Rayuwar annabi



Yüklə 0,65 Mb.
səhifə11/12
tarix24.10.2017
ölçüsü0,65 Mb.
#12101
1   ...   4   5   6   7   8   9   10   11   12

Kammalawa


Wannan aiki da ya gabata ya qunshi xan taqaitaccen tarihi ne a kan Rayuwar Masoyinmu kuma Annabinmu Sallahu Alaihi Wasallam, a cikin watan Azumin Ramalana. Mun ga irin yadda Ma’aiki yake gaxa da farin cikin kamawar wannan wata mai alfarma da girman daraja. Yake kuma shirya wa ibadar da ke cikinsa matuqar shiryawa. Hidimar Azumi da nauye-nauyensa ba su hana Annabi Sallahu Alaihi Wasallam kula da haqqoqan da ke bisa kansa na matansa, ta fukkar kyautatawa da karantarwa da shiryar da su ba. Tare da haka kuma bai kasa kulawa da al’ummarsa ba, wato Sahabbai. Tsaye yake Sallahu Alaihi Wasallam su ma, a kan karantar da su ta hanyar aza wa qananansu a fagen ma’arifa xan ba, tare da ci gaba da tattashiya da matsakaitansu. Shi ke yi masu sulhu ya kuma shige masu gaba a wasu buqatun, duk ba tare da wani aiki ya hana shi kula da wani ba Sallahu Alaihi Wasallam.

Irin wannan qwazo kuwa na Ma’aiki baiwa ce daga Allah wadda ya yi gare shi, don ya zama abin koyi ga al’ummarsa, ta hanyar share masu hanya tare da kafa masu hujja; Malaman su da farare hula.

A fahimtata, wannan aiki ya zo a kan kari, domin kuwa babu wani alheri ga musulmi irin ya gudanar da rayuwarsa kamar yadda Manzon ya koyar sallahu alaihi wasallam. Wannan ita ce hanya madaidaiciya kuma ‘yar kurxe, wadda ke kai mutum zuwa ga samun yardar Allah Mahalici, da karva kiransa kamar yadda yake cewa, a wata aya: “Ka ce: “Idan kun kasance kuna son Allah, to ku bi ni sai Allah ya so ku, ya kuma gafarta maku zunubanku, kuma Allah mai gafar ne mai jinqayi.” (2:31).

Ko shakka babu, idan muka yi aiki da abin da wannan aya ta qunsa, addinimu zai kyautata. Kuma tabbas ina da yaqinin cewa alu’ummarmu na da matuqar sha’awar biyar koyarwar Annabi Sallahu Alaihi Wasallam, sai dai waxansu abubuwa ne ke yi masu shamaki, su hana su more wa alherin da ke cikin wannan wata mai alfarma. waxannan abubuwa sun haxa da.




  1. Rashin masaniya da yadda Ma’aiki ke gudanar da rayuwasa a cikin watan Azumi.

  2. Rashin mayar da hankali ga tabbatar da hikimomin da ke cikin ibadun da anka shar’anta yi a cikin watan.

  3. Imani da wasu mutane da yawa ke da shi, na cewa ibadar Azumi ta qunshi nisantar wasu abubuwa ne kawai. Sun manta da cewa akwai wasu ibadodi da anka gindaya na neman kusanci don qara tabbatar da manufar Azumi da samun lada mai yawa.

  4. Wasu mutane kuma sun manta da cewa qananan zunubbai da laifukka, duk da yake ba su vata Azumi gaba xaya, suna rage masa kwarjini. Kai wani lokaci ma idan suka biyu ya sha yanwa da qishiruwar banza kawai.

  5. Wasu kuma sai su mayar da hanakili ga abubuwan da ba su taimkawa da komai ga tabbatar da alfarman Azumi kamar yawaita kwasar gara (abinci) da sauran abubuwan jin daxi, da doguwar hira da dare da baccin rana da yawace-yawacen banza da zama da ‘yan zaman kashe wando, da mayar da hankali kacokan a kan al’amurran duniya, a manta da Lahira.

Ka ji waxannan abubuwa. Sai dai kuma ba takalmin kaza ba ne su, ana iya magance su ta hanyoyi kamar haka.


  1. Lalle ne, Malamai magada Annabawa su tsare aikansu na wa’azi da gargaxi tare da aikata abubuwan da suke faxa, don mutane su kwaikwaya. Kada su yarda a same su suna aikata abubuwan ashsha. Wannan manufa na iya tabbata ta hanyar amfani da kayayyakin sadarwa na zamani.

  2. Lalle ne kuma kowane musulmi ya yi iyi qoqarin ganin dalilin da ya sa Allah ya halincce shi ya yi amfani. Haka za ta taimaka masa ga qara qaimi a kan ayyukan qwarai da nisantar na ashsha, ta hanyar awo da gwaji da sanin ciwon kai. Irin wannan fahimta ce ke sa mutum ya xaure akuyar zuciyarsa gindin magarya. Ya yi amfani da lokacinsa yadda ya kamata ta hanyar qin yarda da wadatuwa da abubuwa na mustahabbi, ga farillai da wajibbai na kallon sa. Ta haka sai ka same shi kabbarar farko ta kowace Sallah da asuba bat a wuce shi, don ya riga ya koya kuma sabo tun a cinkin watan Ramalana.

  3. Haka kuma wajibi ne mutane su haxa qarfi da qarfe a kan ganin sun cusa wa al’umma ruhin koyi da Annabi Sallahu Alaihi Wasallam sau da qafa, a cikin kafatanin sasannin rayuwarsu, da kuma musamman a cikin watan Azumin Ramalana. Wannan kuwa karatu, da yi wa ladubba da hukunce-hukuncen Azumi nazarin qwaqwaf, da yaxa su a cikin al’umma ta yadda kowa zai fahimce su, ya kuma ci moriyar alheri da nagarta, za su yawita aikin jama’a, sharri da fitsara kuma su yi bankwana.

Bayan wannan kuma lalle ne a yi qoqarin gwargwadon hali, a ga tsare-tsaren mu na gudanarwa a makarantun zamani da kafafafen watsa labarai, Ta fuskar yawa da nagarta ta yadda za su dace da qalubalen zamani. Ta haka gurbin da ke akwai a zukatanmu, tattare da zamansa wagege zai cike, ko muna dawowa cikin hayyacinmu.

A qarshen ina roqon Allah Ta’ala ya yi mana jagora, ya haskaka zukanmu, ya xora mu a kan tafarki madaidaci. Ina roqon ka ya Allah ka saka wa duk wanda ya taimaka da wani abu a cikin tabbata da yaxuwar wannan littafi ta kowace hanya, kamar qarawa abubuwan da ya qunsa armashi, da gyara wa kalmomi da jumlolinsa zama, ko qoqarin ganin ya cika duniyar musulmi. Allah ka sa mu ci moriyar rayuwarmu a cikin muhimman lokutan ibada, waxanda ka arzutta mu da su, da ma wasunsu. Allah ka karva ibadodinmu a cikin wannan lokaci. Ka shiryar mana da ‘yan’yanmu, da iyalinmu. Ka sanya albarka a cikin dukiyoyinmu. Kai mai iko ne a kan haka, ya Allah. Wa Sallallahu Ala Nabiyyina Al-amin Wa Ala Alihi Wa Sahbihi Ajma’ina.


1Muslimu, 1718

2 Buhari, 7280

3 Tafsirn Alqur’ani Mai Girma na Ibnu kasir: 7/521

4 Buhari, 14. Muslimu, 92

1 Jami’ul - Ulumi wal - Hikam, 1/389

2 Fathul - Bari na Ibnu Hajar, 1/59

1 Jami’ul - Bayan na Dabari, 6/568

2 Taisirul - Karimir Rahman na Sa’adi, 367.

1 Amma wasu Malamai sun ce, yakan yawaita Azumin ne a cikin wannan wata na Sha’abana a matsayin

ranko na Azumin kwanaki uku a kowane wata da ba yakan sami damar yi ba Sallallahu Alaihi



Wasallama. Wasu kuma suka ce yana taya matansa ne, saboda a lokacin ne suke rankon Azumin

Ramalana. Amma dai mafi ingancin zance shi ne cewar da Ibnu Hajar ya yi a cikin Al-fathu, (4 /253)

cewa: “Mafificiyar magana ita ce abin da aka riwaito daga Usamatu xan Zaidu, wanda ya ce: Na ce: Ya

Manzon Allah ban ga watan da kake yawaita Azumi cikinsa ba kamar yadda kake yi a cikin Sha’abana

ba? Sai ya karva mani da cewa: “Wannan wata ne da mutane ba su cika kula da shi ba, wato saboda

kasancewarsa tsakanin Rajab da Ramalana. Ga shi kuma wata ne da ake kai wa Ubangijin bayi rahoton

ayyukansu na shekara. To ina kwaxayin nawa ayyukkan su isa ina xauke da Azumi.” Nisa’i ne ya fitar

da Hadisin (2357) kuma kyakkyawa ne. Amma kuma bai kore magangannun sauran Malamai ba. Allah

Shi ne mafi sani.


2 Buhari, 1969

3 Muslimu, 1156

4 Majmu’ul Fatawa na Ibnu Usaimin, 20/22-23


1 Buhari, 1899

2 Tirmizi, 682. Hadisi ne ingantacce

3 Nisa’i, 2106. Hadisi ne ingantacce

4 Buhari, 1797


1 Abu Dawuda, 2342. Hadisi ne ingantace.

2 Abu Dawuda, 2340. Sammaku ne ya riwato shi daga Ikramata, kuma akwai gargada a cikinsa. Amma

Hadisin can na xan Umar ya kashe kaifinta.



1 Nisa’i, 2116. Hadisi ne ingantace.

2 Buhari, 1808

3 Nisa’i, 2130. Hadisi ne ingantacce.

4 Muslim, 1082

5 Malamai da dama sun tafi a kan cewa yin Azumin “Ko-aka yi” haramun ne. Wasu kuwa suka ce a’a

makaruhi dai. A yayin da sashen Malaman Mazhabar Hambaliyya suka ce yin sa ma wajibi ne, sauransu

kuma suka ce, a’a idan dai mutum ya yi ba laifi. Wannan ra’ayi na cewa babu laifi, shi ne Abu Hanifa

yake a kai. Kuma Imamu Ahmad ya faxi haka kai tsaye. Sannan hakan shi ne abin da da jawa, ko mafi

yawan Sahabbai da Tabi’ai suka tafi a kai, kamar yadda Ibnu Taimiyya ya faxa. Duba Majmu’ul

fatawa, 25/ 98-100



1 Tirmizi, 686. Hadisi ne ingantacce.

2 Majmu’ul- Fatawa na Ibnu Taimiyya, 25/101.

3 Majmu’ul- fatawa na Ibnu Usaimin, 19 /36-37.

4 Tirmizi 697

5 Malamai sun kasu kashi uku a kan wannan mas’ala. Kashi na farko suka ce, yau da mutum xaya zai ga

watan Azumi ko na Sallah da qwayar idonsa, amma kuma a qi yarda da shi, to, sai ya kama Azumin ya

kuma aje a asirce. Kashi na biyu kuma suka ce, a’a, kama Azumin kawai zai yi shi kaxai, amma ya jira

mutane su aje tare. Kashi na qarshe kuma suka ce, ko alama. Kada ya xauka balle ya aje, sai tare da sauran jama’a. Wannan magana ta qarshe ita ce mafificiya, saboda wancan Hadisi da ya gabata. Allah shi ne mafi sani. Duba Majmu’ul Fatawa na Ibnu Taimiyyah (25/214-218).



1 An gina wannan hukunci ne a kan mafificin zancen nan da ke cewa mahudar jinjirin wata na savawa gwargwadon savawar garuwa. A kan haka, sai dai kowane gari ya nemi watansa keve. Idan ya bayyana gare su, to, xaukar Azumi ta wajaba a kansu, da maqwabtansu, su kuwa sauran garuruwa su jira bayyanar nasu. Dalili kuwa shi ne cewar da Allah Ta’ala ya yi “Watan Ramalana ne wanda aka saukar da Alqur’ani a cikinsa, yana mai shiryarwa ga mutane da hujjoji bayyanannu na shiriya da rarrabewa. To, wanda ya kasance halarce daga cikinku a watan, sai ya azumce shi” (2:185). Kuma Annabi Sallallahu Alaihi Wasallama cewa ya yi: “Kada ku xauki Azumi ko aje shi sai an ga jinjirin watan Ramalana da na Shawwal.” Ka ga kenan a shar’ance sai an ga wata ake kama Azumi. Kuma Malamai sun yi ittifaqi a kan cewa, mahudar watan ba xaya ba ce. Kalmar “gari” kuwa da muka yi amfani da ita a matsayin kalmar Iqlim ta Larabci, na nufin yankin da wata ke bayyana gare su a lokaci xaya, ba yankin da ke qarqashin tutar siyasa xaya ba. Duk da yake watan kan bayyana ga wasunsu lokaci xaya. Duk da yake kuma wata magana mai qarfi ta ce: a duk lokacin da wani yanki ya ga wata sumul, to, wajibi ne ga sauran musulmin duniya su kama Azumi. Duba: Majmu’ul-Fatawa na xan Usaimin, 19/44-47.


1 Buhari, 4837.

2 abu Dawuda, 904. Hadisi ne ingantacce

3 Ibnu Hibban, 620. Isnadinsa kuma a kan sharaxin Muslim yake.

1 Tirmizi, 696, Hadisi ne ingantacce. Amma idan mai Azumi bai sami xaya daga cikin waxannan abubuwa ba, to ya samu ya buxa baki da abin da ya sauwaqa na halas. Idan ma ya kasa samun komai,

sai ya buxa bakin da niyya kawai. Allah shi ne mafi sani.



2 Muslimu, 1099.


1 Buhari, 1941/ Muslimu, 1101. Lafazin na Muslimu ne.

2 Nisa’i, 2162, Hadisi ne ingantacce.

3 Buhari,1921.

4 Abu Dawuda, 2345. Hadisi ne ingantacce

5 Nisa’i, 2167, Hadisi ne ingantacce.

6 Xan Hibbanu, 3504. Isnadinsa a kan sharaxin Bukhari da Muslim ya ke.

7 Xan Hibbanu, 3476. Hadisi ne mai kyau.

8 Musannaf Abdir Razzaq, 7591.

1 Tirmizi, 725. Ya kuma ce: “Abin da Malamai suka ce a kan wannan mas’ala shi ne, babu laifi don mai Azumi ya yi aswaki, kuma ba da xanyen icce ba, kada kuma ya yi shi da marece” Mal. Ibnul qayyim ya ce a cikin Zadul Ma’adi, (2/ 61): “Ya inganta cewa Annabi Sallallahu Alaihi Wasallama kan yi aswaki yana kuma Azumi”. Malamai da yawa ne suka riwaito Hadisin. Kuma a cikin silalin isnadinsa akwai Asimu xan Ubaidullahi, wanda Malamai da dama ke da xan qaiqayi a kan riwayarsa. Buhari ya ce: “Hadisinsa ba ya da kyau”. Ibnu Adiyyin ya ce “Duk da rauninsa nakan rubuta Hadisinsa” Malam Ijli kuma ya ce: “Al’amarinsa ba laifi; da dama.” Duba: Tahzibut – Tahzib, (5/46).

1 Musand Ahmad, 7- Hadisi ne ingantacce saboda wanninsa.

2 Musnad Ahmad, 22/3. Hadisi ne ingantacce saboda waninsa.

3 Ahmad, 9930. Isnadinsa kuma a kan sharaxin Buhari da Musulimu ya ke.

4  Muslim, 252

5 At- Tamhid na Ibnu Abdilbarri, (7/198)

6 Buhari tare da Fathul Bari (4/187).

7 Dan Huzaimatu, 3/247

8 Buhari, 1805. Saboda wannan Hadisi ne wasu Malamai suka qyamaci yin asawaki ga mai Azumi da

marece, don kada ya gusar da xoyin da bakinsa ke yi a lokacin, sakamakon daxewa bai ci bai sha ba.

Wasu kuma suka ce babu laifi ya yi koyaushe. Wasu kuma suka ce an so ya yi kafin Sallar azahar

kawai. Idan har La’asar ta yi, yin sa makaruhi ne in ji wasu. Wasu kuwa suka taqaita wannan qangi ga

Azumin farilla, ban da na nafila, saboda yana da wuya a yi riya a cikinsa. Amma dai ingantattar Magana

ita ce, abin da waxancan Hadisai suka tabbatar. Allah shi ne mafi sani. Duba: At Tamhid na Ibnu Abdilbarri, (19/57), da Umdatul-Qari na Malam Badruddini, (16/ 384).



2 At-Tamhid na Ibnu Abdilbarri, (7/199).

3 Buhari, 1927

4 Buhari, 1829/ Muslimu, 1109. Kuma lafazin nasa ne.

5 Abu Dawuda, 2365, Hadisi ne ingantacce.


1 Buhari, 2/680-681.

2 Majmu’ul- Fatawa na Ibnu Taimiyya: (25/281-282).

3 Abu Dawuda 142. Hadisi ne imgantacce. Kuma Ibnul qayyim ya faxa a cikin: Zadul- ma’adi, (2/16): “Annabi kan kurkure baki ya kuma shaqa ruwa alhali yana Azumi. Amma kuma ya, hana mai Azumi kai

matuqa a cikin shaqa ruwa”.



4 Zadul- Ma’adi na Ibnul qayyim, (2 /32).

1 Buhari, 1961

2 Buhari, 1965

3 Buhari, 1862.

4 Buhari, 1856. Duba: Majmu’ul Fatawa na Ibnu Usaimin (20/59-60).

5 Duba: Zadul- Ma’ad na Ibnul qayyim (2/32-34 ).

1 Duba: Fathul- Bari na Ibnu Hajar, (6/229).

2 Buhari, 4279

3 Muslimu, 1122

4 Ahmad, 5866. Hadisi ne ingantacce

5 Buhari, 4275

1 Buhari, 2733

2 Muslim, 1114-Duba: Majmu’ul- Fatawa na Ibnu Usaimin (19/135), don qarin bayani.

3 Abu Dawuda, 2408. Hadisi ne ingantacce

4 Muslim,1120

5 Zadul- ma’ad: (2/55-56).

6 Duba: Nailul Auxari na shaukani: (4/304), da Tuhfatul Ahwazi na Mubarakfuri, (3/325).

7 Nisa’i, 2116. Hadisi ne ingantacce, kuma yana halastar da karvar shedar mutum biyu a kan tsayuwar wata da faxuwarsa. Ya zo a cikin: al-Musnad, 18915, cewa: Idan mutum biyu musulmi suka bayar da sheda a kan wata, to ku xauki Azumi, ku kuma aje.” Wannan shi ne hukunci na asali. Amma saboda kasancewar Annabi Sallahu Alaihi Wasallam ya karvi shedar Ibnu Umar Raliyallahu Anhu a kan ganin wata, ya kuma hori mutane da xaukar Azumi a kan haka. Sannan kuma ma ya karvi ta wani Balaraben qauye, ba tare da ya buqaci su kai su biyu ba. Sai Malamai suka ce ana karvar shedar mutum xaya don tabbatar da tsayuwar watan na Azumi. Amma abin da ya shafi qarewarsa, sai an sami shedar mutum bityu. Allah shi ne mafi sani.

1 Buhari,6502

2 Buhari, 6057

1 Buhari, 1147

2 Buhari, 1164

3 Buhari, 990

4 Duba: Ma’ar-rasul Fi Ramalan na Axiyya Muhammad Salim

5 Ahmad, 24268

6 Buhari, 1902

1 Muslim,1104

2 Buhari, 1129. muslim, 761 Lafazin na Muslimu ne

3 Tirmizi, 806 Hadisi ne ingantacce

1 Buhari, 1906. Mustadrak na Hakim, 1608.

2 Fala’ilul- Qur’an na Ibnu abid- Dunya, 30

3 Nasa’i, 364. Hadisi ne ingantacce.

1 Buhari, 2013

2 Nisa’i 1616. Hadisi ne ingantacce

3 Muwaxxa Maliku, 250

4 Sunanul kubura na Baihaqi, 2/496

1


2 Buhari, 2041

3 Musulimu, 1167

4 Buhari, 2026

5 Don Majah, 1775. Hadisi ne ingantacce

1 Muslimu, 1171

2 Zudul- Mi;ad na xan Kayyin, 2/90

3 Buhari, 1914

4 Muslimu, 1173

1 Buhari, 1936

2 Majmu’ul- Fatawa na xan Usaimin, 20/172

3 Mujmu’uyl- Fatawa na xan ussaimijn, 20/184

4 Buhari, 296

5 Fathul- Bari na xan Hajar, 4/320

6 Abu Dawuda, 2473

1 Buhari, 1897

2 Ahmad, 6495 Hadisi ne ingantacce a dalilin waninsa

3 Buhari, 2029

4 buhaari, 3281

1 Buhari,1890

2 Buahari, 1900/Muslim, 2700. Lafazin kuma nasa ne

3 Umdatul- qar na al-Aini, 11/148

4 Tirmizi, 803. Hadisi ne ingantacce

5 Dan Hibban, 3663, isnadinsa a kan sharaxin musulim ya ke,

1 Fathul Bari na xan Hajaru, 4/334

1 Malam xan Usaimin na cewa a cikin Majmu’ul fatwa, 20/ 150:” karvaven Li’itikaf a wurin Allah shi ne

wanda mai shi ya al’amurran duniyya a cikinsa, wato saye da sayarwa.



2 Haramun ne a mazhabar Hambaliyya qulla ciniki a cikin masallaci, blle ya tabbata Amma jumhuru sun

ne idan an riga an qulla, ya ingamta , sai dai an yi karahiyya. Duba; Fathul- li’tikaf na Dr Halidu al

-mushaiqihu, 176


3 Majmu;ul- fatwa na xan usaimin 20/180

4 Buhari, 6502

5 Majmu’ul Ramalana na xan Usaimin 20/159

6 Durusu Ramalana , na Hammadi, 172

1 Maj’mu’ul – fatawa na xan Usaimi 20/159

2 Abu Dawuda, 1374 Hadisi ne ingantace

3 Musulim, 1175

4 Muslim, 1174

5 Al-musnad, 6/146

1 Muslim,1167

2 qiyamu Ramalana, na al Maruzi, 92

3 Abu Dawuda, 1377. Hadisi ne ingan tacce

4 Sunanul- kubra na Bailaqi, 2/494

5 Abdurrazzaq, 25/5

1 Buhari, 1902

2 Buhari,3624

3 Fathul- Bari, 1/42

4 Amma kuma idan mutum ya fi gane wa yin karatun da rana to an fi son ya yi a lokacin Allah shi ne

mafi sani



5 Fathul Bari, na xan Hajaru, 9/45

1 Sharhul- Buhari na xan Baxalu, 1/13

2 Al- Tamhid, na Ibnu Abdilarri, 6/111

3 Laxa’iful- Ma'arifi, na xan Rajabu, 183

4 Duba Littafi na sama. Acikinsa akwai inda yake cewa, wasu Malamai sun kawo hujjar

da ta hana mayar sa sauka a cikin qasa da kwana uku abin ya, amma idan an yi haka

ne don a ci ribar wani lokaci mai alfarma, ko wari, to babu laifi Dalilinsa Shi ne, takin

qasar Hadisin na Abdullahi xan Amru na nuna haka, 183



5 Abu Dwawuda, 1392/ Dan nabbanu, 758. Nadisi igan tacce.

1 Abdurrazaak, 6010

2 Al- itqan na Sauxi 2/ 468. Hadisin kuma Ahmad ne ya riwato shi, 5/130

3 Shu'abul Imani na Bai haqi 1807

4 Jami'u Ahkamil- qur'an na qurxabi, 1/53

5 Ihya'u Uhuddini na Gazzali /275

1 Majmu'ul Fatawa na xan Usaimin 20/ 78

2 Abu Dawuda, 1374, Hadisi ne mai kyau

3 Dan maja, 1775. Hadisi ne ingantacce

4 Ahmad, 5349. Hadisi ne ingantacce

1 Buhari, 2018

2 Tirmizi, 696. Hadisi ne ingantacce.

3 Nisa,I 2167 Hadisi ne ingantacce

4 Abu dawuda, 1379 Hadisi ne mai kyau.


Yüklə 0,65 Mb.

Dostları ilə paylaş:
1   ...   4   5   6   7   8   9   10   11   12




Verilənlər bazası müəlliflik hüququ ilə müdafiə olunur ©muhaz.org 2024
rəhbərliyinə müraciət

gir | qeydiyyatdan keç
    Ana səhifə


yükləyin