Tafarkin sunnah


Wai Sun Karvo Mazhabarsu Daga Ma’asumai



Yüklə 2,75 Mb.
səhifə10/51
tarix28.10.2017
ölçüsü2,75 Mb.
#17506
1   ...   6   7   8   9   10   11   12   13   ...   51

2.7 Wai Sun Karvo Mazhabarsu Daga Ma’asumai

Xan Shi’ar ya ce: Fuska ta huxu, ita ce, ‘yan Shi’ah Imamiyyah sun karvo mazhabarsu ne daga imamai ma’asumai waxanda aka sani da falala da ilimi da gudun duniya da tsentseni, masu shagalta kowane lokaci da ibada da addu’a da karatun Alqur’ani, da dawwama a kan wannan tun yarantansu har mutuwarsu. Daga cikinsu akwai masu koya wa mutane ilimi, kuma a kansu ne suratul-Insan ta sauka. Da ayar tsarkin Ahlul-Baiti da wajabcin son su, da ayar la’ani da sauransu. Ali Raliyallahu Anhu ya kasance yana yin raka’a dubu kowane yini da dare kuma yana karanta Alqur’ani duk da jarabar yaqi da ya yi fama da ita.


2.7.1 Imami na Farko:

Sayyidina Ali Raliyallahu Anhu

Xan Shi’ar ya ce: Imami na farko shi ne Ali Raliyallahu Anhu wanda shi ne mafificin bayi bayan Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama. Allah Ta’ala ya kira ran Manzo wurin da ya ce:

ﭽ ﯰ ﯱ ﭼ آل عمران: ٦١

Da kawunammu da kawunanku. Al-Imran: 61

Manzo ya qulla ‘yan’uwantaka da shi, kuma ya aurar masa da xiyarsa. Falalarsa ba a voye take ba, mu’ujizozi da yawa sun bayyana a hannunsa har wasu mutane suka ce shi ma abin bautawa ne, ya kashe su. Wasu kuma suka bi maganarsu kamar Gulatu da Nusairiyyah.


Martani:

Ba mu yarda cewa, ‘yan-sha-biyu sun karvo mazhabarsu daga Ahlul-Baiti ba, ba su ba ba sauran ‘yan Shi’a ba. Su da suka sava wa Ali Raliyallahu Anhu da Ahlul-Baiti a cikin duk asullansu da saka sava wa Ahlus-Sunnah a cikinsu! Abin da ya tabbata daga Ali Raliyallahu Anhu da Ahlul-Baiti shi ne tabbatar wa Allah Ta’ala da siffofin da ya tabbatar wa kansa da imani da qaddara da tabbatar da halifancin halifofi uku na farko, da tabbatar da falalarsu, kuma duk a nan ‘yan-sha-biyu sun sava ma su. An samu riwayoyi da yawa game da wannan cikin littaffan malamai ta yadda waxannan riwayoyin na sa mutum ya kai ga samun ilimi na yaqini cewa Ali da Ahlul-Baiti ba su tare da ‘yan-sha-biyu.

‘Yan-sha-biyu kuma harwayau sun sava a tsakanin junansu game da abubuwan da suka shafi sifofin Allah Ta’ala da imani da qaddara, da sauran abubuwan da suka shafi asullan addininsu. To wace magana ce suka karvo daga imamansun da ba su kuskure? Har ma abin da ya shafi imamancin suna da Savani da yawa cikin sa.

Kai har ma game da Mahadin su ke jira suna da savani. Daga cikinsu akwai masu cewa Ja’afar xan Muhammad ne. Wasu kuma sun ce a’a xansa ne Musa xan Ja’afar. Akwai kuma waxanda suka ce Muhammad xan Abdullahi xan Hasan shi ne Mahadin. A yayin da wasu suka ce Muhammad xan Hanafiyya ne. Wasu kuma sun ce Ali xan Hassan xan Husain ya yi wasici ne ga xansa Abu Ja’afar, wasu kuma na cewa ga xansa Abdullahi. Haka dai a kowane imami sai da suka yi savani.

Wasu abubuwan da ya faxa sharholiya ce kawai, irin cewar da ya yi, a kansu ne aka saukar da Suratul Insan. Domin wannan surar a Makka ta sauka tun kafin auren Ali da Nana Fatima. Ita ma ayar tsarkake Ahlu-Baiti da tafi da qazanta daga gunsu, tattare kasancewarta tana magana ne a kan matan Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama, ba labari take bayarwa ba, umurni ne kamar irin umurni da aka yi wa musulmi baki xaya da yin alwala kuma Allah ya yi irin wannan maganar a Suratul Ma’ida ya ce: Allah ba ya nufin ya quntata ma ku, amma yana son ne ya tsarkake ku. Al-Ma’ida:6.

Sai cewar da ya yi wai, Ali na sallah raka’a dubu kowace rana. Wannan ya nuna bai ma san mene ne falala ba. Domin Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama bai tava wuce raka’a goma sha uku a dare xaya ba kamar yadda ya zo a cikin Buhari da Muslim. A cikin Buhari da Muslim kuma, Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama ya ce: “Mafificin tsayuwar dare shi ne na Annabi Dawuda Alaihis Salamu; ya kan yi baccin rabin dare, sannan ya yi tsayin sulusi, sannan ya sake baccin sudusi”.

Haka shi ma cewar da ya yi, wai, Ali shi ne mafificin talikai bayan Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama, cika baki ne kawai, ba hujja.

Hadisin da ya kawo cewa, Annabi Sallallahu Alaihi Wasallama ya qulla ‘yan’uwantaka tsakaninsa da Ali shi ma irin wancan ne. Don Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama ya qulla tsakaninsa da kowa ba, bai kuma yi tsakanin Muhajirai wasu-wasu ba, ko tsakanin Ansarai wasu-wasu. Abin da ya tabbata a sahihan hadissai shi ne, ya yi wannan haxin zumunci ne tsakanin Muhajirai da Ansarai, kamar yadda ya yi a tsakanin Sa’adu xan Rabi’u da Abdurrahman xan Aufu, da kuma tsakanin Salmanul-Farisi da Abud-Darda’i.

Sai cewa, Allah ya sanya Ali shi ne ainin Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama in da ya ce: Da kawunanmu da kawunanku. Ali Imran: 61. Wannan in da Allah ya ce ne: In da ma lokacin da kuka ji shi (qazafin) muminai maza da mata sun zaci alheri ga kawunansu (yana nufin ga ‘yar uwarsu kuma uwarsu A’ishah). An-Nur:12. Ka ga duk muminai ‘yan’uwan juna ne sashensu majinvinta sashe.

Aurar ma sa da Fatima kuma daraja ce kamar aurar ma Usman da Ummu Kulsumi da Ruqayyatu. Don haka ma ake ce ma Usman Dhun-Nuraini mai haske biyu. Haka auren ‘yar Abubakar da Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama ya yi daraja ne ga Abubakar. Haka auren xiyar Umar shi ma daraja ne ga Umar xin. Saboda haka duk halifofinsa huxu Allah ya ba su wannan falalar ta surukuta da shi Sallallahu Alaihi Wasallama.

Sai cewar da ya yi Ali na da mu’ujizoji masu yawa. Wataqila yana nufin karamomi. Wannan ko ba wani kayan gabas ne ba ga Ali, don ya fi daraja a kan mafi yawan waxanda suka samu karamomin, cikinsu har da jahilai. Kuma don wasu sun xaukaka shi har sun ce ma sa Allah, wannan bai zama daraja. Ai duk mu’ujizar da ta bayyana gare shi in har akwai to, ta Annabi Sallallahu Alaihi Wasallama ta fi ta, amma babu mai hankalin da ya tava ce ma sa Allah. Shikenan don wasu sun ce Annabi Isah Allah ne sai a fifita shi a kan Annabi Muhammadu Sallallahu Alaihi Wasallama? Ina banbancin shirmen masu ce ma sa Allah da na Harijawa masu kafirta shi? In ka ce saboda xaukakarsa ne da zamansa na Allah waxancan suka ce shi ne Allah, wani zai ce, saboda yawan zunubansa da miyagun ayyukansa Harijawa suka kafirta shi. In ka ce saboda rashin hankalin Harijawa ne suka kafirta shi, to, su ma waxancan ‘yan Shi’ar saboda rashin hankalinsu ne suka Allantar da shi. Kuma tare da haka Harijawa sun fi ‘yan Shi’ah hankali da riqon addini sau ba iyaka, sun fi su kafa hujja mai xan sauraruwa.

A wurin Ali kansa gara Harijawa da Gulatun ‘yan Shi’ah masu Allantar da shi.


2.7.2 Hasan da Husaini

Xan Shi’ar ya ci gaba da cewa: Xan Shi’ar ya ci gaba da cewa: ‘Yayansa biyu su ne jikokin Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama, kuma su ne shugabannin matasan aljanna. Imamai biyu ne bisa ga nassin Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama. Su ne suka fi kowa ilimi da zuhudu a zamaninsu. Sun yi jihadi a tafarkin Allah yadda ya kamata har aka kashe su. Hasan ya sa rigar gashin dabbobi a qarqashin tufafinsa masu tsada ba tare da mutane sun san da haka ba. Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama watarana ya xora Husaini akan cinyarsa ta dama ya xora xansa Ibrahimu akan cinyarsa ta hagu, sai Jibrilu Alaihis Salamu ya sauko ya ce ma sa: “Allah ya ce ba zai haxa ma ka su ba, don haka ka zavi xayansu”. Sai Manzo ya ce, in Husain ya mutu zan yi kuka, Ali ma ya yi, sannan Fatima ta yi, amma in Ibrahim ya mutu to, ni kaxai zan yi kuka, sai ya zavi mutuwar Ibrahim ya kuwa mutu bayan kwanan uku. Wannan ne ya sa, inji xan Shi’ar duk lokacin da Husaini ya zo wurinsa sai ya ce maraba da wanda na fansa da xana Ibrahim.



Martani:

Tabbataccen abu shi ne Hasan shugaba ne da Allah zai kimtsa shirin musulmi da shi a lokacin tashin hankali da rikici a tsakaninsu. Haka Sallallahu Alaihi Wasallama ya faxa. Kuma ta tabbata cewa, Annabi Sallallahu Alaihi Wasallama kan xora Hasan a xaya cinyarsa, Usamatu xan Zaidu a xaya, ya ce: “Ya Allah! Haqiqa ina son su, kai ma ka so su, ka so wanda yake son su”.

Wannan kuwa na nuna abin da Hasan ya yi na sauka daga muqami da rashin ci gaba da tilasta waxanda ba sa son shugabancinsa shi ne abin da Allah da Manzo ya fi so. Yin hakan ba aibi ne ba, ba kuma keta alfarmar gaskiya ne ba kamar yadda ‘yan-sha-biyu ke gani. Wannan shi ya sa Annabi Sallallahu Alaihi Wasallama ya so su shi da Usamatu. Ka ga ai ko Usamatu yana cikin masu qyamar fitina da yaqi a lokacin tashin hankali, shi ya sa bai shiga cikin rundunar Ali ko ta Mu’awiyah ba. Shi kuma Hasan a kullum yana ba mahaifinsa shawarar barin yaqi. Savanin abin da ‘yan-sha-biyu ke cewa, Hasan ya tozarta musulmi da ya nemi a zauna lafiya. In da a ce, akwai wani shugaba da ya wajaba kowa ya bi shi don yana ma’asumi kuma duk wanda ya hau ba shi ba mulkinsa vatacce ne, ai da wannan sulhin da Hasan ya yi ya zama varna kamar yadda suke cewa. To, da haka ne ko za a yabi Hasan a kan wannan gyara? Sai dai ko a ce an yi masa uzuri don rauni ko kasawa. Hasan kuma ya fi Husaini damar yin yaqi, amma ya bar shi. Allah na xaukaka darajar muminai ko a aljannan wani ya fi wani. Tattare da kasancewar yardar Allah ta tabbata a gare su baki xaya.

Sannan idan har Annabi Sallallahu Alaihi Wasallama ne ya nassanta zamansu imamai, to, ba wani amfani ga nassanta su da Alin ya yi. Mu dai mun san Hasan da Husaini abar qaunar Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama ne a duniya, kuma ya saka su a cikin bargo ya yi masu addu’a. Suna da darajoji masu yawa, da matsayi babba a wurin musulmi. Amma cewa, sun fi kowa ilimi ko gudun duniya wannan cika baki ne kawai, ba dalili.

Sai cewar da ya yi wai, sun yi jihadi har suka bar duniya. Abin da duniya ta sani shi ne, Hasan ya kira Mu’awiyah da kansa ya damqa masa ragamar shugabancin musulmi duk da kasancewar rundunar Iraqi duka tana tare da shi. A tarihinsa bai tava zavin yaqar musulmi ba. A lokacin mutuwarsa kuma wasu sun ce an saka masa guba ne a abinci. Ta haka ya samu xaukakar yin shahada kenan. Amma dai bai mutu yana riqe da makami ba, sam. Shi kuma Husaini ya fita da nufin yaqi, amma a zatonsa zai samu goyon bayan ‘yan Shi’ar Iraqi. Da ya lura da cin amanarsu dai ya canza niyya, ya buqaci a bar shi ya koma gida, ko ya je jihadin kafirai ko ya tafi da kansa wurin sarki Yazidu. Rashin samun damar yin ko xaya daga cikin abin a ya nema shi ya sa ya yi yaqi kuma har aka kashe shi akan zalunci, ya yi shahada.

Shi kuma Hasan da xan Shi’ar ya ce wai, yana sanya tufan gashin dabbobi a qarqashin tufan auduga, wannan ba wata daraja a cikinsa, don kamar shigen cewa, Ali na raka’a dubu a kullum ne. Kawai abin da za mu ce shi ne, da yin haka addini ne da Annabi Sallallahu Alaihi Wasallama ya sunnanta haka, ko dai ta hanyar ya aikata, ko ya nuna ma wani ya aikata, ko wani ya yi haka Annabi Sallallahu Alaihi Wasallama ya tabbatar da abin da ya yi xin. Tunda kuwa aka ga Annabi Sallallahu Alaihi Wasallama ba haka yake yi ba, ba kuma haka Sahabbai suke yi ba, mun san ba wata falala a cikin haka. Annabi Sallallahu Alaihi Wasallama da kansa ya kan sanya rigar auduga musamman a cikin tafiye-tafiyensa.

Daga qarshen hadisin da ya kawo cewa, Annabi Sallallahu Alaihi Wasallama ya xora Husaini da Ibrahim a kan cinansa, kuma Jibrilu Alaihis Salamu ya zo ya ba shi zavi a tsakaninsu, tatsuniya ce kawai da ba ta da asali sai a cikin qwaqwalen jahilai. Kuma ai a ga Hasan nan an bari tare da Husaini. To, sai me?
2.7.3 Zainul Abidina da Baqir da Sadiq

Shi kuma Ali xan Husaini Zainul abidina ya kasance yana azumi da rana, ya yi sallah da dare, ya kuma karanta Alqur’ani. Yana yin sallar raka’oi dubu ga yini da darensa kowace rana. Yana kuma addu’a bayan rakao’i biyu da addu’oi nasa da waxanda aka riwaito daga iyayensa, sannan ya jerfar da takarda yana mai cewa, yaya ma zan iya yin ibada irin ta kakana Ali. Kamar yana damuwa. Ya kasance yana yawaita kuka har hawaye suka yi masa tsaga a fuska, yayi sajada har aka kira shi mai tambon sallah. Kuma Manzo ya kira shi Sayyidul Abidina, shugaban masu ibada.

Akwai lokacin da Hishamu xan Abdulmalik ya je aikin hajji ya yi qoqarin sunbuntar Hajarul-Aswad bai samu damar yin haka ba saboda gwamatso, amma lokacin da Ali xan Husaini ya zo yin haka sai dukan mutane suka ba shi wuri ya sumbaci dutsen shi kaxai. Sai Hishamu xan Abdulmalik ya ce, wane ne wannan? Sai Farazdaq ya yi waqoqin nan nasa da aka sani game da shi. Sai Zainul Abidina ya aika ma Farazdaq dinari dubu zuwa, shi ko ya qi karva, ya ce, abin da ya sa na yi wannan waqar don fusata saboda Allah da Manzonsa. Ba zan karvi kuxi a kansa ba. Sai ya ce mu Ahlul-Baiti abin da ya fita daga wurinmu ba ya komawa. Sai Farazdaq ya karvi kuxin.

Akwai wasu mutane a Madina, abincinsu na zo masu da dare ba su san daga inda yake zuwa ba, sai da Zainul Abidina ya mutu sai suka gane cewa abincin daga wurinsa yake zuwa.

Xan Shi’ar ya ci gaba da cewa: Xansa Muhammad Al-Baqir ya fi kowa zuhudi da ibada. Sujada duk ta kware fuskarsa. Ya fi kowa ilimi a zamaninsa. Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama ya kira shi Baqir, mai ramin sujada. Jabiru xan Abdullahi ya zo wurinsa a lokacin Baqir xin yana qarami a makarantar Allo, sai ya ce masa: “Kakanka Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama na gaishe ka”. Sai aka ce wa Jabir yaya aka yi haka? Sai ya ce: Na kasance wurin Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama Husaini na bisa qafarsa yana wasa, sai Manzo ya ce, za a haifa ma sa xan da ake kira Ali, ranar tashin qiyama wani mai kira zai kira yana cewa, shugaban masu ibada ya tashi, sai Alin ya tashi, sannan a haifa ma sa xan da ake kira Muhammad Al-Baqir, zai fexe ilimi fexewa. In ka haxu da shi ka isar ma sa da gaisuwata. Abu Hanifa ya riwaito shi da waninsa.

Xan Shi’ar ya ce: Sai kuma xansa As-Sadiq wanda ya fi duk mutanen zamaninsa ilimi da ibada. Malamman tarihi sun riwaito cewa, shagaltarsa da ilimi ta hana masa neman shugabanci. Umar xan Abul Miqdami ya ce: Na kasance in na dubi Ja’afar xan Muhammad As-Sadiq sai in san cewa yana daga cikin zuriyar Annabawa. Shi ne ya yaxa fiqihun ‘yan-sha-biyu da ilimi na haqiqa da aqidodi na yaqini. Bai kasance yana ba da labarin abu ba face ya auku. Don haka na ake kiran sa As-Sadiq Al-Amin.

Abdullahi xan Husaini ya tara mabiyan Ali don yin mubaya’a ga ‘ya’yansa biyu, sai Sadiq ya ce ma sa, wannan lamarin ba zai auku ba, sai ya yi fushi a kan haka. Sai ya ce, mai shuxin hular can ne zai zama sarki, yana nuna Mansur. Da Mansur ya ji haka, ya san cewa lamarin zai auku, kuma sarauta za ta kai wurinsa. Amma lokacin da ya samu matsala har ya gudu sai ya rinqa cewa, ina zancen mai gaskiyar nan nasu? A qarshe dai shi ya sami mulkin.
Martani:

Shi dai Zainul Abidina yana daga cikin manyan Tabi’ai a fagen ilimi da riqon addini. Malaman Sunna sun yi ma sa sheda a zamaninsa.

Malam Yahaya xan Sa’idu ya ce: “Zainul Abidina ne mafi darajar bahashimen da na tarar a Madina”. Shi kuma Muhammadu xan Sa’adu cewa ya yi: “Zainul Abidina ya kasance amintacce, yardajje, mai yawan hadisai, na qwarai; masu gajeruwar hanya”. Yahaya xan Sa’idu kuma ya ce, na ji Zainul Abidina na cewa: “Ya ku mutane! Ku so mu irin son musulunci. Wannan son da kuke yi mana ya kusa zama abin kunya a kanmu”.

Sai cewa yana raka’a dubu kullum. Mun riga mun faxi cewa, wannan ba zai yiwu ba sai in an yi sallolin ba yadda shari’ah ta nema ba. Kuma tun can asali shari’a ba ta yi umurni da yin haka ba. Haka kuma ba wani hadisi mai asalai a kan cewa, Annabi Sallallahu Alaihi Wasallama ne ya sa ma sa wannan laqabi na Sayyidul Abidina.

Shi ma xansa Abu Ja’afar Al-Baqir yana daga cikin masu ilimi da riqon addini. An ce ana kiransa Baqir ne don ya tona ilimi, ba don sujada ta ci goshinsa ba kamar yadda xan Shi’ar ya ce. Amma shi ma ba gaskiya ba ne a ce ya fi kowa ilimi a zamaninsa. Ga irin su Zuhuri a zamaninsa wanda malamai sun san ya fi shi ilimi. Hadisin cewa, Annabi ya kira Baqir shi ma ba ya da asali, qarya ne. Haka cewa, wai, Jabir Raliyallahu Anhu ya isar ma sa da gaisuwar Annabi.

Ja’afarus-Sadiq ma haka. Yana cikin malamai masu daraja. Amru xan Abul Miqdami ya ce: Duk na kalli Ja’afar xan Muhammadu nikan gano cewa, yana cikin zuri’ar annabta. Amma cewa, ya kama ibada ya bar sha’anin mulki ya ci karo da aqidarku ta ‘yan-sha-biyu. Domin a wurinku dole ne ya jagoranci jama’a tun da Allah ne ya xora ma sa, inji ku. In da ya tsaya ya yi wannan wajibin ai da ya fi ma sa yawan nafilfili ko?

Sai cewa, shi ya yaxa ilimin Imamiyyah da aqidunsu. Yana son ya ce ya qago wani ilimi ne da babu shi kafin lokacinsa? Ko kuma waxanda suka gabace shi ne ba su yi bayanan da ya kamata ba? Ai duk mai hankali ya san cewa, Annabi Sallallahu Alaihi Wasallama ya gama bayyana ma al’ummarsa duk wata aqida da ya wajaba su qudurta, ya karantar da su cikakken addininsu. Sahabbai kuma sun yi iya qoqarinsu wajen ganin sun xauko wannan sun isar da shi ga sauran musulmi. Maganar xan Shi’ar dai in ba ta zama suka ga Ja’afarus-Sadiq ba, to, suka yake nufi ga magabatansa. Kuma Ja’afarus-Sadiq ya zama shi ne alqiblar maqaryatan wannan al’umma, kowa ya kwaso sharar maganganunsa sai ya jingina a gare shi. Allah zai yi hukunci da adalci a tsakaninsa da maqaryata.
2.7.4 Musa xan Ja’afar

Xan Shi’ar ya ce: Sai kuma xansa Musa Al-Kazim. Ana kiransa bawan Allah Nagari, ya fi kowa bautar Allah a zamaninsa. Yana azumi da rana kuma ya tsayar da sallah da dare. An kira shi Kazim don in wani abu ya zo masa daga wani sai ya aika masa kuxi. Ibnul jauzi xaya daga cikin Hambalawa ya ce: An riwaito daga Shaqiq Al-Balakhi ya ce, na fita zuwa hajji a shekarar 149H, sai na sauka a Qadisiyyah, sai ga wani saurayi kyakkyawa, wankan tarwaxa, yana sanye da tufa mai gashi, ya rataya gwado, yana kuma sanye da takalma, ya zaune shi kaxai. Sai na ce a raina, wannan saurayin Sufi ne, yana son ya zama nauyi akan mutane, wallahi zan tafi wurinsa in tsawace shi. Sai na kusanta gare shi. Lokacin da ya ga na nufo shi sai ya ce, ya Shaqiq: Ka nisanci mafi yawan zato don sashen zato zunubi ne. Al-Hujurat 12.

Sai na ce cikin raina wannan bawa ne salihi ya furta abin da ke cikin raina, zan tafi wurinsa in ce ya yafe ma ni, sai ya vace daga idanuna. A lokacin da muka sauka Waqisa sai ga shi yana sallah, gavovinsa na kakkarwa, idonsa na zubar da hawaye, sai na ce: Zan je in ce ya yi mani uzuri, sai ya taqaita sallah ya ce, ya Shaqiq: Lalle ni mai yawan gafartawa ne ga wanda ya tuba, ya yi imani, ya kuma aiki na gari, sannan ya shiriya. Xaha:82. Sai na ce wannan yana cikin Abdalu zavavvun matanen da Allah kiyaye duniya da su, ya yi magana game da sirrina sau biyu kenan. Lokacin da muka sauka wurin da ake kira Zibalah, sai ga shi tsaye bakin wata rijiya, da wani abu a hannunsa don xibar ruwa, sai abin ya faxa cikin rijiya. Sai ya xaga kansa sama ya ce:

Kai ne Ubangijina idan na yi qishi

Kai ne kuma abincina idan na ji yunwa

Ya shugbana! Ba ni da wata guga in ba wannan ba.

Sai Shaqiq ya ce: Wallahi na ga rijiya ta taso, ya xauki gugarsa, cike da ruwa, ya yi alwala, ya yi sallah raka’a huxu, sannan ya tafi wurin wani tulin rairayi, sai ya rinqa xibar rairayin yana sa wa cikin guga yana sha, sai na ce ka ciyar da ni cikin sauran abin da Allah Ta’ala ya ciyar da kai, ko abin da Allah Ta’ala ya ni’imta ka da shi, sai ya ce: Ya kai Shaqiq! Ni’imomin Allah Ta’ala bayyanannu da voyayyu ba su gushe ba a kanmu, ka kyautata zato ga Allah Ta’ala. Sai ya bani gugar, sai na tarar cewa wani abin sha ne da aka haxa da sukari, ban tava shan abu mai daxi da qanshi ba irinsa. Na sha na yi dis. Na yi kwana da kwananaki bayan haka ba na sha’awar wani abin ci ko abin sha. Ban sake ganin sa ba sai a Makka, sai na gan shi a wani wuri cikin masallaci da tsakiyar dare yana sallah da natsuwa, yana nishi da kuka, bai gushe a cikin wannan halin ba har safiya ta waye, da asuba ta yi sai ya zauna wurin sallarsa yana tasbihi, sannan ya tashi don ya yi sallar farilla, sai ya yi xawafi shuxi bakwai sannan ya fita. Sai na bi shi, na kuma tarar cewa yana da mabiya da kuxi da bayi, savanin yadda na gan shi a hanya, sai mutane suka kewaye shi suna yi masa sallama suna neman albarkarsa. Sai na ce masu: Wane ne wannan? Suka ce: Musa ne xan Ja’afar. Sai na ce, na yi mamakin irin waxannan abubuwa ga wani ba irin wannan sharifin ba. Wannan bahambale ne ya riwaito shi.

Kuma a hannunsa ne Bishir Al-Hafi ya tuba, don akwai ranar da ya wuce ta gidansa a Bagadaza sai ya ji ana ta yin ma-sha’a, da waqoqi da raye-raye a gidan nasa. Sai ga wata kuyanga ta fito da shara, sai ta jefar da ita a juji. Sai ya ce mata, ke yarinya, maigidan nan bawa ne ko xa? Sai ta ce da shi, xa ne. Sai ya ce, kin yi gaskiya, don da bawa ne da ya ji tsoron Ubangijinsa. Da kuyangar ta shiga gida sai ta tarar mai gidan yana shan giya, ya ce: me ya tsayar da ke? Sai ta ba shi labari. Sai ya fita ba takalma har ya isa wurin shugabanmu Ja’afar ya tuba a hannunsa.


Martani:

Iyakar abin da aka sani a kan Musa shi ne, an haife shi a garin Madina, a bayan shekara ta 120. daga nan kuma Sarkin Musulmi Mahadi ya kira shi zuwa Bagadaza. Ya kuma sake dawo da shi Madina bayan haka. A nan ne ya ci gaba da rayuwa har zamanin Sarki Rashid. A zamanin Sarki Haruna Rashid da ya je Umrah, ya bi ta Madina, ya kuma ya xauki Musal Kazim karo na biyu zuwa hedikwatar mulki; Bagadaza, ya kuma tsare shi a can har ajalinsa ya riske shi yana a tsare.

Musal-Kazim mutum ne da ya shahara a fagen qoqarin ibada. Waxanda ke bayansa babu wani ilimi na addini da duniya ta qaru da shi daga wurin su, domin kuwa kafin ka yarda mutum na iya ba ka riga sai ka duba ta wuyansa. Labarin da aka yaxa kuwa cewa Bishir Al-Hafi ya tuba ne a hannunsa na daga cikin qarairayi na masu qarin gishiri. Domin kuwa bai samu sukunin da zai iya haxuwa ma da Bishir ba zuwansa Bagadaza, kuma a girke yake wuri xaya.
2.7.5 Ali Ar-Ridha

Xan Shi’ar ya ce: Shi kuwa Ali Ar Ridha shahararren malami ne. kuma ya fi kowa Zuhudu a zamaninsa. Malaman Sunnah da dama ne suka yi karatu a wurinsa. Sarki Ma’amun ya naxa shi saboda iliminsa. Ya tava yi wa xan’uwansa Zaidu gargaxi yana tunatar da shi cewa, Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama ya tabbatar wa zuri’ar Fatima cewa, Allah ya yi mata alqawarin wuta ba zata ci zuri’arta ba don kamun kan da ita Fatimar ta yi. Ya ce masa: To, me zaka ce ma Manzon Allah idan ka zubar da jinin musulmi, ka qwaci dukiyarsu babu dalili, ka razanar da hanyoyinsu saboda jahilan Kufa sun ruxe ka? A wata riwaya kuma an ce: Ali Raliyallahu Anhu ya ce da Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama me ya sa ka sa wa Fatima wannan suna? Sai ya ce: Don Allah ya cire ta ita da zuri’arta daga masu shiga wuta. Ali ar-Ridha ya ci gaba da ce masa: Kasancewar ta kare mutuncinta ba zai hana ka shiga wuta ba in har ka yi zalunci. Wallahi zuri’arta ba su samu wancan matsayin ba sai don xa’ar Allah. Idan kuwa ka kuskura ka nemi abin da suka samu ta hanyar sava ma Allah, to, kamar kana so ne ka fifita kanka a kansu.

Xan Shi’ar ya ci gaba da cewa: Kuma Sarki Ma’amun ya rubuta sunan Ali ar-Radha akan kuxi, ya aika zuwa garuruwa cewa, a yi masa mubaya’a. ya kuma daina sa baqaqen kaya, ya sanya kore a madadin haka.

Kuma wai, inji xan Shi’ar, a cikin wata qasida da Abu Nawwas ya yi yana yabon sa, ya faxi cewa: Ba za a iya qare yabon ka ba tun da Jibrilu ne da kansa ke hidimar kakanka.


Martani:

Ba shakka zuri’ar sayyidina Husaini basu tava gamuwa da musibar da ta fi jinginar da ‘yan Shi’ah ke yi gare su ba. yabon da suke masu gara ma zargi da shi. In ba don Ahlus-Sunnah sun san waxannan bayin Allah ba, da an qware su a dalilin maganganun ‘yan Shi’ah da za su iya sa a munana zato ga waxannan talikai.

Duk abin da xan Shi’ar nan ya faxi a kan Ali Ar-Ridha ba na kamawa a ciki. Ka ga dai cewar da ya yi, ya fi kowa ilimi da gudun duniya a zamaninsa. Maganar fanko ce wayam; babu hujja ko misqala zarratin akan ta. Duk wanda yake son wani in bai sa tsoron Allah da adalci ba zai iya faxin irin wannan a kansa. Cika baki kuwa ai kowa ma zai iya shi. In ba haka ba, wa zai haxa Ridha ta fuskar ilimi da Shafi’i, da Ishaqa xan Rahawaihi, da Ahmadu xan Hambali da Ashabu xan Abdul Azizi ire-irensu? Ko ina ya yi gudun duniyar irin su Abu Sulaiman Ad-Darani da Ma’aruf Al-Karkhi da ire-irensu?

Kuma cewa, malaman Sunnah da yawa sun yi karatu wurinsa. To, kamar su wa? Ba wani malamin da aka san ya yi karatu wurinsa. Amma in an ce yana da xalibai waxanda ba sanannu ba, wannan abu ne mai yiwuwa, tunda masu neman ilimi duk inda suka samu abin tsinta ba su yin sakaci da shi. Amma a ce ga wani malami da aka sani ya yi xalibta wurinsa ba gaskiya ba ne.

Sai maganar da suke yaxawa cewa, ma’aruf Al-Karkhi ya yi hidima a wurinsa. Kuma ma wai, a hannunsa ya musulunta. Duk irin waxannan kalamai ne da ba su da tushe. Kamar hadisin Fatima da ya kawo da cewa, Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama ya yi mata alqawarin kare ta da zuri’arta daga wuta don ta tsare mutuncinta. Wannan ba abu ne da aka sani a addini ba, cewa, zuri’ar wani zata haramta ga wuta don shi ya kama kansa. Ballantana kuma irin lafazinsu na ce ma Jibrilu (AS) mai hidimar Manzon Allah. Wannan duk da yake yana nuna kamar sun darajanta Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama, amma akwai cin haqqin Mala’iku da rashin sanin girmansu a cikin wannan magana. Amma su ‘yan Shi’ah koyaushe irin waxannan waqoqin daxinsu suke ji, har da kafa hujja da su a addini. Wannan ko ba xabi’ar masu basira ga addini ba ce.


Yüklə 2,75 Mb.

Dostları ilə paylaş:
1   ...   6   7   8   9   10   11   12   13   ...   51




Verilənlər bazası müəlliflik hüququ ilə müdafiə olunur ©muhaz.org 2024
rəhbərliyinə müraciət

gir | qeydiyyatdan keç
    Ana səhifə


yükləyin