Tafarkin sunnah



Yüklə 2,75 Mb.
səhifə24/51
tarix28.10.2017
ölçüsü2,75 Mb.
#17506
1   ...   20   21   22   23   24   25   26   27   ...   51

Martani:

Da farko dai, muna tabbatar wa xan Shi’ar cewa wannan magan irin ta ‘yan sandace. Musamman da yake bai faxi yadda ta inganta ba. Baya kuwa kamata ga mutum mai hankali, ya kafa hujja da abin da ba yada toshe balle makama. Don nan take ne za’a iya kwashe masa kafafu. Kamar yadda za mu yi masa yanzu…

Abin da ya tabbata a cikin sahihul Buhari da wasu littafai, ya tabbatar da cewa wannan magana qarya ce. Domin kuwa waxannan ‘yan kwamiti, su ne a qashin kansu, uku daga cikinsu suka zavi salama daga xaukar wannan nauyi suka bar uku. Sannan sauran ukkun kuma suka xorawa Abdurrahman xan Aufu fitar da gwani daga cikin biyunsu, tunda shima ya bi sawun ukkun can na farko kuma Umar Raliyallahu Anhu ba yada hannu a cikin wannan tsari.

Abin da zai tabbatar maka da wannan magana shi ne tabbataccen hadisin da aka riwaito daga Amru xan Maimun, wanda ya ce: kafin shexar Umar Raliyallahu Anhu ta qarshe ta kai ga bugawa, a lokacin da aka soke shi, ya ce: tun kafin yau wasu mutane ke neman in nada magaji, don kada a sami tajin-tajin bayan na wuce. To na danqa wannan al’amari hannun sababban nan shida. Waxanda ko da Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama ya rasu yayi matuqar yadda da al’amarinsu, wato: Ali da Usman da Xalhatu da Zubairu da Abdur-Rahmanu xan Aufu da Sa’adu xan Maliku Raliyallahu Anhu sannan Abdullah xan Umar ya zama Alqali. Amma kada su kuskura su zave shi a matsayin halifa.

Idan Allah ya sa Sa’adu ne suka zava, daidai. Idan kuwa wani ne, to ina horonsa da ya yi aiki da shi. Domin kuwa ba wata kasawa ko yaudara ce tasa na tuve shi ba.

Daga nan kuma sai ya ce: ina yi wa duk wanda Allah ya xorawa wannan nauyi, bayan na wuce, wasiyya da tsoron Allah Ta’ala. Kuma don Allah ya tsare alfarmar muhajiru na. mutanen nan na farko da aka zava da gidajensu da dukiyoyensu don kawai sunce Allah, ya kuma ba su haqqinsu. Haka kuma don Allah ya kula da Ansaru. Mutanen nan da suka saxaukantar da gidajensu, suka kuma yi imani tun gabaninsu, duk abin da suka yi na kyautatawa ya qarva, ya kuma yafe kura - kurarsu haka kuma ina yi masa wasiya daya kula da mutanen sauran garuruwa, yayi tayi man alheri. Domin kuwa ba don su ba, da musulunci bai kai labari ba, sun turawa magabata haushi. Suna kuma tsaye haiqan ga tara haqqin Allah na dukiya. Kada ya kula da wani abin da suka yi ko za su yi, sai na alheri kuma ya jira sai sunci sun raga, sannan a nemi yardarsu a kan saura. Haka kuma Larabawan qauye, suma don Allah ya kyautata masu. Don sune tushen Larabawa da makamashin musulunci. Idan aka tashi karvar zakka daga gare su, a kuma raba ta ga talakawa daga cikinsu. Haka kuma kafiran amana, don Allah ya tabbata ya cika duk arqawarin dake tsakaninmu dasu, bisa yardar Allah da Manzonsa. Ya kuma yaqi duk wanda ke dagagensu. Kada kuma ya xora masu duk abin da basu iyawa.

To ka ji iyakar abin da Umar Raliyallahu Anhu ya ce, gab akin wanda ba ya qarya.

Mun qare da wannan. Bari mu koma ga cewar da xan Shi’ar yayi, kuma wai Umar ya ce: idan bakin Ali da Usman Raliyallahu Anhu ya haxu to, duk wanda suka zava ya zavu. Idan kuma suka kai su uku, wato kwamitin ya rabu gida biyu, to duk wanda inda Abdur-Rahman, yake suka zava ya zavu. Kuma wai inji xan Shi’ar Umar Raliyallahu Anhu ya yi haka ne don ya san ba yadda za a yi bakin Ali da Usman Raliyallahu Anhu ya haxu a kan wani al’amari, haka suke kamar Annabi da kafirci. Kuma wai halifan ya san da cewa Abdur-Rahman ba zai kasa zaven xan Ammininsa Usmanu ba.

To a nan, muna son xan Shi’ar ya gaya mana wanda ya ce Umar Raliyallahu Anhu ya ce haka. To kuma tafi. Ko da ta tabbata ya ce haka xin, baya halatta da dacewa a yi masa irin wannan fassara, cewa ya kutsa haka ne don yana son a zavi Usman, yana kuma kyamar a zavi Ali Raliyallahu Anhu. Ai inda wannan itace manufarsa, to kai tsaye tun farko, zaice na zavi Usman ya gaje ni. Kuma babu wanda zai yi gigin musa - masa. don kuwa gashi bayan ma ya qaura xin Usman xin ne aka zava. Wanda hakan ke nuna suna son sa fiye da kowa. Kuma inda ma hakan yayi, to alqadarin Usman xin zai fi fitowa, don xa’arsu gare shi za tafi kauri a matsayinsu na mutane masu son addini da rajen aikata alheri da tabbatar da adalci. Kamar yadda muminai suka shede su. Kai I ko da akasin haka suka kasance. Kamar yadda munafukai ke zarginsu, ba za su kasa fesawa wannan zave na Umar turaren xa’a ba.

Ko shakka babu, da wannan itace manufarsa, kamar yadda na faxa a baya kaxan. To babu abin da zai hana shi tabbatar da ita, kai tsaye ba tare da wasu kewaye - kewaye ba. Tunda ba wanda yake tsoro. Wanda har hakan tasa ‘yan Shi’ah nace masa: Fir’aunan al’ummar Muhammadu.

Kai kasan idan dai har halifa Umar Raliyallahu Anhu ba zai ji shakkun miqewa ba shi kaxai, ya zavi Abubakar Raliyallahu Anhu a matsayin magaji Muhammadu Sallallahu Alaihi Wasallama ba. Ba kuwa zai ji shakkar tabbatar wani, ko ba Usmanu Raliyallahu Anhu ba, da halifanci bayansa ba. A lokacin da mutane suka riga suka saba da biyayya, musamman gare shi.

Ka ga a hankalce Umar Raliyallahu Anhu ba yada buqatar shirya irin wannan qungiya - qungiya don tabbatar da irin wannan sassauqar manufa. Kuma tafi na ji. Wai ma me zai ba Umar yaqi Ali saboda Usman Raliyallahu Anhu? ai babu wata alaka dake tsakaninsa da Usman fiye da Alin Raliyallahu Anhu wadda zata wajabtar da faruwar haka. Babu wata kariya tsakaninsu ta qabilanci ko akasin haka balle a ce.

Ko harma a ce wai: Umar Raliyallahu Anhu ya san ba yadda za a yi bakin Ali da Usman Raliyallahu Anhu ya haxu a kan wani al’amari xaya. Wai Shi ya sa ya shirya waccan munqisa.

Haba! Wace irin qiyayya ce wannan?

Wannan magana qarya kawai aka yi wa halifa Umar Raliyallahu Anhu domin kuwa ba a tava ganin halifofin a rana biyu ba, tsawon rayuwar halifan. Hasali ma dangantakar dake tsakaninsu, babu ta tsakanin xayansu da wani daga cikin sauran manbobin kwamitin gida huxu. Domin duka su biyun bani Abdulmunafi ne. Mutanen da kodayaushe kansu haxe yake tsawon tarihi.

Haka kuma cewar da xan Shi’ar ya yi wai halifa Umar Raliyallahu Anhu ya san cewa Abdurrahman ba zai kasa zaven Usmanu Raliyallahu Anhu ba, a matsayinsa na xan ammininsa, qarya ce kawai.

Na farko dai Umar bai da alaqa da wannan magana. Na biyu kuma babu wani zumunci tsakanin Abdurrahman da Usman Raliyallahu Anhu balle ya zama xan ammininsa. Kai i hasali ma ba ’yan qabila xaya bane. Abdurrahman xan qabilar bani Zahrata ne. shi kuwa Usman xan qabilar bani Umayya ne. kuma ma hulxar jakadancin dake akwai tsakanin banu zahrata da banu hashim tafi wadda ke tsakaninsu da banu Umayyata nesa ba kusa ba. Domin su banu Zahrata xin kawanni ne ga Annabi Sallallahu Alaihi Wasallama kuma daga cikinsu ne shi Abdurrahman yake. Har ma da Sa’ad xan Abi Wakkasin, wanda har watarana Annabi yayi alfahari da shi, da cewa: Sa’ad xaya ne daga cikin kawannina, mutum ya gwada mani nasa kawon.

Kai ba wannan dangantaka ta jini ba. Ko da irin zumuncin nan na musulunci babu shi tsakanin Usman da Abdurrahman. Domin kuwa Annabi Sallallahu Alaihi Wasallama bai qulla irin wannan zumunci tsakanin Muhajiruna ko Ansaru wasu - wasu ba. Ya dai qulla shi ne tsakanin jinsunan mutanen biyu. A inda shi Abdur-Rahman a matsayinsa na muhajiri ya zama xan’uwan Sa’adu xan Rabi’u Ansari. Sahabin da keda hadisi shahararre a cikin Sihahu da wasu littafai. Babu wani malami a cikin wannan fanni da bai san da shi ba. Amma Annabi Sallallahu Alaihi Wasallama bai qulla irin wannan zumunci tsakanin Usman da Abdur-Rahman ba. Balle ace ko don shi ya zave shi. Kai! Hasali ma, ko irin wanan hulxa ta rayuwar duniya Usman bai cika yi dashi, balle.

Sannan kuma idan tsawon wannan mujadala bai sa ka manta ba. Xan Shi’ar ya ce wai kuma: Umar ya yi umurni da a kashe ‘yan kwamitin idan suka kasa yi wa xayansu bayi’a har tsawon kwana uku.

Ina fatar ka tuna.

To da farko dai wannan magana qarya ce. Ko kuma idan xan Shi’ar na musu, to ya gaya mana wanda ya inganta ta. Ko tabbataccen asalinta.

Abin da kawai ya tabbata a tarihi shi ne, halifan ya hori Ansaru da cewa kada suyi nesa da kwamitin har sai an zavi wanda aka zava an kuma yi ma sa bai’a.

Sannan kuma abu na biyu: Wannan magana kamar yadda muka faxa, qarya ce. Babu wani ma’abuci ilimi daya riwaito ta. Kuma ma dai ai abin ya savawa hankali Umar Raliyallahu Anhu ya yihoro da kashe waxannan Sahabbai. Alhali ya san babu kamarsu a wannan al’umma. Kuma idan aka kashe su, lalle sai an yi da an sani irin matsanancin fasalin da zai faru, dalilin haka. Kuma inda gaskiya ne ya bayar da wannan umurni, to lalle ne a samu ko ya ce: bayan kun kashe sai ku naxa wane da kowane. dole ne a samu haka. Don bata yiwuwa mai hankali ya karva wa makaho sanda, ba tare da ya ba shi wata ba. Daxa ko ko ta raga ce.

Ka ga a haka wannan xan Shi’ar ya tabbata maqryaci, irin wanda bai san abin daya kamata ya rubuta ba, shar’ance da al’adance.

Kuma ma wani abin ban mamaki dake kasa tabbatar maka da cewa rashin kunyar fafilawa ya vaci shi ne, cewa suka yi wancan kisa da Umar Raliyallahu Anhu ya yihoro da shi ayi wa ‘yan kwamitin. Hukuncin ya dadare dasu amma banda gogan nasu Ali Raliyallahu Anhu.

To mu qaddara cewa gaskiya ne ya bayar da umurnin. To ya za a yi da cewar can kuma da suka yi wai yana matuqar son sune ban da Ali don haka ya taqaita halifancin a da’irarsu?

Ka ga a haka kamar suna sone su haxa ruwa da wuta ne wuri xaya.

Wannan kenan. Amma kuma na san saboda tsananin kangara. ‘yan Shi’ah na iya cewa, Umar Raliyallahu Anhu ya bayar da wancan umurni ne kawai. Amma Ali Raliyallahu Anhu kawai yake nufin a kai.

To sai mu ce masu: wannan ma ba ta savo, wai bindiga a ruwa. Yau da gaba xayan ‘yan kwamitin za su yi mubaya’a ga wanda suka zava. Amma Ali Raliyallahu Anhu ya qiyi, hakan ba zai hana naxin yiwuwa ba. Balle har a nemi kau da shi. Ga al’adar irin wannan sha’ani na shugabanci ana gafartar da wanda ake jin yana iya kawo tsagaro gare shi ne idan ya wandare. Ai ka ga Sa’adu xan Ubaidata bai yi wa Abubakar Raliyallahu Anhu bai’a ba amma ko jan ido ba a yi masa ba. Balle xauri ko duka. Daxa balle kashi.

Ka dai sake vulo mun daddale wannan.

Kuma ai ka ga akwai masu cewa Ali Raliyallahu Anhu da gaba xayan banu Hashim, duk ba su yi wa Abubakar Raliyallahu Anhu bai’a ba sai bayan wata shida. Amma kuma kafin haka babu wanda ya yi masu ko jan ido balle duka, ko tilasta su bai’ar. To bai’ar Abubakar Raliyallahu Anhu kenan wadda gaba xayan Sahabbai ke jin wajibi ce a kansu. Ka ga ya savawa hankali matuqa wannan bai’a ta Usmanu. Wadda ko shi kansa Umar xin bai wajabtawa kansa balle wani.

To, aje ma duk wannan. Tarihin musulunci ya tabbatar da cewa tsawon lokacin halifancin Abubakar da Umar Raliyallahu Anhuma sahabba na matuqar karrama Ali Raliyallahu Anhu da sauran bani Hashim, fiye da yadda suke karrama sauran mutane. Harma an riwaito Abubakar Raliyallahu Anhu kan ce: ya ku mutane! ku kiyaye alfarmar Muhammadu Sallallahu Alaihi Wasallama ta hanyar tsare mutuncin mutanen gidansa.

Kuma yakan taka da kafafunsa har gidan Ali Raliyallahu Anhu a inda yakan taras da banu Hashim anjin. Ya zauna suyi taxi: ya ba su girman suna kasancewa dangin Manzon Allah. Su kuma su bashi nashi na kasancewa halifa kuma shugabansu, harma suyi masa jinjina. A irin wannan haxuwa ce suka bashi haquri a kan rashi yi masa bai’a cikin dubu. Nan take kuma suka yi ta xaga su sai shi.

Bayan haka kuma dubban dalilai, sun tabbatar da cewa akwai matuqar qauna da fahimtar juna tsakanin Ali Raliyallahu Anhu da waxannan sabahabbai biyu. Abin da kuma ire-iren wannan shaqiyin xan Shi’a ke faxa qarya ne. Ah! qarya ne mana. Kai ka san da Sahabban na da qudurin cutar da Alin Raliyallahu Anhu a lokacin da suke halifofi suna da wannan iko. Ba sai sunyi qoqarin yin haka ta kure shi daga halifancin ba. Abun bai kai can ba.

Qarya ce da rennin hankalin mutane ‘yan Shi’ah ke yi, suce wai Sahabban sun zalunci Ali Raliyallahu Anhu a daidai lokacin da yake iya yi wa kansa faxa. Amma kuma sun kasa zaluntarsa a lokacin ba su da wani qarfi ko iko a kan haka, ko da sun so. Ka ga a hankalce, lokacin da suka yi qarfi ne, mutane na sauraransu ya kamata ace sun zalunce shi xin, da suna da kudurin haka ko?

Haka kuma ita ma cewar da xan Shi’ar ya yi wai Umar xin ya yi wani umurnin da kashe duk wanda ya savawa mutum huxu ko uku da bakinsu yazo xaya, kuma cikinsu da Abdurrahman, qarya ce.

To muma qaddara ya ce hakan, to sai me kuma? Ai hakan ba ta savawa addini ba. Hakan ma yafi dacewa. don a kashe wanda ke son tayar da fitina ibada ne. kamar yadda Annabi Sallallahu Alaihi Wasallama ya ce: duk wanda ya taras daku tsintsiya maxaurinki xaya, kuna da’a ga mutum xaya, ya nemi raba kanku, to ku sare kansa da takobi ko xan waye.

Abin da kawai ya tabbata shi ne Umar Raliyallahu Anhu ya yi umurni ne da kashe duk wanda ya yi wa wani bai’a, ba tare da ya shawarci sauran musulmai ba. Kuma ya dogara ne akan wannan hadisi da ya gabata.

Amma kashe wani don xai ya qi yin bai’a, bai kuma nemi tayar da wata fitina ba, balle raba kan musulmai. Umar Raliyallahu Anhu bai yi wannan umurni ba. Hasali ma kashe irin wannan mutum ba ya halatta.

Haka kuma isharorin da xan Shi’ar ya ambata wai na kashe Usman da qin zaven Ali Raliyallahu Anhu duk qarya ne, Umar bai qulla haka ba.

Cewar da Abdur-Rahman yayi : idan ka aikata (kaza) wallahi suna kashe ka. Labari ne kawai yake bayarwa, ko ya riga ya bayar ba. Kamar yadda cewar da ya yi: ba za su zave shi ba. Ita ma labarin abin da yake ganin zai faru ne kawai yake bayar wa. Ba wai umurni ne yake bayarwa da aikata hakan ba.

Duk da yake gaba xayan waxannan lafuzza, a cikin irin wannan siyaki basu tabbata daga bakin halifa Umar Raliyallahu Anhu ba. qarya ce aka yi masa.

Allah Ta’ala shi ne mafi sani.
2.57 Xan Shi’ar ya Dira A Kan Usman

Dama na gaya maka cewa ina zaton xan Shi’ar nan zai ta kan halifofin nan uku ne, xaya bayan xaya. Ga shi tako tabbata. Ya qare da Umar bayan Abubakar Raliyallahu Anhu yanzu kuma ya dira kan Usmanu Raliyallahu Anhu inda ya fara sukar lamarin halifan da cewa:

shi kuwa Usmanu, babban laifinsa shi ne xaukar muqami ya danqawa waxanda ba su dace dasu ba. wanda hakan tasa a qarshe, babu abin da suka sukkuna wa jama’a, in banda yaxa fasiqanci da varna a bayan qasa. Wani kuma daga cikinsu suka xaure wa zalunci gindi. Kuma abin ban ta kaici, inji xan Shi’ar duk waxanda yaba muqaman nan ‘yan‘uwansa ne na kusa. Saboda haka, da mutane suka yi qorafi a kansa, yayi kunnen uwar shege dasu.

Ka ga Walidu xan Ikibata, wanda halifan ya naxa gwamna, babu abin da ya aje sai shan giya. Har watarana ta kai shi gaba mutane salla yana lage. Shi kuwa Sa’idu xan Asi wanda halifan ya kai Kufa, aika - aikar da ya yi bata faxuwa. Wadda har tasa mutanen garin suka kore shi. Sai Abdullahi xan Sa’ad xan Abi Sarhu, wanda ya kai masar. Shi kuwa saboda tsanancin zaluncinsa saida talakawansa suka kawo qararsa wurin halifan. Amma saboda qin Allah, sai halifan ya aika masa a rubuce, cewa wannan ba komai bane, Ya ci gaba da mulkinsa yadda ya saba. Ya aika masa da wannan saqo ne asirce, savanin abin da ya rubuta masa a bayyane. Ya kuma yi masa umurni da kashe wani mutum da ake kira Muhammad bin Abubakar.

Haka kuma dai inji xan Shi’ar, Usman ya naxa Mu’awiyah gwamnan sham, inda yaje ya shimfixa maqaqiyar tabarmar fitina, haka kuma ya kai Abdullahi xan Amru a busra. Shima yayi ganin damarsa a can. Qarewa da qarau ma, sai ya danqa wa Marwanu ragamar gudanar da komai. Har da tasarrafi da hatiminsa na halifanci. Wanda a qarshe hakan ta zama sanadiyar kashe Usmanu Raliyallahu Anhu wutar fitina ta kama sosai a cikin al’umma. Kafin haka inji xan Shi’ar, halifan ya kasance yana xibar dukiya mai yawa daga baitil mali yana ba ‘yan’uwansa da iyalinsa. Wanda har watarana ya xibi dinari dubu xari huxu yaba wasu kuraishawa huxu dake auren ‘yayansa mata. Ya kuma ba Marwanun can dinari dubu biyu.

Ya ci gaba da cewa: Usmanu ne, bayan yahau gadon halifanci, yasa aka yi wa xan mas’ud dukan tsiya, har saboda yana suka tare da kafirtarsa har ransa ya fita. Haka yasa aka yi wa Amru har fatar jikinsa ta farfashe. Alhali kuwa Annabi Sallallahu Alaihi Wasallama ya ce: Amru wata fata ce daga cikin fatun idona. Kuma ina jin wasu la’ananni ne za su kashe shi. Waxanda nake fatar Allah ba zai sasu cikin cetona ba, ranar qiyama. Shi ma Amru ya sami wancan xanyen hukunci ne saboda sukar halifan da yake yi.

Haka kuma wai kafin Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama ya kwanta dama, sai da ya kori ammin halifan, Hakamu xan Abilas, tare da xansa Marwan daga birnin Madina. Birnin da ya yi masu qarshen xan goma tsawon rayuwar manzon da halifa Abubakar da Umar Raliyallahu Anhuma amma wai hawan Usmanu karagar keda wuya sai ya dawo dasu birnin. Ya kuma naxa Marwanun magatakardansa, kuma sarkin fada. Alhali Allah Ta’ala ya ce: Ba zaka sami mutane masu yin imani da Allah da Ranar lahira ba suna soyayya da wanda ya sava wa Allah da manzonsa, ko da sun kasance ubanninsu ne, ko xiyansu (58:22).

Kuma inji xan Shi’ar, Usman Raliyallahu Anhu xin dai ne wanda ya kori Abu Zarrin daga Madina ya koma Rabzata, bayan shima ya yi masa xan Karen duka. Alhali kuwa Annabi Sallallahu Alaihi Wasallama ya ce: kasa bata tava xaukar wani mutum mai faxin gaskiya inuwa ba kamar Abu Zarri. Ya kuma ce: haqiqa Allah ya yi mani wahayin cewa akwai wasu Sahabbai nawa da yake matukar so. Saboda haka ni ma ina so su. Sahabbai suka tambaye shi su waye waxannan ya Manzon Allah? Sai ya ce : limaminsu shi ne Ali, sai Salmanu da Miqdad da Abu Zarri.

Kuma wai halifan ya keta alfarmar hukuncin Allah. Saboda yaqi kashe Ubaidullahi xan Umar wanda ya kashe Hurmazanu bawan Ali Raliyallahu Anhu wai Alin ne ya tashi tsaye yana qarsheta dai wurin Mu’awiyah ya fake . kuma wai halifan yaso yaqi zartar da hukuncin shan giya ga Wahdu xan Ukbata, saida Ali Raliyallahu Anhu ya karvi aikin a hannunsa ya zartas, yana mai cewa: bata yiwuwa a tozarta hukuncin Allah ina nan kuma raye.

Haka kuma wai Usman Raliyallahu Anhu xin ne ya bidi’ar da kiran salla na biyu a ranar juma’a. har aka wayi gari hakan ta zama sunna a yau. Kuma wai saboda waxannan halaye ne nasa, gaba xayan musulunci suka juya masa baya har suka aika shi lahira, tare da yin Allah waddai da ayyukansa. Suka yi masa rakiya da cewa : kaqi fita yaqin Badar, ka fita na Uhudu ka gudo. Kuma bada kai aka yi bai’atur - Ridhwan.

Xan Shi’ar ya kamala da cewa: irin waxannan miyagun labarai a kan Usmanu ba su da iyaka.

Martan: kafin mu shiga fixar wannan magana dalla-dalla tare da warwarar zare da abawarta, muna tabbatarwa xan Shi’ar da cewa, ai ba lalle Sarkin mugun ba faxa ya zama mugu. Kuma daga tai dahakimai su cuci sarkinsu, a tarihin musulunci bag a halifa Usmanu aka fara ba. Cutar da wakilan Ali Raliyallahu Anhu a garuruwa suka guma masa, tare da yin yamma a duk lokacin da ya yi gabas, tafi wadda wakilan Usman Raliyallahu Anhu suka yi.

Akwai rubuce-rubuce da dama da aka yi a kan wasu waqilai da Alin Raliyallahu Anhu ya naxa suka kwashe dukiyar talakawansu. Wasu kuma suka bar shi, suka koma gindin Mu’awiyah. Kuma ta tabbata Alin Raliyallahu Anhu yayi aiki tare da Zayyadu xan Abu sufyanu, baban Abdullahi xan Zayyadu, makashin Husaini, a matsayin waqilinsa. Haka kuma yayi da Al-ashtar An-Nakh’i da Muhammad xan Abubakar da makamantarsu. Duk a wannan matsayi. Kuma kai kasan Mu’awiyah xan Abu Sufyanu Raliyallahu Anhu yafi duk waxannan zama mutumin kirki ga duk mai hankali.

Sannan kuma naxa ‘yan’uwa da makusanta muqamai baga halifa Usmanu Raliyallahu Anhu ne karau ba. Balle ‘yan Shi’ah su addabe shi damu. ai tarihi ya gaya mana cewa a lokacin da Ali Raliyallahu Anhu ya zama halifa shima ya naxa nasa ‘yan’uwa da makusanta, na wajen uwa da uba. Kamar irin su: Abdullahi da Ubaindullahi ‘’ya’yan Abbas. Ya kai Ubaidu a yaman, Qasimu xan Abbas xin kuma Makka da Daya. A Madina kuma ya naxa Sahlu xan Hunaifu a matsayin gwamna. Wasu malaman tarihi kuma suka ce: a’a Samamatu xan Abbas ne ya kai can. A yayin da ya kai Abdullahhin can xan Abbas, harwayau, Barra. A masar kuma ya kai xan ‘yaye da renonsa, wato Muhammad xan Abubakar.

Kuma qarewa da qarau ma, saboda tsananin mamaya, handama da babakere, Aliyun Raliyallahu Anhu bai bar duniya ba saida ya yi wasicci a kan kada a fitar da halifanci daga hannun zu’arsa, xaya bayan xaya. Kamar yadda Shi’ah ‘yan-sha-biyu ke faxawa duniya.

Ina fatar xan Shi’ar ya san wannan tarihi:

Kuma kai mai karatu, ka san idan wanda ya naxa danginsa sarautu da muqamai ya yi wani abin qi da kyama. To abin da waninsa yayi a qaqaice masu uwar muqamai, wato halifancin yafi zama laifi. Musamman kuma idan aka taras ‘ya’yansa da jikokinsa ne, ya yi wa wancan qaqacin ba danginsa ba a wajen Uba kamar yadda wancan yayi. Kuma ma a kan wannan ma’auni ne wasu malaman fiqihu suka yanke hukuncin cewa, duk wani waqili ko waliyin da baya isarwa kansa ga wata hulxa ta ciniki, to baya halatta ya waqilci xansa a irin wannan mu’amala. Kuma ko da dukiya ce aka ba shi don yayi kyauta da ita ga duk wanda yaga dama, to wanda yaba shi ba zai karvarwa kansa ko xansa ita ba, a xayan zantukan.

Haka kuma malaman sun karu da junansu sani, a kan halacci da yiwuwar halifa ya yi wasicci da xansa ya gade shi. Wasu suka yarda da ha kan wasu kuma suka ce, faufau. Kuma a wurin mafi yawan malamai, ba a karvar shedar mahaifi ga dansa. Amma shedar mutuma ga ammininsa karvavva ce. Haka hukuncin yake a cikin sauran hukunce-hukunce.

Wato abin da muke son fitarwa a nan shi ne, a shar’ance, xa da mahaifi abu xaya ne ya rabu biyu. Haka kuma abin da ke tsakaninsu na haqqoqi. Kamar yadda Annabi Sallallahu Alaihi Wasallama ya ce: da mutum da dukiyarsa duk mallakar mahaifinsa ce. Ya kuma ce: babu wanda keda xamar tayar da kyamutar da ya yi. Sai fa idan xan cikinsa ya yi wa.

Wannan kenan. Amma kuma da ‘yan Shi’ah za su ce: Ai Ali Raliyallahu Anhu yayi abin da ya yi ne da umurnin Allah da Manzonsa.

To sai mu ce masu: Eh! To, ba mu musun kasancewar Ali Raliyallahu Anhu halifa nagartacce, kamar yadda Usmanu Raliyallahu Anhu yake. Amma kuma koba musan dalilin kowanensu ba, a kan abin da ya yin. Duk mai hankali zai fi shakku da zargin Ali fiye da Usman Raliyallahu Anhu.

Amma kuma na san ‘yan shi’ah za su kawai qale ni biris ne, suce wata qila ko ban gane abin da suke nufi ba. Alhali kuwa na gane.

Suna sone suce: Ali na da hujja a kan wancan aiki da ya yi.

To naji na kuma yarda. Amma ina tabbata masu hujjar da Usmanu Raliyallahu Anhu keda ita tafi tasa nesa ba kusa ba. Don na san iyakar abin da za suce shi ne, ai Ali Raliyallahu Anhu Ma’suni ne, duk abin da ma ya aikata daidai ne a shari’a. saboda haka sai a kame baki daga sukar sa haka nan. To wannan ma naji kuma na yarda. Amma kuma ina tabbatar masu da cewa hujjar da kega Usman Raliyallahu Anhu ta kasancewarsa mujtahidi, tafi iya sa masu sukar sa su saurara, ta kuma fi zama kusa ga hankali da naqali.

Allah dai ya sawwaqa.

Idan ka kwantar da hankali , za ka fahimci cewa iyakar abin da xan Shi’ar ke guri da wannan aiki nasa tun farkonsa, shi ne ya shafawa mutanen da lafiyayyen hankali da ingantaccen naqali suka tabbatar da fifikonsu a kan takwarorimu qashin kaji. A lokaci xaya kuma ya yi wa waxanda ake bin wancan tsarki. Duk ta hanyar sukar wadancan da yabon waxannan, kamar yadda Nasara suka yi tsakanin Annabawan Allah. Suka qasqanta darajar waxanda Allah ya xaukaka daga cikinsu, tare da nuna darajarsu bata ko kai ta Sahabban Annabi Isa Alaihis Salamu ba. Shi kuwa Isan Allah ma sukutum.

Babban abin ban ta kaici da mamaki ma duk bai fi yadda suka naxawa Sahabban na Annabi Isah Alaihis Salamu rawanin ma’asumanci ba. Tattare da kasancewar darajarsu ko gata Annabawa ba ta kai ba. A lokaci guda kuma suna sukar lamirin Annabawan. Kamar Annabi Sulaimanu da waninsa.

Kai! Ba Sulaimanu kawai ba. A wajen nasara darajar Sahabban Annabi Isah Alaihis Salamu tafi ta Annabi Ibrahim da Muhammad Alaihis Salamu ka kuwa san dalilai da yawa na shari’a sun tabbatar da fifikon darajar waxannan Annabawa biyu a kan Isan kansa, balle Sahabbansa. Amma kaji aqidar nasara a kansu.

Irin wannan aiki na jahilci kuwa, da shishshigi na daga cikin abubuwan da Allah Ta’ala ya hana nasara yi. Inda ya ce: Ya mutanen littafi! Kada ku zurfafa a cikin addinku. Kuma kada ku faxa ga Allah face gaskiya. Abin da aka sani kawai, Al-Masihu Isah xan Maryama Manzon Allah ne, kuma kalmarsa, ya jefa ta zuwa ga Maryama, kuma ruhi ne daga gare shi (4:171).

To yadda ka ji haka, haka ‘yan Shi’ah suke, su da Nasara ba wani banbanci.

Eh! Ba wani banbanci mana a tsakaninsu. Tunda su ma shishshiginsu yasa sunce Ali Raliyallahu Anhu Allah ne. to ka ga a nan ma har gwamma Nasarawa dasu. Don Isa Annabi ne, to Ali fa. A yayin da wasu ragilawan ke cewa Annabi dai ne shi Alin ba Allah ba. To ka gasu waxannan dai- dai suke da mabiyan Musailamatul-Kazzabi, waxanda suka yarda da wani Annabi bayan Muhammadu Sallallahu Alaihi Wasallama illa dai shi Ali Raliyallahu Anhu ba yada wani laifi cikin wannan al’amari. Don ba shi ne ya kira kansa Allah ko Annabi ba. Savanin Musailamatu da takwarorinsa.

Su kuwa Shi’ah ‘yan-sha-biyu abin da suke iqirari shi ne, imamancin Ali Raliyallahu Anhu tabbataccen abune bisa nasu. Kuma shi da, da yawa daga cikin zuri’arsa duk ma’asumai ne. Kuma wai sauran Sahabbai sun zalunce su.

Ma’asumancin nan da kake ji, ma’anarsa a wurinsu daidai take da ta Annabci. Domin kuwa wajibi ne wai a yi wa ma’asumi xa’a a cikin duk abin da ya faxa, sava masa haramun ne. Ka kuwa san Annabawa kawai ne keda wannan matsayi. Saboda sune Allah Subhanahu WaTa’ala ya umurce mu da yin imani da abin da aka saukar masu, inda ya ce: ku ce: “mun yi imani da Allah, da abin da aka saukar zuwa gare mu, da abin da aka saukar zuwa ga Ibrahim da Isma’ila da Ishaka da yaqubu da Jikoki, da abin da aka bai wa Musa da Isah, da abin da aka bai wa Annabawa daga Ubangijinsu, bamu rarrabewa a tsakanin kowa daga gare su, kuma mu a gare shi masu salamawa ne (2:136).

Ka ga a nan Allah ya umurce mu damu ce: mun yi imani da abin da aka ba Annabawa. Kuma gaba xayan musulmi sun yi ittifaqi a kan cewa imani dakowane Annabi wajibi ne. duk kuwa wanda ya kafirce wa waninsu to kafuri ne. idan da kuma izgilin zagin xaya daga cikinsu wani yayi to jininsa ya halatta inji malamai.

Wannan matsayi kuwa na Annabawa ne kawai, babu wani wAliyu ko shugaba ko fasihi ko malami ko waninsu da keda irinsa. Duk kuwa wanda ya ce ga wani mutum wai shi ma’asumi ne da imani da duk abin da ya faxa yake wajibi, bayan Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama to yana aufin shi ma Annabi ne.

Eh! Haka yake nufi mana ko da kuwa bai ambace shi da sunan ba. Kuma babu wani banbanci tsakanin wannan da Annabawan bani Isra’ilu.Waxanda aka umurta biyar shari’arttawa.

Wannan kenan. Sannan kuma sanannen abune cewa irin waxannan kudurce - kudurce na wuce gona da iri, da qoqarin samarwa da wani gunki a haxa shi da Allah da manzonsa a bauta, ya savawa Addinin Musulunci, Alqur’ani da Sunna da ijma’in al’umma da malamanta duk ba su yarda da haka ba. Ga kuma abin da Allah Ta’ala ke cewa: Ya ku waxanda suka yi imani! Ku yi xa’a ga Allah, kuma kuyi xa’a ga manzonsa, da ma’abuta al’amari daga cikinku. Idan kun yi jayayya a cikin wani abu, to ku mayar dashi zuwa ga Allah da manzonsa (4:59).

Ka ga ashe kenan duk wanda ya samar da wani mutum ya kuma ce ma’asumi ne, bayan Manzon. Wanda kuma duk abin da ya faxa gaskiya ne. to yana nufin kenan wajibi ne a mayar da abin da ya faskara gare shi. Wannan kuwa ya savawa umurnin Alqur’ani.

Domin kuwa Manzo ne kawai Alqur’ani ya wajabta yi wa xa’a maras adadi, ba ma’asumi ba kamar yadda Shi’ah ‘yan-sha-biyu ke cewa, ya kuma tabbbatar da alwashin farko ga duk wanda ya sava masa. Tabbataccen wannan magana. Shi ne abin da Allah Ta’ala ke cewa: Kuma waxannan da suka yi xa’a ga Allah da Manzonsa, to, waxannan suna tare da waxanda Allah ya yi ni’ima kansu daga Annabawa da masu yawan gaskiya, da masu shahada, da salihai. Kuma waxannan sun kyautatu ga zama abokan tafiya (4:69). Ya kuma ce: to, wanda ya savawa Allah da Manzonsa, to, lalle yana da wutar jahannama, suna masu dawwama a cikinta har abada (27:23).

Ka ga anan da wurare da dama Alqur’ani ya nuna cewa gidan aljanna shi ne sakamakon wanda ya yi xa’a ga Manzo. Amma bai sharxanta haka ga wani don yayi xa’a ga wani wai shi ma’asumi ba duk kuwa irin yadda zai yi xa’a ga ma’asumi to makomarsa ita ce wuta, matuqar bai yi xa’a ga Manzo ba.

Domin Manzo Sallallahu Alaihi Wasallama shi ne Alfijirin da Allah ya ware ‘yan aljanna daga ‘yan wuta da shi. Ya kuma sa shamaki tsakanin fajirai da nagatattun bayi da albarkarsa. Ya kuma yi katangar qarfe tsakanin qarya da gaskiya, da bata da shirya, da sanadarinsa. Wanda kuma tahowarsa ce ta kafawa shaqiyai tasu bukka daban, ta kuma kafa wa Sa’idai tasu. Shi ne wanda ake yi wa xa’a a rabbanta, a saba masa a vakita. Babu kuma mai irin wannan daraja sai shi Sallallahu Alaihi Wasallama.

A kan haka ne, kan gaba xayan malaman da suka naqalci sirrin Alqur’ani da sunna, ya haxu a kan cewa babu wanda yafi qarfin a xauki maganarsa in anso, ko a saka ta kwandon shara in anso sai mijin Khadija baban Zainab Sallallahu Alaihi Wasallama shi kan wajibi ne duk abin da ya faxa a gasgata, duk abin da ya yi umurni kuma a aikata. Saboda shi ma’asumi ne da komai ya faxa umurni ne daga Allah Subhanahu WaTa’ala ba son zuri’arsa ba. Don baya dashi. Shi ne kuma wanda Allah zai tambayi mutane a kan yadda suka xauke shi, ranar qiyama. Kamar yadda Allah Ta’ala ya faxa mana: sa’annan lalle ne muna tambayar waxanda aka aika zuwa garesu, kuma lalle muna tambayar manzanni (7:6) .

Shi ne kuma wanda Allah zai jarraba mutane a kansa, a cikin qaburburansu yasa ace wakowannensu: waye Ubangijinka? Mene ne kuma Addininka? Kuma wanene Annabinka? Wace irin sheda kake iya bayarwa a kan manzon da aka aika maku? A nan ne Allah zai taimaki masu imani na gaskiya, ya ba su ikon cewa: Annabinmu dai shi ne xan Abdullahi (Muhammadu) bawan Allah ne kuma Manzonsa. Ya zo mana da walihahhen abubuwa da shirya kuma munyi imani dashi mun bishi.

Da mutum zai kuskure ya ambaci wani ba Muhammadu Sallallahu Alaihi Wasallama ba, kamar wani Sahabi ko tabi’i. Ko wani malami, to kashinsa ya bushe. Don lokacin ba a son jin sunan kowa in ba shi ba.

A taqaice dai, kada inji ka da nisa. Abin da kawai muke son tabbatar da wannan dogon karatu shi ne, duk uzurin da wani zai iya kawowa, don ya ceci wuyan Ali Raliyallahu Anhu a kan abubuwan da ake qorafi a kansa, to akwai dubunsu da qari, da ake iya kawowa don a daxa gyara wuyan rigar Usman Raliyallahu Anhu a kan shigen waxannan abubuwa.

A taqaicen taqaitawa ma ka ga, Ali Raliyallahu Anhu ya yaqi musulmi tantagarya saboda kujerar halifanci, har aka salwantar da rayukan jama’a da dama. Kuma tsawon halifancinsa bai yi yaqi da kafirai balle yaci garuruwansu, xaukar musulunci ta faxaxa ba. Babu wani ci gaba da musulmi suka samu a lokacinsa. Kuma ya ba waxanda ya ga dama daga cikin makusan tansa muqamai, kamar yadda Usman Raliyallahu Anhu yayi. Illah dai hikimar Usman sun fi nasa xa’a da misantar sharri.

Ita kuwa dukiyar da ake zargin Usmanu Raliyallahu Anhu wai da Almubazzarantarwa, halifan yana da hujja a kan haka (tawili) kamar yadda wai Ali Raliyallahu Anhu keda tashi hujja (Tawuli) a kan zubar da jinin musulmi. Ka kuwa san jinainai sufi dukiya haxari ko?!

Sannan abu na biyu kuma shi ne, wannan nassi kuke ta gogogo dashi, a matsayi hujjar Ali Raliyallahu Anhu a kan wannan abu da ya yi, ku kanku kun kasa haxa kanku a kansa, idan wasunku suka yi gabas sai wasu suyi yamma. Wannan kuwa shi ke tabbatar da cewa gaba xayanku baku da wata taqammar hujja. Tunda ‘yan kame - kame ne da kurin qarya kowannen ku keyi. Kuma jumhurun malamai sun tabbatar da haka.

Wannan kenan. sannan abu na ukku kuma, da za’a kalli abin da halifa Usmanu yayi a bawa banu Umayyatu muqamai, da idon taura, to za’a fahimci cewa wani abune kamar sunna. Kamar yadda shi halifan kan kafa hujja a duk lokacin da aka qalubalance shi, da cewa: ai bani na fara ba: ko Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama yayi aiki dasu a lokacin da yake raye. Kuma halifa, Abubakar Raliyallahu Anhu ma yayi aiki dasu. ba kuwa don suna danginsa ba, balle a tuhumce shi. Kai har Umar ma bai ki suba.

Hasali ma iya saninmu ba musan wata qabila da Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama ya yawaita aiki tare da ‘ya’yanta, daga cikin qabilun Larabawa, kamar banu Abdush-shams. Ko banza qabilace mai tsananin yawa da gabaci. Wanda hakan tasa Annabi Sallallahu Alaihi Wasallama ya naxa Uttabu xan Asyad dan Abi Aisu xan Umayyata gwamnan qasa mafi daraja, wato Makka. Da fatar hakan ta taimaka ga bunqasa musulunci. Ya kuma kai Abu sufyanu xan Harbu xan Umayyata a Najiranu. Khaddu xan sa’id xan Asi ya kai shi Wan’a’al-yaman bayan yasa shi karvar zakka daga banu mazhajin. Yana yamen din ne a matsayinsa na gwamna Allah ya karvi ran manzo Sallallahu Alaihi Wasallama. Haka kuma manzon ya kai sa’id xan Asin taima’a da Haibara da sauran Alkaryun Uraibah, don ya rike su. Ya kuma sa Abban dan sa’idun kula da balahyoyi.daga nan kuma ya yi masa canjin aiki zuwa Bahrain, bayannan xauke Ala’u dan Hadhrami daga can. A can ne Abbanun ya ci gabada aiki har qarshe rayuwar Annabi Sallallahu Alaihi Wasallama haka kuma manzon ya yi aiki da walidu dan ukubata. Wanda a kansa ne ma Allah Ta’ala ya saukar da: idan fasiqi ya zo muku da wani babban labari, to, ku nemi bayani, domin kada ku cuci wadansu mutane a cikin jahilci (49:6).

Ka ga a haka halifa Usman nada cikakar hujja ta cewa: ai na raya sunnar Annabi ne. Don na yi aiki da waxanda ya yi aiki dasu.

Kuma irin wannan aiki da Usman Raliyallahu Anhu ya yine Abubakar da Umar Raliyallahu Anhuma suka yi kafinsa. Don Abubakar Raliyallahu Anhu ya yiaiki da Yazid xan Abu Sufyanu xan Harbu a yaqin da aka ci sham, a matsayi shugaba. Kuma da Umar Raliyallahu Anhu yazo bai canza masa wurin aiki ba. Bayansa ne kuma Umar xin Raliyallahu Anhu ya maye gurbinsa da xan’uwansa Mu’aiwiyya.

Wannan magana da muke gaya maka ta aikin da Annabi Sallallahu Alaihi Wasallama yayi da waxannan mutane tabbatattace. Matsayinta ma a wurin marubutan ilimi ya kai na mutawatura. Wani sashe nata ma har malaman hadisi sun karvetada hannu biyu - biyu a wannan matsayi. A yayin da sashenta ma daga bakinsu ne malamai suka jita. Kuma a jumlance ma dai babu wani daga cikinsu dake musun kasancewarta gaskiya.


Yüklə 2,75 Mb.

Dostları ilə paylaş:
1   ...   20   21   22   23   24   25   26   27   ...   51




Verilənlər bazası müəlliflik hüququ ilə müdafiə olunur ©muhaz.org 2024
rəhbərliyinə müraciət

gir | qeydiyyatdan keç
    Ana səhifə


yükləyin