Tafarkin sunnah



Yüklə 2,75 Mb.
səhifə11/51
tarix28.10.2017
ölçüsü2,75 Mb.
#17506
1   ...   7   8   9   10   11   12   13   14   ...   51

2.7.6 Muhammadu Al-Jawad

Xan Shi’ar ya ci gaba da cewa: Imami na gaba shi ne: Muhammadu Al-Jawad, wanda ya bi tafarkin mahaifinsa ta fuskar ilimi da taqawa da baiwa. Kuma a lokacin da mahaifinsa ya rasu, sai Sarki Ma’amun ya nutsa ga qaunarsa saboda iliminsa da addininsa, da kammalar hankalinsa cikin qarancin shekarunsa. A kan haka ne kuma ya so ya aura masa da ‘yarsa Ummul Fadhli kamar yadda ya aura wa mahaifinsa da ‘yarsa Ummu Habib. Anan ne kuma, inji xan Shi’ar, Abbasiyyawa suka tsananta masa, suka ji tsoron sarautar ta fice daga hannunsu, ta hanyar shi ya yi wa Jawad mubaya’a kamar yadda ya yi wa babansa. Don haka dattawansu suka haxu suka kira shi zuwa ga oda. Suka ce masa, wai, wannan xan qaramin yaro ne da ba shi da karatu. Sai Sarkin ya ce: Na fi ku saninsa. Amma in kuna so ku gwada shi. Sai suka aminta da haka. Anan ne kuma wai, suka ba Alqali Yahaya xan Aksamu kuxi mai yawan gaske don ya qure shi.

Xan Shi’ar ya ci gaba da ba da labari: Wai, sai aka sanya rana da wuri da lokaci. Mutane suka haxu. Sarki ya sa aka kira shi, aka kuma kira Abbasiyyawa. Daga nan sai Alqali ya fara tambayar sa game da hukuncin mai harama in ya yi farauta. Nan take sai Jawad ya ce masa: A ina ya kashe shi; a harami ko a wajensa? Ya san hukuncin yin haka ko bai sani ba? Ya kashe dabbar ne don buqatarsa gare ta ko don ya kare kansa? Qaramar dabba ce ko babba? Cikin dangin tsuntsaye take ko cikin wani dangi na daban?

Sai kawai aka ga Alqali ya rikice, in ji mai xan Shi’ar mai ba da labari. Ya shige gashi har kowa ma ya gane haka a wurin. Sai Sarki Ma’amun ya ce da jama’arsa: Kun fahimci abin da nike gaya muku, wanda kuma kuke musunsa? Sannan sai ya juya kan Imamu Jawad, ya ce masa: Ka shirya neman auren? Imamu ya ce: Na’am. Nan take kuwa ya nemi xiyar Sarki aka ba shi ita a kansadaki Dirhami xari biyar, daidai sadakin kakarsa Fatim. Ya kuma biya naqadan, ta zama matarsa.


Martani:

Muhammad Al-Jawad, babu shakka, yana cikin fitattun Hashimawa, masu kwarjini ga idon jama’a. Ga shi kuma karimin mutum. Wannan laqabin nasa ma yana nuni ne ga karimci da sakin hannunsa. Bai yi tsawon rai ba, don a lokacin wafatinsa bai wuce shekaru ashirin da biyar ba (95H-120H). Kuma Sarki Ma’amun ya aurar masa da ‘yarsa. Yana kuma aika masa Dirhami miliyan xaya kowace shekara. Sannan Sarki Mu’utasim ya gayyace shi zuwa Bagadaza inda ya zauna can har ya cika.

To, ka ji gaskiyar labari. Amma irin wannan saqaqqen labari na xan Shi’ar ko alama babu qanshin gaskiya a cikinsa. Wannan labarin warin qarya ma yake yi. Don masana sun san Alqali Yahaya ya fi qarfin ya yi tambaya don neman qurewa wai, a kan hukuncin farauta! Kai tafi ma labarin haka yake. To, sai me? Sai ya zan imami don ya jera ma Alqali waxannan tambayoyi? Magana da mai hankali da basira take da daxi. Amma su ‘yan Shi’ah kullum irin waxannan labarai su ne hajarsu da suke baje koli. Allah ya sawwaqa.
2.7.7 Ali Al-Hadi

Xan Shi’ar ya ce: Imamu na gaba shi ne, Ali xan Muhammad wanda ake ma laqabi da Askari. Mutawakkil ya tura shi daga Madina zuwa Bagadaza, daga nan kuma zuwa garin Surra Man Ra’a. A can ne ya sauka wani wuri da ake kira Askar, sai aka yi masa wannan suna. Ya ce: Mutawakkil dai ya gargaxo shi ne daga Madina don shi sarkin mai qin Ali ne. Sai ya lura da mutane sun karkata zuwa gare shi ainun, sai ya ji tsoron sa. Ya yi umurni a zo da shi. Mutanen Madina kuwa duk suka fashe da kuka, saboda alherinsa a wurinsu da yawan ibadarsa. Aka dai bincika gidansa ba a samu komai ba sai Alqur’ani da littafan karatu da na addu’oi. Wannan ya sa sai wannan imami ya yi daraja a wurinsa, har ya rinqa yi masa hidima da kansa.

Xan Shi’ar ya ci gaba da cewa: A lokacin da Yahaya xan Hubairata ya zo da Al-Hadi a Bagadaza sai ya soma da gidan gwamna Ishaqu xan Ibrahim Ax-Xa’i yana mai ce masa: Ka ga wannan jikan Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama ne, kuma ka san halin Sarki. In har ka ba shi shawarar kashe shi, to, da Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama zaka kyas ranar Alqiyama. Da suka shiga wurin Sarki kuma, aka ba shi labarin Zuhudunsa da tsentseninsa sai ya mutunta shi. Ana haka kuwa sai watarana sarki Mutawakkil ya yi rashin lafiya. Ya kuwa yi alwashin idan Allah ya ba shi lafiya zai yi sadaka da kuxi mai yawa, amma bai ayyana yawan ba. don haka da ya warke sai ya nemi malamai a Bagadaza babu wanda ya san amsar da zai ba shi. Sai da aka nemi Al-Hadi sannan ya ba shi da cewa, zai yi sadaka da Dirhami 83 domin su ne yawan yaqoqan Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama kuma ga shi Allah ya kira da yawa inda ya ce: Haqiqa Allah ya taimake ku a cikin wurare masu yawa 9:25. Ya ce: Domin Annabi Sallallahu Alaihi Wasallama ya fita yaqi 27 da kansa, ya tura an yi yaqi ba da shi ba har sau 56.

Xan Shi’ar ya ci gaba da cewa: Mas’udi ya ce, An ba sarki Mutawakkil labarin Al-Hadi na voye makamai, waxanda ‘yan Shi’arsa daga garin Qum ke kawo masa. Don haka nan gaba zai yi yunqurin juyin mulki. Wai, sai ya sa wasu turkawa suka shiga gidansa da dare amma ba su samu kome ba. suka tarar da shi ya kulle kansa a wani wuri yana ta karatun Alqur’ani, akan rairayi da tsakuwa, sai aka tungumo shi a haka zuwa wurin sarki, shi kuma a lokacin yana shan giya daa kofinta a hannunsa. Wai, sai sarki ya girmama shi, ya zaunar da shi kusa da shi har ya taya masa shan giyar. Sai Al-Hadi ya ce masa: Yi haquri. Ni ban tava shan ta ba, bale in saba da ita. A nan ne fa, inji xan Shi’ar, Al-Hadi ya yi masa gargaxi mai ratsa zukata, ya karanta masa ayoyin Alqur’ani. Mutawakkil kuwa ya yi ta rusa kuka har sai da ya jiqe gemunsa.


Martani:

Wannan magana, ita da ta xazu duk ‘yan gida guda ne. Sunan gwamnan ma a yadda ya faxe shi ba haka yake ba, tunda shi bai san tarihi ba.

Sunan gwamnan Bagadaza na wancan lokacin shi ne Ishaq xan Ibrahim Al-Khuza’i. Ba ya da alaqa da qabilar Xayyi’ balle a ce masa Xa’i. Kuma fa sanannen mutum ne, xan babban gida; duk masana tarihi sun san shi. Ga ma xan cikinsa ya yi gwamnan Bagadaza a zamanin Mutawakkil xin da bayansa! Kuma xan baffansa ne; Abdullahi xan Xahiru ya yi gwamna a Khurasan. Sannan shi ne wanda ya yi wa Imamu Ahmad sallah lokacin da ya cika. Ya yi gwamna ne tun zamanin Mu’utasim da Wasiq, da wani xan lokaci a zamanin Mutawakkil. Saboda haka wannan gida na Khuza’ata sanannu ne, ba abin da ya haxa su da Xayyi’, balle a kira xayansu Xa’i kamar yadda shi xan Shi’ar ya yi.

Sai kuma zancen fatawar da ya ce an yi, wacce ke kware al’aurar jahilcinsa. Wane masani ne zai yarda da wannan fassara da fatawa da ya jingina ma Al-Hadi? Duk ma yaqoqan Annabi Sallallahu Alaihi Wasallama ba su kai adadin da ya faxi ba. Ba kuma dukan yaqoqan aya ke magana ba; waxanda aka yi kafin Hunainu take magana. A su xin ma, wuraren da aka ci nasara; ba irin Uhudu ba misali. Kuma don ayar ta ce waxannan yaqoqa na da yawa ba ya nuna duk wanda ya yi rantsuwa a kan wani abu mai yawa wannan adadin ne fatawarsa ba. Kana tsammanin a nan kaxai ne Maxaukakin Sarki ya faxi “Mai yawa”? Duba sauran ayoyin Alqur’ani mana gasu nan tari, a cikinsu har da masu nuni ga xari bakwai, da masu nuni ga dubu xari biyu, a kowacce an ce suna da yawa.

Saboda haka, yawan abu, ba ya nufin wani kevantaccen adadi bale an yi hikima da ba da irin wannan fatawa. Wannan fa da a ce maganar tana da wani tushe da za a iya gaskata ta kenan. To, ina kuma ga shi an tabbatar da cewa, sun fesa ta?!
2.7.8 Hasan xan Muhammad Al-Askari1

Xan Shi’ar ya ce: Imami na sha xaya shi ne: Al-Hasan xan Muhammad Al-Askari, xan wannan da ya gabata. Kuma ya kasance malami, mai gudun duniya, mai yawan kirki da ibada. Shi ne mafifici duk a zamaninsa. Da yawa malaman Sunnah ke ruwaya daga wurinsa.


Martani:

Maganarsa a nan ba ta banbanta da sauran maganganun da ya saba yi na cika baki ba, da faxin abin da ba shi aka sani ba. Duk dai malamai sanannu a zamanin wannan taliki an san su, an san riwayoyinsu. Kuma ba mu san xaya daga cikinsu da ya karvo kalima xaya ba daga wurin wannan Askari. Duba fitattun littafan Sunnah guda shida: Buhari da Muslim da Abu Dawuda da Tirmidhi da Nasa’i da Ibnu Majah duk sun rayu a kusan lokacinsa, amma ba wanda ya ce ya ji ko qala daga wannan mutum. Kai qarewa ma, ka duba littafin da Ibnu Asakir ya wallafa wanda ya jera sunayen malaman da aka yi ruwaya wurinsu. Ko samatar wannan mutum babu. To, ya za a saurari wannan cika baki wai, Da yawa malaman Sunnah ke ruwaya daga wurinsa?

Haka ita ma cewar da ya yi wai, shi ne mafifici duk a zamaninsa. Mun saba da jin irin wannan tun ba yau ba.2
2.7.9 Muhammad Xan Hassan

(Mahadi-na-Voye)

Xan Shi’ar ya ci gaba da cewa: Bayan Askari kuma sai xansa; shugabanmu Muhammadu Al-Mahadi amincin Allah ya tabbata a gare shi. Ibnul Jauzi ya riwaito daga Ibnu Umar cewa, Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama ya ce: “Wani mutum zai bayyana a qarshen zamani wanda sunansa ya yi daidai da nawa, haka ma alkunyarsa. Zai cika qasa da adalci kamar yadda aka cika ta da zalunci. Wancan shi ne Mahadi”.


Martani:

Abin da malamai suka kawo irin su Xabari da Abdulbaqi da ire-irensu masana tarihi da ilmin dangantaka shi ne cewa, Askari bai tava haifuwa ba. Su kuma ‘yan Shi’ah sun ce ya bar cikinsa, amma xan nasa ya vuya tun yana qarami. Wasu daga cikinsu su ce, shekarunsa biyu, wasu uku, wasu ma har biyar. To, irin wannan yaro in har akwai shi, a shari’ar Allah da Manzo ai wajibi ne a sa shi qarqashin kulawar wata macce; uwa ko kaka ko inna, don ta kula da shi ta yi renonsa. Dukiyarsa da ya gada kuma a matsayinsa na maraya dole ne a ba da ita ga maza daga cikin dangin ubansa don su kula da ita. In har babu sai a bar ta a hannun sarki ya kula masa har sai ya girma ya isa aure. Kamar yadda Maxaukakin Sarki ya ce:

ﭽ ﯥ ﯦ ﯧ ﯨ ﯩ ﯪ ﯫ ﯬ ﯭ ﯮ ﯯ ﯰ ﯱﯲ ﯳ ﯴ ﯵ ﯶ ﯷ ﯸﯹ ﯺ ﯻ ﯼ ﯽﯾ ﯿ ﰀ ﰁ ﰂ ﰃﰄ ﰅ ﰆ ﰇ ﰈ ﰉ ﰊﰋ ﰌ ﰍ ﰎ ﰏ ﭼ النساء: ٦

Kuma ku jarraba marayu, har lokacin da suka isa aure. To, idan kun lura da shiriya daga gare su, to, ku miqa masu dukiyoyinsu. Kada ku ci ta da varna da yin gaggawa gudun su girma (su karvi abarsu) 4:6.

To, wanda ko kula da kansa ba a xora masa ba da nassin Alqur’ani, ba a kuma yarda a hannunta masa dukiyarsa ba, ina maganar a ce shugaba ne ga musulmi, kuma har wai mutum ba ya zama musulmi sai ya ba da gaskiya da shi?!

Kuma wannan xan taliki, in har ma Allah ya halicce xin, to, bai amfanin su da komai a duniya ko a addini. Bai tava karantar da kowa bihin ba, ba a kuma tava qarar da hairinsa ba. Ba xaya daga cikin manufofin shugabanci da aka samu ta wurinsa. In da ma akwai shin, to, sharrin da samuwarsa ta haifar ya isa. Don kuwa masu ba da gaskiya da shi ba su more masa ba, masu qaryata shi kuma za su xanxani kuxarsu. To, ina amfanin wannan shugaba?! Wace maslaha zata sa Allah ya halicci wanda yake haka, sai ka ce ba gwanin Sarki ba?!! Tsarki ya tabbatar ma Allah daga yin irin wannan.

Suna iya cewa, ya vuya ne saboda zaluncin mutane. To, amma ai ko a zamanin iyayensa ana zalunci. Me su, basu vuya ba? Kuma ga mabiyansa nan cike da sassan qasa. Me ya hana shi bayyana koda sau xaya a wurinsu, ko kuma ya aiko masu wani xan aike da zai karantar da su wani abu na addini? Kuma ai za iya fakewa wurin wasu magoya bayansa masu qarfi irin na Sham..

In ko har bai iya faxa ma kowa kome saboda tsoronsa, to, ina amfanin kasantuwarsa? Ka ga ai ko Annabawan da aka aiko da mutane basu gaskata su ba, sun dai bayyana ga mutane sun isar da saqo, sun tsayar da hujja akan mutane. Su ko ‘yan-sha-biyu ba abin da abin jiran nasu ya tsinana masu sai wahala da damuwa, da qiyayya da mutane, da addu’ar da Allah bai karva. Fiye da shekaru 450 suna abu guda, basu je ko ina ba!

Kai, ya ma sava ma hankali da al’adar da aka sani ga wannan al’umma. Don tun farkonta ba a tava sanin wani ya wuce shekaru 120 ba, balle 450. Imamul Buhari ya riwaito daga Annabi Sallallahu Alaihi Wasallama yana cewa: “Kun ga daren nan na yau? Duk wanda ke bayan qasa daga yau, ba zai rayu fiye da shekara xari ba”.

Idan ya kasance a wancan zamanin ba a wuce shekaru xari, to, ga al’ada daga baya abin ma ragewa zai yi. Domin wannan ita ce sunnar Allah a cikin halitta; shekarunsu suna yi suna ragewa. Nuhu Alaihis Salamu shekaru 950 ya yi yana kiran jama’arsa. Adamu Alaihis Salamu shi ma sai da ya shekara dubu kamar yadda ya inganta a cikinsunan na tirmidhi. Amma tsawon rayuwa yana ta ragewa kodayaushe. Ya kuma inganta a cikin hadisi cewa: “Tsawon rayuwar al’ummata yana reto a tsakanin shukaru sittin zuwa saba’in. Kaxan ne za su wuce haka”.

Sukan kafa hujja da cewa, wai ai Haliru ma yana nan raye. To, wannan hujja gara ma yin shiru da kafa ta. Domin ko wane ne ya yarda cewa har yanzu Haliru na a duniya?! Malamai na gaskiya tun tabbatar da mutuwarsa. Kai, in ma mun sallama; yana raye, to, ai shi ba cikin wannan al’umma yake ba. Shi ya sa ake samun maqaryata daga cikin aljannu da mutane koyaushe suna cewa, su ne Haliru. Waxanda ke ganin su kuma sai su gaskata hakan.

Shi ma Muhammadu xan Hassan; Mahadin ‘yan biyu, mutane da dama sun yi da’awar su ne shi. Kuma wannan qarya ba ta banbanta da waccan ga masu basira da hankali.
2.7.10 Hadisin Mahadi

Cewar da xan Shi’ar ya yi wai, Ibnul Jauzi ya riwaito daga Ibnu Umar cewa, Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama ya ce: “Wani mutum zai bayyana a qarshen zamani wanda sunansa ya yi daidai da nawa, haka ma alkunyarsa. Zai cika qasa da adalci kamar yadda aka cika ta da zalunci. Wancan shi ne Mahadi”.


Martani:

Tun farko dai baku yarda da hadissan Ahlus-Sunnah ba. To, don me za ku kafa hujja da shi? In kun ce, ai don mu kafa maku hujja da hadisan malamanku ne. Sai mu ce, to, ku bari mu kawo maganganunsu.

Sannan kuma wannan hadisi ba ya da wani qarfin da za a kafa hujja da shi. Duk da haka kuma xan Shi’ar ya canza lafazin hadisin, domin in aka karanta shi a yadda ya ke, mu ne za mu kafa maku hujja da shi. Hadisin cewa ya yi: “Sunansa ya yi daidai da nawa. Na mahaifinsa kuma ya yi daidai da na mahaifina”. To, shi wannan Mahadin naku ai ba xan Abdullahi ne ba. Ya kuma zo a wani hadisin cewa, daga zuri’ar Hassan yake. Naku kuma jikan Husaini ne.

A wannan wuri dai xan Shi’ar ya yi halinsu da aka san su da shi na maguxi da algussu don voye gaskiya. Ka ga cewar da ya yi Ibnul Jauzi ya riwaito. Ba fa Ibnul Jauzin da duniya ta sani ne; malamin Sunnah ba. Wani Ibnul Jauzi ne xan La’ilaha’ula’i. Sunansa na ainihi Yusufu xan Quzzu. Shi ne wanda ya wallafa wani littafin tarihi mai suna Mir’atuz Zamani, da kuma wani littafi akan Imamai goma sha biyu mai suna I’ilamul Khawasi. Shi wannan mutum kamar hawainiya ya ke; yana rikixewa ne duk inda ya je. Ya yi rubutu akan darajojin Khulafa’ur Rashiduna, ya kuma yi akan zaginsu. Shi xan maula ne kawai da sunan malamai. Wannan shi ne xan Shi’ar ya ke kafa hujja da shi.


2.8 Wai Imamai Sha Biyu Sun fi Kowa!

Xan Shi’ar ya qara sharhi bayan kawo waxancan Imamai yana cewa: Waxannan su ne Imamai masu girman daraja, ma’asumai, waxanda matsayinsu a wurin Allah ba ya misaltuwa, don sun kai qolin ga kamala. Sun tsaya inda Allah ya tsayar da su a lokacin da wasu suka shagalta da sha’anin mulki da sharholiya da shaye-shaye. Wanda hakan ta sa suka yi varna da danginsu kamar yadda kowa ya sani. Mu; ‘yan Shi’ah ba abin da muke sai Allah ya isa. Inji shi.

Sannan sai ya yi kwaikwayon wani mawaqi xan’uwansa; xan Shi’ah da ke kira ga a jefar da mazhabobin Sunnah gaba xaya don taqaitar madogararsu, a koma ga masu karvo hukunce-hukunce kai tsaye daga Allah ta hannun kakansu!
Martani:

Da kuka ce su ma’asumai ne ai baku ba da kowace irin hujja ba sai cika baki da cewa, ai dole ne Allah ya samar da shugaba ma’asumi; wanda ba ya kuskure ko tuntuven harshe, don hakan ta samar da maslaha da luxufi ga jama’a. Wannan hujjar kuwa yanar gizo ta fi ta qarfi. Shi ya sa kun kasa nuna ma kowa ma’asumin sai Malam-na-Voye wanda bai tava amfaninku ba; ku da kuka yarda da shi, ballantana sauran musulmi da suka xauke shi a matsayin Malam Babu.

Cewa kuma matsayinsu a wurin Allah ba ya misaltuwa don sun kai qolin ga kamala. Wannan shi ma cika baki ne kawai. In wani ma yana so sai ya yi irin wannan cika bakin ga wasu da suka fi su ilimi da daraja daga cikin magabata. Kuma baku da abin da za ku ce masa. Duk wani masanin tarihi yana sane da cewa, Imamanku na goma da na sha xaya (Askari babba da qarami) ba su kai darajar wasu magabatan ba ma na lokacinsu.

Ko kiran su shugabanni da kuka yi. Muna buqatar ku bayyana mana irin shugabancinsu. Suna da qarfi ne na mulki da iko akan jama’a ta yadda ake jin tsoron su? Ko kuwa shugabanni dai ne ta fuskar ilimi da karantar da jama’a? Idan kun ce suna da qarfi to, mun san kuna yaudarar kanku ne. Kuma kun sani in banda Ali daga cikinsu babu wanda ya samu wannan qarfi. Shi xin ma kuma bai same shi yadda ake so ba, tun da kusan rabin al’umma basu tare da shi, ko abin da ya fi haka ko ya kasa. Kai da yawa ma sun yaqe shi. Daga cikin waxanda ke tare da shi kuma wasu suka kauce masa lokacin da zai yaqi waxancan don rashin amincewarsu da yin yaqin. A cikin waxanda suka kauce ma yaqin kuwa akwai da dama da sun fi waxanda suka yi yaqin na kowane vangare.

Idan kuma kun ce, su shugabanni ne ta fuskar ilimi da karantar da jama’a, don haka ya wajaba al’umma ta goyi bayansu. Sai mu ce, ba haka ba ne. Kasancewar mutum ya isa ya yi shugabanci ko limanci ko alqalanci ko jagorancin yaqi ba ta wajabta zamansa haka xin. Sallah kuwa a bayan liman ake yin ta, ba bayan wanda kawai ya cancanci limanci ba. Haka ma alqali mai iko ne ke yanke hukunci. Kuma kwamandan mayaqa shi ke jagoranci ba duk zarumin da yake iyawa ba.

Harwayau muna neman qarin bayani. Kuna nufin waxannan bayin Allah kowanensu ya kamata ya zama shugaba a lokacinsa, shi kaxai? Ko ko a’a, yana cikin waxanda suka cancanta a cikin Quraishawa irin sa?

Zancen da xan Shi’ar ya yi cewa, sun tsaya inda Allah ya tsayar da su a lokacin da wasu suka shagalta da sha’anin mulki da sharholiya da shaye-shaye, ba zancen adalci ba ne. Domin ba wani Ahlus-Sunnah da ya ce ayi koyi da masu sharholiya da varna; sara kai ne ko ba sara kai ba. Amma kasancewar Ahlus-Sunnah suna neman taimako da sara kai a kan abin da suke da amfani a cikinsa, suna kuma taimaka masu a cikin abin da shari’a ta yarda da shi. In har wannan laifi ne, to, ‘yan Shi’ah sun fi su yin wannan laifi. Domin su kowa ya san a wurin kafirai suke neman taimako da agaji. Shi kansa wannan malamin da muke taqaddama da shi shaida ne a kan haka, don kafiran Mugul da ire-irensu da dama sara kansa ne ta wannan fuskar. Kuma wannan shi ne tarihin ‘yan Shi’ah tun daxai.

Muna qara nanata cewa, su waxannan imaman da ‘yan Shi’ah ke bi, waxanda suka ce ma’asumai ne, ba su da iko ko xaya na zartar da hukunci. Ba a yin sallar jum’ah, kai ko ma salawatul hamsi bayan xayansu don ba liman ne ba. Ba a neman warware jayayyar fili ko gado ko wata husuma tsakanin ‘yan’uwa a wurinsu. Ba su shugabantar jihadi ko hajji, balle su tsayar da haddi ga masu laifi. Mutum kuma ba ya neman haqqinsa kowane iri na zama xan qasa daga wurinsu. Ba su hana ‘yan fashi ko varayi wanzuwa. Basu raba ma jama’a dukiyar baitul-mali. Iyakacinsu yin fatawa kamar yadda sauran malamai ire-irensu suka kasance suna yi. To, duk wanda yake neman wani abu irin wannan kuma ya tasar ma wanda ba shi da iko ai sunansa wawa. Wanda ya nemi abu daga mai shi, mai iko a kanshi, shi ne mai hankali.

Sannan malamin ya yi tsaga da faxi a cikin tuhumar da ya yi ma sarakuna. Domin kuwa kowa ya san a cikinsu akwai na kirki irin su Umaru xan Abdulazizi da sarki Mahadi. Da yawan waxanda ake tuhuma da savo a cikinsu kuma ba a bayyane suke yi ba. Wasunsu suna da zunubbai, amma akwai yiwuwar sun tuba, ko sun samu ladar da zata kankare zunubin nasu, ko Allah ya jarabce su da wani abin da ke kankare laifinsu. Abin da ya kamata a sani shi ne, su sarakuna ayyukansu na lada manya ne, haka ma zunubansu. Ba daidai suke da xaixaikun musulmi ba. Ina ko zaka haxa talaka mai qoqarin ibada gwargwadon qarfinsa da wanda ke tsayar da dokokin Allah akan al’umma, ya hana savo, ya qarfafi ayyukan alheri da yawa, ya yaqi kafirai, ya sadar da haqqoqan mutane da dama zuwa gare su, ya kwatanta adalci, ya hana da yawa daga cikin zalunci?!

Mu, bamu tava cewa sarakuna basu savo ko aikata zunubi ba. Kamar yadda sauran gama-garin musulmi duk suke, haka su ma sarakuna. Amma wa ya ce in mutum na zunubi an gama zaman lafiya da shi, kuma ba a taimakon sa a inda yake akwai maslaha da alheri a ciki?

‘Yan Shi’a na iya cewa, imamansu na da wani voyayyen ilimi da babu shi a wurin kowa! To, ina amfani voyayyen ilimi da ba a bayyana shi? Me ya raba shi da taskar kuxi da aka tsuke ta ba a ba kowa? Ya za a kira mutane ga bin wanda bai iya karantar da su kome irin Malam Babu na ‘yan Shi’ah?

In ko har suka ce, a’a, suna bayyana ma kevantattun mutane ne da suke da kusanci da su, to, mun san qarya suke yi. Dubi Ja’afar As-Sadiq, wanda malamai irin su Malik da Sufyanu xan Uyainata da Shu’ubatu da Sufyanus-Sauri da Ibnu Juraiju da Yahaya xan Sa’idu da ire-irensu daga cikin mashahuran malamai suka yi karatu wurinsa. Wa zai yarda cewa, As-Sadiq ya voye ma waxannan taurari wani karatun da ya bayyana ma jahillai, da al’umma ba ta ko san da zamansu ba?! Babu shakka waxannan malamai da muka ambata da ire-irensu sun fi qaunar Allah da Manzo da kishin tsare addini da isar da shi ga al’umma da son masu son Allah da qiyayya da masu qin sa fiye da shaihunan Shi’ah. Wannan ko shi ne halin ‘yan Shi’ah a kowane zamani. Mutum ya duba lokacinsa. Ga wannan xan Shi’ah da muke magana a kansa. Suna ganin shi ne mafificinsu a wannan zamani. Amma in ya furta wata magana ko kare ba ya ci ba. Sai ya nace a kan maganar da duk mai hankali ya san qarya ce. To, in ya sani ya ya yima Allah da Manzonsa qarya? In kuma bai sani ba ai iya qurewar jahilci kenan.


2.9 Malaman Sunnah Sun fi Qarfin Zargi

A qoqarinsa na xaukaka alqadarin mazhabarsa, xan Shi’ar ya zargi Ahlus-Sunnah yana mai cewa: Babu wani mutum xaya daga cikin Ahlus-Sunnah in dai ya san inda kansa ke ciwo, kuma ya kalli mazhabobi da idon basira, sai ya zavin mazhabar ‘yan-sha-biyu ya bar saura. Amma ta kan yiwu ya voye, ya bayyana akasin haka don neman abin duniya. Tun da an gina masu makarantu da cibiyoyi don su ci gaba da yin farfaganda ga sarakunan Banul Abbas, su sanya qaunarsu cikin zukatan mutane.

Xan Shi’ar ya ci gaba da cewa: Sau da yawa ni kan ga cikinsu wanda yake ibada ta hanyar Shi’anci irin na Imamiyyah (‘yan-sha-biyu), amma ba ya bayyana shi don kwaxayin abin duniya. Na ma tava ganin wani shugaba a mazhabar Hambali yana iqirarin shi xan sha biyu ne. Sai na ce masa: “To, don me kake karantar da Hambaliyyah?” Sai ya ce, “Don wurinku ba masqi!” Kuma babban malamin Shafi’awa a wannan zamani da zai mutu wasicci ya yi da wasu muminai (yana nufin ‘yan Shi’ah) su yi masa wanka. Ya kuma nemi a rufe shi a maqabartar Kazim ta ‘yan Shi’ah. Har ma kuma ya kafa shedu a kan zai mutu bisa mazhabar Shi’ah!
Martani:

Ko shakka babu wanda yake furta wannan magana bai fita daga xayan biyu; ko dai bai san su waye Ahlus-Sunnah ba, ko kuma maqaryaci ne na gidi. Yaushe ne aka kafa makarantu da cibiyoyi? Sunnah ta riga su kafuwa da nisa. A Bagadaza ne aka fara gina makarantu a cikin qarni na biyar. Kamar makarantar Nizzamiyyah an kafa ta a kusan shekarar 460H. Kuma akan mazhaba xaya kacal manhajarta ta ke. A lokacin ma duk mazhabobin Sunnah sun gama yaxuwa a gabascin duniya da yammacinta. Kuma babu wanda yake da makaranta a cikinsu. Malikawa kuma da ke yamma ai basu ko ambaton sarakunan Banul Abbas, balle su yi kira ga a so su.

Kai, a haqiqanin gaskiya ma Sunnah ta fi qarfi kafin kafa daular Abbasiyyah. Domin a zamanin Abbasiyyar ne ‘yan Shi’ah da wasu ‘yan bidi’a irin su suka fara miqe qafafu. Kuma ba wani Ahlus-Sunnah da ya ce halifanci kayan gidan Abbas ne kamar yadda ‘yan Shi’ah kuka ce gadon gidan Ali ne. A wurin malaman Sunnah duk Baquraishe in yana da cancanta ana iya ba shi, Alawi ne ko Abbasi ko Umawi ko ma ba su ba. Zargin magabata shugabannin mazhabobin Sunnah da fadanci ko zargi ne maras tushe. Su malamai ne ‘yan “Sunnah sak”! Amma suna ganin halifofi huxu na farko da gashi, ga shi ko babu xan gidan Abbas a cikinsu.

Duk mai hankali ya san ba a samun xan sha biyu cikin malaman Sunnah. Domin sun fi kowa ganin wautarsu da jahilcinsu da vatan kansu. Kai sun fi kowa nisa daga shiriya. Dole ne a qyamace su, don sun haxa duk sharrin da ke cikin sauran qungiyoyin bidi’ah, kamar Jahamiyyah da Qadariyyah. Waxannan kuwa kowace ta samu rabonta na zargi da suka daga bakunan magabatan al’umma.

Wallahi, duk da yawan nazarce-nazarcena ga maganganun malamai na Sunnah da na Shi’ah ban tava ganin wanda ake zargi da zama xan Shi’ah Imamiyyah daga cikin mutanen kirki ba, balle ko a ce yana qudurta ta a voye. Amma ka ga Zaidiyyah, an tuhumci Hasan xan Salihu xan Hayyu da yin ta. Ga shi ko malami ne na kirki, mai gudun duniya. Amma babu wanda ya ce ya soki Abubakar ko Umar balle ko a ce bai yarda da halifancinsu ba. Daman su Zaidiyyah ba su wannan. Kuma ko ‘yan Shi’ah na farko babu wanda aka zarga cikinsu da ganin fifikon Ali a kan Abubakar da Umar. Suna dai son sa. Kuma cikinsu akwai masu fifita shi a kan Usman. Kuma ko cikin jama’ar Ali xin, waxanda suka taya shi yaqi ba kowa ne ke ganin ya fi Usman ba.

Game da maganarsa kuwa, wai ya ga malaman Sunnah fitattu waxanda a voye ‘yan Shi’ah ne. Sai mu ce masa: Ku ne duniya ta san kuna wannan xabi’a; ku shiga cikin musulmi ku voye aqidarku, kuna ganin wannan wani abin neman kusanci zuwa ga Allah. Kuma a cikin musulmi a kansamu munafuki. To, ina abin mamaki don an samu munafikin xan Shi’ah ya saqe jiki cikin almajiran wata mazhaba ta Sunnah? Wanda ya kafa hujja da irin waxannan munafukai akan vacin aqidar Sunnah shi ne jahili.


Yüklə 2,75 Mb.

Dostları ilə paylaş:
1   ...   7   8   9   10   11   12   13   14   ...   51




Verilənlər bazası müəlliflik hüququ ilə müdafiə olunur ©muhaz.org 2024
rəhbərliyinə müraciət

gir | qeydiyyatdan keç
    Ana səhifə


yükləyin