taji dadi dashi domin ka isa zuwa gaskiya da kuma sanin Allah madaukaki, lallai dama ce wanda ya wajaba ka ribace ta matukar kofar tuba yana bude da komawa zuwa ga Allah tun gabanin mutuwa ta zo maka, a lokacin nadama bata amfani, a wurin Allah kuma baka tsoron zalumci ko kuma kunge kayi murna da abunda zai farnta maka yadda zai gafarta maka dukkanin zunuban ka baki daya wand aka aikata da kura kurai saboda haka kada wannan dama ta wuce maka, Allah madaukaki yana cewa: " kace ma wanda suka kafurta idan suka bar kafurcin nasu za'a gafarta masu abunda suka aikata a baya amma idan suka ci gaba to hakika sunnar mutanen farko ya gabata (38)" suratul anfal.

Lallai ina cikin yarda cikakke cewa dayawa basu yarda da abunda suke ciki ban a bautan wanin Allah daya mabuwayi wanda ya halicce su kuma ya samar dasu daga rashi musamman ma masu bautan halittu irinsu kamar dabbobi da dabi'a, lallai zakayi mamaki matuka ga wanda suke neman abun bauta mutum me hankali da wayewa zai rika bautan wuta da shedan da makamantan haka, hakika zuciyar su ta kurmance kafin ganin su game da bautan Allah na gaskiya, Allah yayi gaskiya: " lallai ba idanuwa bane suke makance wa zuciya da take cikin kiraza ne take makancewa (46)" suratul hajj.

Duk wanda yakeson gaskiya Allah zai datar dashi idan Allah yasan gaskiyar niyyar sa akan haka, Allah madaukaki yace: " duk wanda yayi imani da Allh zai shiryar da zuciyar sa, Allah masani ne ga dukkan komai (11)" suratul tagabun.

Kada ka kasance cikin masu girman kai game da gaskiya da masu dagawa akan mutane sai gaskiya ta bace cikin zuciyar ka, da shamaki a idanun ka yadda bazaka ga komai ba sai abunda yayi daidai dason zuciyar ka kuma hakan ya zama sanadin halakar ka, Allah madaukaki yace: " da sannu dan shafe ayoyi nag a mutanen da suke girman kai cikin kasa batare da gaskiya ba, idan sunga ko wani aya basa imani dashi, idan sunga hanyar shiriya basa riketa a matsayin hanyar bi, idan kuma sunga hanyar bata da rudu sais u riketa a matsayin hanyar bi, hakan ya kasance ne saboda sun kasance suna karyata ayoyin mu kuma suna gafala daga garesu (146)" suratul a'araf.

Ka koma zuwa ga abun bautanka na gaskiya zaka same shi me rahama a gareka sama da mahaifiyar ka wacce ta dauki cikin ka ta kuma shayar dakai da renon ka, Allah madaukaki yace: " shine wanda yake yabon ku da ambatan ku kuma mala'ikun sa suna maku addu'a domin ya fitar daku daga duhu zuwa haske, kuma ya kasance me rahama ga muminai a lahira (43)". Suratul ahazab.

Yana farin ciki da tuban ka da komowa zuwa ga bautan sa kamar yadda manzon Allah s.a.w ya fadi cewa: " lallai Allah yana farin ciki da tuban bawansa bayan yayi zunubi sama da farin cikin mutumi matafiyi cikin sahara tare da abun hawan sa wanda ya daura mata abincin sa da ruwan shansa kawai sai ta bace masa ya cire rai da rayuwa tabbas mutuwa kawai zayyi ya zauna yana jiran lokacin sa sai barci ya kwashe shi yana bude ido sai yaga wannan abun hawar nasa ta dawo irin murnan da wannan mutumi zayya to lallai Allah yafi murna da tuban bawan sa sama dashi" sahihu muslim.


Yüklə 241,3 Kb.

Dostları ilə paylaş:
1   ...   21   22   23   24   25   26   27   28   29




Verilənlər bazası müəlliflik hüququ ilə müdafiə olunur ©muhaz.org 2024
rəhbərliyinə müraciət

gir | qeydiyyatdan keç
    Ana səhifə


yükləyin