Tafarkin sunnah


Malaman Sunnah ba su Ta’assubanci



Yüklə 2,75 Mb.
səhifə12/51
tarix28.10.2017
ölçüsü2,75 Mb.
#17506
1   ...   8   9   10   11   12   13   14   15   ...   51

2.9.1 Malaman Sunnah ba su Ta’assubanci

Xan Shi’ar ya ce: Su dai ‘yan-sha-biyu ba su da ra’ayin riqau ga abin da ba gaskiya ba. Savanin Ahlus-Sunnah. Misali a nan shi ne Imamul Ghazali da Mawardi daga cikin malaman Shafi’iyyah sun tafi a kan cewa, daidaita qaburbura shi ya yi daidai da shari’ah. Amma saboda ‘yan-sha-biyu sun mayar da shi al’ada mun bar shi. Za mu rinqa xaga qaburburanmu zuwa sama. Kuma wai, Zamakhshari daga cikin malaman Hanafiyyah ya fassara faxar Allah Ta’ala da ya ce: (Allah) Shi ne wanda yake yin salati akan ku da Mala’ikunsa Ahzab :43. Zamakhsharin ya ce: Ya halalta bisa ga wannan aya ayi salati ga xaixaikun musulmi. Amma saboda ‘yan-sha-biyu suna yi wa imamansu salati sai muka hana.

Xan Shi’ar ya ci gaba da cewa: Mai littafin Al-Hidaya daga cikin Hanafiyyawa ya ce, sanya zobe a hannun dama shi ne Sunnah. Amma tunda ‘yan-sha-biyu na yin sa to, mun mayar da shi hagu. Ire-iren wannan na da yawa, inji shi. Ya kuma ci gaba da cewa: “Duba wanda ke canza shari’ah, ya musaya hukuncin da Annabi ya sanya don kawai yana adawa da wasu mutane. To, ina dalilin bin wannan da xaukar maganarsa?”
Martani:

Duk waxannan maganganu da xan Shi’ar ya yi sun fi dacewa da a mayar masa da su. Domin Allah ya tsarkake malaman Sunnah daga irin wannan.

A haqiqanin gaskiya, bamu tava sanin wata qungiya mai ra’ayin riqau ga qarya kamar ‘yan-sha-biyu ba. Su ne waxanda aka san suna shedar zur idan shari’ah za ta hau kan xan Shi’ah irin su. Wane ta’assubanci ma ya wuce qarya? Su ne fa suka ce, wai, ‘ya macce na gadon duk dukiyar ubanta, don su kori Abbas daga magadan Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama, su bar Fatima ita kaxai! Kuma a cikinsu akwai masu haramta cin naman raqumi, wai, don Nana A’ishah ta hau kansa a ranar yaqin basasa. Suka sava ma Alqur’ani da Sunnah da ijma’in Ahlul-Baiti da malaman Sunnah don bin son ransu. Abin da kowa ya sani ne cewa, koda wancan raqumin da Nana A’ishah ta hau yake a raye ba za a haramta hawansa a Shari’ah ba. Domin kuwa ko kafirai da suka hau dabbobi ba a haramta hawansu ba, balle cin namansu.

Kai, ta’assubancin ‘yan Shi’ah ya kai ga suna qyamar lamba 10 don kauce ma mutane goma da Allah ya yi wa bushara da aljanna. Sai ka ji sun ce, tara da xaya. Suna qoqarin kada su yi komai ya dace da goma saboda haka.

Don tsananin ta’assubancinsu ma, in suka ga mai suna Ali ko Ja’afar ko Hasan da Husaini sai suna zanzari wajen girmama shi koda fasiqi ne. Dubi kuma yadda suka kafa ma Banu Umayyata qahon zuqa don wasu daga cikinsu sun kasance suna qyamar Ali. Alhali kuwa akwai mutanen kirki da dama daga cikin Banu Umayyata waxanda sun mutu tun kafin faruwar fitinar da ta gudana. Hasali ma babu wata qabila da Annabi Sallallahu Alaihi Wasallama ya yawaita sanyawa cikin aikin gwamnati kamar su. Kamar yadda ya shugabantar da Attabu xan Usaidu akan Makkah. Ya kuma shugabantar da Khalidu xan Sa’idu da ‘yan’uwansa Abanu da Sa’idu a wasu wurare daban. Haka kuma ya shugabantar da Abu Sufyan xan Harbu xan Umayyata ko xansa Yazidu akan Najran. Har Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama ya cika kuwa yana gwamna a wurin. Sannan Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama ya aurar da ‘ya’yansa mata uku ga dangin na Umayyata. Domin babbar ‘yarsa Zainab ya aurar da ita ne ga Abul Asi xan Rabi’u, wanda Annabi ya yabe shi a lokacin da Ali ya so ya auri xiyar Abu Jahali. Annabi Sallallahu Alaihi Wasallama ya nuna jin daxinsa da surukutar Abul Asi, kuma ya qara da cewa: “Ya faxa mani magana ya yi gaskiya, ya kuma yi mani alqawari ya cika”. Sannan ya aurar da Ruqayyatu da Ummu Kulsumi ga sayyidina Usman. Duk waxannan ‘yan gidan Umayyata ne.

Yana daga cikin jahilcin ‘yan Shi’ah, qyamar da suke ma mutanen Sham gaba xaya, domin can farko an samu waxanda ba su son Ali Raliyallahu Anhu. To, ai ko Makkah an yi lokacin da kafirai ke a cikinta; waxanda ba su son Manzo. A Madina ma kuma an yi munafukai. Amma a halin da ake ciki yau, babu mai qyamar Ali ko xaya a Sham. To, don me suka tsane su?

Haka ma suna jin haushin duk wanda ya yi amfani da wani abu da ya rage na Banu Umayyata kamar shan ruwan rijiyar Yazid. Alhalin Yazidu bai ma gina rijiyar ba, ya dai yalwata ta ne kawai, sai aka kira ta da sunansa. Basu kuma son a yi sallah a masallacin Banu Umayyata. In don Banu Umayyata sun gina shi ne kuwa, ai Ka’aba mushrikai suka gina ta, amma Annabi Sallallahu Alaihi Wasallama ya yi sallah a cikin ta. Kuma Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama bai tava qin shiga gidajen da suka gina, ko ya qi shan ruwan rijiyar da suka haqa, ko sa tufan da suka saqa ko kashe kuxin da suka buga ba. To, wannan kafirai kenan fa; ina ga musulmi?!.

Wani amintacce ya bani labarin wanda yake da kare a cikinsu, sai aka kira karen nasa Bukairu, sai nan take ya fusata, wai an sa ma karensa sunan ‘yan wuta. Wal iyazu billahi. A dalilin haka suka yi ta faxa har abin ya kai aka zubar da jini. Wa ya fi mai yin wannan ta’assubanci da wauta?.

Su dai malaman Sunnah daxai ba su ce abar wani abu da shari’ah ta yarda da shi don wani xan bidi’ah ya aikata shi ba. Ka ga maganar daidaita qabari da ya yi. Mazhabar Abu Hanifa da Ahmad ita ce xaga shi ya fi. Hujjarsu kuwa ita ce, haka aka yi wa Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama. Kuma suka ce, hakan ya fi nisantar da shi daga kama da gine-ginen duniya, kuma yana taimakawa wajen hana a zauna a kansa. Amma Imamus-Shafi’i sai ya so a shafe shi; ya ce mustahabbi ne. Domin akwai dalilai da suka nuna haka. Wasu daga cikin almajiransa suka ce, ai yin haka xabi’ar ‘yan Shi’ah ce, don haka suka karhanta. Amma akasarin almajiransa suka ce ba haka ba ne; mustahabbi dai ne ko ‘yan Shi’ah na yinsa.

Haka shi ma bayyana karatun bismillah shi ne mazhabar ‘yan-sha-biyu. Kuma a kan wannan ne da maganar qunutin asuba wasu suka yi magana akan Imamus-Shafi’i, saboda abin ya shahara a Iraqi garin ‘yan Shi’ah. Amma duk da haka, shi Imamus-Shafi’i bai daina ba tunda yana ganin shi ne Sunnah. To, ka ga ba wani malamin da ya tava barin Sunnah saboda wai wasu ‘yan bidi’ah irinku na yin ta.


2.9.2 Addu’a ga Halifofi Cikin Huxuba

Sannan xan Shi’ar ya ce: Su dai Ahlus-Sunnah sun qago bidi’oi da yawa a cikin addini alhlai suna sane. Kuma Annabi Sallallahu Alaihi Wasallama ya ce: “Kowace bidi’ah vata ce. Kuma kowace vata makomarta wuta”. Ya kuma ce: “Duk wanda ya shigar da wani baqon abu a cikin addininmu to, ya yi ta banza”. Kuma ko an so a hana su waxannan bidi’oi ba su bari. Kamar addu’ar da suke ma halifofi a cikin huxuba, wadda ba ta da asali a cikin addini. Kuma ba a yi ta ba a zamanin Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama da zamanin Sahabbai ko na Tabi’ai. Kai, ko ma zamanin Banu Umayyata da Banul Abbas ba a yinta. Sarki Mansur ne ya qago ta don ya musguna ma Alawiyyah sa’adda ya yi wata hatsaniya da su. Ga shi ko Ahlus-Sunnah na yinta har ila yaumina haza.


Martani:

Yana da kyau a rinqa ba ilimi da tarihi haqqinsu. Shi dai yin addu’a ga halifofi huxu a kan mimbari abu ne da tarihi ya tabbatar da an yi shi tun zamanin Sarkin Musulmi Umaru xan Abdulazizi. Dalilin yin sa kuwa shi ne, don kariyar martabar sayyidina Ali da wasu ‘yan kazagin Banu Umayyata suka fara zagi a cikin huxubobinsau. Saboda adalcinsa sarki Umaru xan Abdulazizi ya ce a musanya wannan da yin addu’a da fatar alheri ga halifofi huxu shiryayyu, cikinsu har da Ali. Ya yi haka ne kuwa a matsayin wani salo na kawar da waccan mugunyar al’adar da ya ji tsoron yaxuwarta.

Kuma tuhumar da ya yi wa sarki Mansur ba ta da makama. Domin ba wata musgunawa ga Alawiyyawa don an yi ma Abubakar da Umar da Usman addu’a an haxa da Ali. Tunda daman sun riga shi yin halifanci kuma ban yi jayayya da su ba. Ba kuma wani Ahlus-Sunnah da ya ce yin wannan addu’a farilla ne a cikin huxuba. Bidi’ah kam sananna ita ce, yi wa Ali shi kaxai addu’a ko ambaton imamai goma sha biyu da ‘yan shi’ah suka naxa. Kamar yadda zagin Ali ko duk wani magabaci a cikin huxuba yake bidi’ah mummuna.

Sanannen abu ne dai cewa, halifofi uku na farko al’umma ta haxu a kan naxinsu. Kuma a zamaninsu kafirai sun xanxana kuxarsu, musulmi sun zauna lafiya. Shi kuma na huxu ya zo bisa qaddarar Allah a lokacin fitina, musulmi basu haxu a kansa ba, ba su kuma zauna lafiya da juna ba. Don haka kafirai sun ci karensu babu babbaka a lokacinsa. To, ka ga faxinsa shi kaxai cikin huxuba a bar waxancan uku babu bidi’ar da ta wuce shi.


2.9.3 Shafar Qafa Wajen Arwalla

Xan Shi’ar ya ce: Ahlus-Sunnah sun canza nassin da Allah ya tabbatar na shafar qafafu a wajen arwalla madadin wanke su, inda Allah ya ce: Sai ku wanke fuskokinku da hannayenku zuwa ga magincirori, kuma ku yi shafa ga kanunku da idanun sau. 5:6. Kuma Ibnu Abbas ya ce: Gava biyu ake wankewa, biyu kuma ake shafawa. Amma suka canza suka wajabta wanke qafafu.


Martani:

Adadin waxanda suka ga Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama yana arwalla, da waxanda suka koya daga wurinsa da waxanda suka yi a zamaninsa har ya gani da idonsa sun fi yawa akan adadin waxanda suka karantar da wannan aya. Domin duk musulmi suna arwalla. Kuma sun gan shi yana yin ta sau shurin masaqi. Kuma gaba xayansu sun gan shi yana wanke qafafu. Har ma sun ce, ya tsoratar da waxanda wankinsu bai yi ba da cewa, wuta zata wanke dugadugansu.

Kuma su matsalar ‘yan Shi’ah ita ce, ba su da cikakkiyar fahimtar Larabci. Don ita wannan aya sam bata sava ma aikin Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama ba; ta yi daidai da shi. Sannan abin al’ajabi shi ne, duk bayan wannan ‘yan Shi’ah su ce ba a shafa a kansafa wadda ta tabbata daga Annabi Sallallahu Alaihi Wasallama a cikinsunnah mutawatira. Wai suna ganin yin haka ya sava ma Alqur’ani, su da Harijawa. Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama kuwa shi ne wanda yake fassara Alqur’ani.
2.9.4 Mutu’ar Hajji da ta Aure

Xan Shi’ar ya ce: Haka kuma Ahlus-Sunnah sun haramta mutu’a biyu da Alqur’ani ya zo da su; Mutu’a hajji da Allah ya ce: To, wanda ya ji daxi da Umra zuwa Hajji, sai ya biya abin da ya sauqaq na hadaya 2:196. Kuma da Annabi Sallallahu Alaihi Wasallama ya rasa samun yin wannan mutu’a ba saboda ya yi qirani sai da ya yi nadama a kan haka. Sai kuma mutu’ar aure da Allah ya ce: Kuma abin da kuka ji daxi da shi daga gare su, to, ku ba sadakinsu bisa farilla 4:24.

Xan Shi’ar ya ce: Kuma waxannan mutu’oi biyu, musulmi sun ci gaba da gudanar da su tsawon zamani rayuwar Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama da halifancin Abubakar da Umar. Haka kawai watarana sai Umar xin ya hau mimbari ya haramta su. Kuma ya ce, duk wanda ya yi su zai to, jikinsa zai gaya masa.
Martani:

Ita dai mutu’ar Hajji da Umrah duk musulmi sun haxu a kan halalcinta. Kuma qarya ne a ce Ahlus-Sunnah sun haramta ta. Da yawan malaman Sunnah na ganin mustahabbi ce. Akwai ma masu rinjayar da ita da masu ganin ta wajibi.

Ita ko mutu’ar aure ba ta a cikin ayar da ya karanta. Ayar dai tana magana ne akan matar da aka xaura ma aure aka kuma ji daxi da ita ta cancanci sadakinta duka. Savanin wadda aka xaura ma aure ba a ji daxi da ita ba wadda ta cancanci kawai rabin sadakinta. Saboda haka ayar ba tana magana kan kowane irin jin daxi da macce ne ba, sai fa jin daxi na halas. Kuma malamai sun haxu a kan bata sadakinta duka idan aure ya tabbata koda vatacce ne. Amma wanda ya ji daxi da ita ta hanyar haram ba wani sadaki da Allah ya ce a ba ta.

Maganar cewa Umar ya haramta mutu’ar aure ba gaskiya ba ce. Annabi Sallallahu Alaihi Wasallama ne ya haramta ta bayan a da mutane na yin ta. Sayyidina Ali ne ma ya bayyana wannan Sunnah ga Ibnu Abbas da bai sani ba. Ya ce masa: Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama ya haramta auren mutu’ah da cin jakin gida a ranar Haibara. Kuma ya tabbata a cikin Sahihu Muslim cewa, Annabi Sallallahu Alaihi Wasallama ya haramta ta a ranar da aka ci Makka haramci na har abada.

Ita kuma cewar da sayyidina Ali ya yi: Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama ya haramta auren mutu’ah da cin naman jakin gida a ranar Haibara. Wasu malamai kamar su Ibnu Uyainata na ganin yana nufin ranar Haibara ranar haramta jakin gidan ce. Amma shi auren mutu’ah a ranar buxa garin Makkah aka haramta ta. Wasu kuma na ganin ranar buxa Makkah haramtawa ta biyu ce. Don haka suke cewa, an haramta ta, sannan aka halalta, sai aka sake haramtawa daga qarshe. Akwai ma har masu cewa, an sake halalta ta kafin ranar Fatahu Makkah, sannan a ranar aka yi mata haramci na qarshe. Amma maganar can ta farko ta su Ibnu Uyainata tafi qarfi cewa, mutune suna yin mutu’ah ba a kuma hana su ba sai ranar buxa Makkah. Daga nan kuma ba wani halalci da ya zo akan ta. Shi kuma Ibnu Abbas da ya yi fatawa akan halaccinta da na cin naman jakin gida bisa ga rashin sani, sai sayyidina Ali ya ankarar da shi ga haramcin da ya tabbata daga Annabi Sallallahu Alaihi Wasallama.

Don haka, Ahlus-Sunnah su ne suka bi Ali da sauran halifofi a cikin abin da suka cirato daga Annabi Sallallahu Alaihi Wasallama. Su kuma ‘yan Shi’ah sun sava ma Ali, sun bi wani ra’ayi na qashin kansu.

Ka ga ai a cikin Alqur’ani mata biyu Allah ya halalta; matar aure, da baiwa. Ita kuma matar mutu’a ba matar aure ba ce, don ba ta gado, ba a sakin ta, balle a ba ta rabin sadaki idan an yi shi kafin baiko. Sannan ba ta idda. Waxannan hukunce-hukuncen kuwa su ne Allah ya tabbatar ma matan aure cikin Alqur’ani. Sannan ita ba baiwa ba ce. Ka ga ta tabbata haramtacciya. Tunda Allah Ta’ala ya ce: Kuma waxanda su masu kariya ne ga al’aurarsu. Sai fa akan matan aurensu ko abin da damansu ta mallaka (na bayi). To, su haqiqa ba waxanda ake zargi ba ne. To, duk wanda ya nemi (jin daxi) bayan wannan, to, su ne masu tsallake iyaka. Mu’minun:5-7.
2.9.5 Ba a Cin Gadon Annabawa

Sai kuma xan Shi’ar ya zargi sayyidina Abubakar Raliyallahu Anhu yana mai cewa: Abubakar ya hana Fatima gadonta. Sai ta ce masa: Kai xan Abu Quhafata! Kai zaka gaji ubanka, ni ban gaji nawa ba? Wai sai Abubakar ya lava ga wata riwaya da kowa bai san ta ba in ba shi ba. Alhalin kuma shi ne abokin jayayyarta, don shi yana cin sadaka. Ya kawo mata hadisin da Alqur’ani ya qaryata shi. Ya ce wai Annabi Sallallahu Alaihi Wasallama ya ce: “Mu Annabawa ba a gadonmu. Duk abin da muka bari sadaka ne”. Alhalin kuwa Allah Ta’ala na cewa:

ﭽ ﮓ ﮔ ﮕ ﮖﮗ ﮘ ﮙ ﮚ ﮛﮜ ﭼ النساء: ١١

Allah yana yi maku wasicci a game da ‘ya’yanku. (Idan kun mutu) namiji zai gadi rabon mace biyu 4:11

Kuma Allah bai sanya wannan ga sauran al’umma banda Manzo ba. Sai ya qaryata riwayarsu. Kuma Allah ya ce:

ﭽ ﭯ ﭰ ﭱﭲ ﭼ النمل: ١٦

Kuma Sulaimanu ya gadi Dawuda

Ya kuma ce:

ﭽ ﭮ ﭯ ﭰ ﭱ ﭲ ﭳ ﭴ ﭵ ﭶ ﭷ ﭸ ﭹ ﭺ ﭻ ﭼ ﭽ ﭾ ﭿ ﮀﮁ ﭼ مريم: ٥ – ٦

Kuma haqiqa ni, na ji tsoron dangi a bayana, kuma matata ta kasance bakarariya (maras haifuwa)! To, ka ba ni wani mataimaki daga wajenka. Ya gaje ni, kuma ya yi gado daga gidan Yaquba 19:5-6

Martani:

Cewar da ya yi wai, Nana Fatima ta ce wa Abubakar: “Kai za ka gaji ubanka, ni ba zan gaji ubana ba?”. Ba maganar da aka san ingancinta ba ce. Da ta inganta kuwa, ba za ta zama hujja ba. Domin babu shakka babanta Sallallahu Alaihi Wasallama yana da nisan banbanci da nasa. Ya ko za a yi wannan gwaji? Ai su Annabawa Allah ya kare su daga a gaji duniya daga wurinsu. Don kada wannan ya zama marataya ga masu son zarginsu. Amma irin Abubakar sai ya gaji mahaifinsa lamui lafiya ba wata damuwa. Kamar yadda Allah ya kare Manzonsa daga iya rubutu ko tsara waqa, ba don hakan tana aibi ga sauran jama’a ba; sai don toshe qofar zargi.

Cewa kuma wai, Abubakar ya lava ga wata riwaya da shi kaxan ya zo da ita, zargi ne da ba shi da qamshin gaskiya. Domin hadisin da ya bayyana ba a gadon Annabawa ba Siddiqu ne kawai ya karantar da shi ba. An same shi daga Umar da Usman da Ali da Xalhatu da Zubairu da Sa’adu da Ibnu Aufi da Abbas da matan Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama da Abu Hurairata. Kuma riwayoyinsu na nan cikin sanannun littafai ta hanyoyi ingantattu. Masana sun san da haka. Ya rage ma mai wannan zargi xayan biyu; jahilci ko katovara.

Ya kuma ce wai, Abubakar ne abokin jayayyarta. Ba kuwa haka ba ne. Don Abubakar bai ce shi zai ci gadon ko iyalansa ba. Cewa ya yi sadaka ce ga musulmin da suka cancanta. Ba shi kuma cikin masu karvar sadakar don ba shi da buqata da ita. Haka ma iyalansa ba su tava amfanuwa daga gare ta ba daxai saboda wadatarsu. Wannan yana daidai da wani attajiri ya yi shaida cewa, wani ya yi wasicci da wata sadaka ga talakawa. Ba abin da zai hana a karvi shaidarsa a nan, don shi ba abin tuhuma ba ne. Kai, koda yana da wani amfani a cikinta, in ya riwaito ana karva, don ba shaida ba ce; riwaya ce. Riwaya kuma hukunce ne da yake game kowa, a wannan mas’ala ko wata irinta har abada. To, ina kuma ga shi Sahabin Manzo! Ai wannan kamar ganin wata ne. Wanda zai gan shi yana cikin waxanda hukuncinsa zai hau kansu amma ba shi kaxai ba.

Kuma ka ga riwayar nan hukunci ne na Shari’a wanda ya haramta gado har ga matan Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama cikinsu har da ‘yar Abubakar. Ya kuma haramta a sayar ballantana ko shi Abubakar ko wani ya saya.

Sai maganar wai, wannan hadisi ya sava ma Alqur’ani. Ka ga dai ita ayar ba inda ta ce Manzo zai bar gado. To, tunda Sunnah ta tabbatar da ba a gadon nasa, ga kuma Sahabbai sun yi ijma’i a kan haka, ina rikici a nan? Ko ka ji wani cikin sauran magadan ya nace akan neman gadon? Gonar kuma ai ta kai zamanin Ali amma bai raba ta ba alhalin akwai sauran magada, da magadan magada. Ayoyin da ya kawo na gadon su Annabi Sulaiman da Annabi Yaqubu gadon ilimi da Annabta da mulki ake nufi. Ai daman ba wata fa’ida a ce xa ya gaji uba in dukiya ce ya gada. Daman kowa na gadon dukiyar ubansa.

Annabi Sallallahu Alaihi Wasallama ya ce: “Lalle Annabawa ba su gadar da dirhami, ko dinari. Suna gadar da ilimi ne. Saboda haka, duk wanda ya riqe shi to, ya yi riqo da babban rabo”. Abu Dawuda ya riwaito shi da wasu ba shi ba.

To, wannan shi ne. Ka ga ai gadon kuxi ba wani abin yabo a cikinsa. Ita kuma wannan aya ta zo ne da yabon Sulaimana Alaihis Salamu. Amma cewa, Sulaimana ya gadi dukiya daga mahaifinsa Dawuda kamar wani ya ce ne, wane ya ci abinci, ya yi bacci. Ba irin labaran Alqur’ani ba ne wannan.



2.9.6 Fatima ta Nemi Gonar Fadak

Xan Shi’ar ya ce: A lokacin da Fatima ta gaya masa cewa mahaifinta Sallallahu Alaihi Wasallama ya ba ta kyautar Fadak, sai ya ce, ki zo da wani mutum baqi ko ja don ya shede ki a kan haka. Sai ta zo da Ummu Aimana ta sheda cewa haka ne. Sai ya ce mata: Mace ce wadda ba a karvar maganarta. Ga shi kuma duk sun riwaito cewa Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama ya ce: “Ummu Aimana mace ce ‘yar aljanna”. Sai Ali ya yi sheda cewa maganar gaskiya ce. Sai Abubakar ya ce: Wannan mijinki ne. Yana son abin ya koma masa, ba za mu yi maki hukunci da shaidarsa ba. Ga shi ko duk sun riwaito cewa, Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama ya ce: “Ali na tare da gaskiya, gaskiya kuma na tare da Ali, tana juyawa duk inda ya juya. Ba za su rabu ba har su zo wurina a qoramar Alkausara.

Xan Shi’ar ya ci gaba da cewa, sai, Fatima ta yi fushi a kan haka, kuma ta tafiyar ta. Ta rantse ba za ta sake magana da Abubakar ko abokinsa ba har sai ta haxu da babanta ta yi qarar su, gare shi. To, a lokacin da zata rasu, inji shi, sai ta yi wa mijinta Ali Raliyallahu Anhu wasicci cewa, ya rufe ta da dare, don kada xayansu ya yi mata sallah.

Xan Shi’ar ya ci gaba: Dukansu sun riwaito cewa, Annabi Sallallahu Alaihi Wasallama ya ce: “Ya Fatima! Allah Ta’alah yana fushi don fushinki, kuma yana yarda don yardarki”. Kuma duk sun riwaito cewa, Annabi Sallallahu Alaihi Wasallama ya ce: “Fatima sashena ce. Wanda ya cuta mata ya cuta mani, wanda ya cuta mani kuwa ya cuta wa Allah Ta’alah”.

Ya ci gaba da cewa: Da wannan labarin gaskiya ne, to, da bai hallata Abubakar ya bar alfadari da takobi da rawanin Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama a wurin Ali Raliyallahu Anhu ba, a lokacin da Abbas ya nemi a ba shi su. Kuma da Ahlul-Baitin da Allah Ta’alah ya tsarkake su cikin littafinsa sun aikata abin da ba ya halatta, don an haramta masu sadaka amma sun neme ta. Bayan haka ne kuma Jabiru xan Abdullahi ya zo ya ce wa Abubakar: Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama ya ce mani: Idan dukiya ta zo daga Bahraini to, zan xibar maka cikon tafina har sau uku. Sai Abubakar ya ce masa: Ka tafi Baitul-Mali ka xibi daidai abin da ya ce. Jabir ya je ya xiba daga cikin dukiyar musulmi ba tare da wani shedu ba; don kawai maganarsa shi kaxai.
Martani:

Wannan maganar dai ta qunshi qarairayi da qage mai yawa. Bari mu soma bayanin su:

Tun farko, a cikin maganarsa akwai tuqa da warwara, don da farko cewa ya yi Fadak gado ce. Yanzu kuma ya ce kyauta ce. Amma, bari mu bi shi a haka. Sai mu ce: Ita wannan kyautar yaushe ne aka yi ta? Mu mun san Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama ya tsarkaku daga yin wasicci ga mai gado. Don hakan ya sava ma Shari’a. Idan kuma tun lokacin da yake cikin qoshin lafiyarsa ne ya yi mata kyautar, to, me ya sa ba ta karva ba sai yanzu? Idan mutum ya yi kyauta, ba a karve ta ba har ya mutu, kyauta ta tashi kenan. Ya ko za a yi Manzo Sallallahu Alaihi Wasallama ya ba da kyautar Fadak ga Fatima kuma matansa da sauran musulmi ba su sani ba, har ya zame cewa Ummu Aimana ko Ali Raliyallahu Anhuma ne suka kevanta da sanin hakan?

Danganta wannan neman Fadak shi kansa ga Fatima, qarya ne. Abul Abbas xan Suraiju ya soke maganar yana mai cewa: Hadissan Buhturi xan hassanu da ya karvo daga Zaidu xan Ali cewa Fatima ta gaya ma Abubakar Raliyallahu Anhu cewa, Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama ya ba ta kyautar Fadak, kuma wai, ta zo da shedar mace da namiji sai ya qi karva, wannan maganar na da ban mamaki!! Lalle Fatima ta tambayi Abubakar gadonta, sai ya faxa mata cewa Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama ya ce: “Ba a gadon mu”. Amma ba a ce Fadak ce ta nema ba, balle a ce ta shedar da wani a kan haka.

Amma Jarir ya riwaito daga Mugirata daga Umaru xan Abdulaziz cewa: “Fatima ta nemi Annabi ya ba ta Fadak, bai ba ta ba. Kuma Annabin ya kasance yana ciyar da wasu Banu Hashim, danginsa daga cikinta, yana taimakon masu rauninsu, ya aurar da marasa aure duk daga cikinta. Haka aka ci gaba har qarshen rayuwar Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama. Fatima kuma ta karvi gaskiya”. Sarki Umaru xan Abdulazizi ya qare da cewa: “Don haka, ina sheda maku cewa, ni ma na bar ta yadda take lokacin Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama”.

Ba wani ingantaccen hadisi da ya tabbatar da cewa Fatima ta ce an ba ta Fadak, ko wani ya yi sheda a kan haka. Da kuwa an yi haka da an riwaito shi, don abin jayyayya ne wanda ya shafi al’umma, kuma aka yawaita maganganu game da shi. Tun a lokacin ba xaya daga cikin musulmi da ya ce ya ji Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama ya ba Fatima ita, ko ita Fatima ta ce an ba ta. Sai daga baya wannan Buhuturi xan hassan ya yo wannan riwaya.

To, ko da an qaddara cewa wannan hadisin ya tabbata, babu hujja a cikinsa. Don Fatima ba ta ce zata rantse tare da shedu aka hana ta ba. Kuma Abubakar bai ce ba shi yarda da shedu da rantsuwa ba.

Abin da tarihi ya bayyana shi ne, Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama gonaki uku ne ya zava, waxanda suka haxa da gonar Banun Nadhir, da ta Haibara da Fadak. Sai ya keve ta Banun Nadhir don biyan buqatunsa da ke iya tasowa. Fadak kuma ya keve ta don matafiya masu buqata. Haibara kuma sai ya raba ta kashi uku; kashi biyu daga ciki ya raba su a tsakanin musulmi, xayan kuma don ci da shan iyalinsa. To, duk abin da ya saura bayan an fitar wa iyalinsa sai a sake raba shi ga matalautan Muhajiruna.

A riwayar Laisu lokacin da Fatima Raliyallahu Anha ta aika ma Abubakar tana tambayar sa game da gadonta cikin dukiyar Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama wadda ta haxa da abin da Allah ya ba shi a Madina ba tare da yaqi ba, da kuma Fadak, da abin da ya saura daga cikin humusin Haibara sai ya gaya mata cewa, Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama ya ce: “Ba a gadonmu (Annabawa). Abin da duk muka bari sadaka ne. Kawai dai ‘yan gidan Manzo suna iya amfani da ita dukiyar, amma ba mallaka ba”. Abubakar ya qara da cewa: “Wallahi ba zan canza komai ba cikin dukiyar daga yadda Annabi Sallallahu Alaihi Wasallama ya saba yi da ita. Don haka sai bai ba Fatima komai na gado ba.

Duk wanda ya san farihin sayyidina Abubakar tare da duba riwayoyin da suka zo kan wannan al’amari ya san lalle Abubakar yana ganin girman Fatima kuma yana karvar maganarta. To, ina kuma ga a ce ta zo da shaidu irin waxanda suka ambata.

Bisa qaddara cewa, ana iya gadon Annabi Sallallahu Alaihi Wasallama, to, waxanda ke da haqqi su ne matansa da wan mahaifinsa Abbas. A irin wannan kuwa da an buqaci shedu mace xaya ko namiji xaya ba zasu wadatar ba bisa ga Alqur’ani da sunnah da haxuwar malamai. Don haka, in har jayayya ce ba Abubakar ne mai yinta ba.

Kafa hujja a irin wannan lamari da kasancewar Ummu Aimana ‘yar aljanna jahilci ne da ya wuce wuri. Domin hujja ce a kansa. Ba wai sayyidina Abubakar ba, koda Hajjaju xan yusufa da Mukhtaru xan Abi Ubaid suka ce basu amsar shedarta ita kaxai ga haqqi, su faxi gaskiya, don qa’ida ce ta Shari’a cewa, ba a karvar shedar macce ga abin da ya shafi kuxi. Zamanta ‘yar aljanna ko bai canza hukuncin Shari’a a wurin masu ilimi da hankali.

Ummu Aimana dai, ita ce uwar Usamatu xan Zaidu. Kuma ita ce wadda ta yi renon Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama. Tana kuma cikin muhajirai mata, masu daraja. Don girman darajarta ne ‘yan Shi’ar suke so su lava gare ta suyi mata qarya. Kuma babu wani littafi na msulunci da aka yarda da shi wand aya kawo wannan magana.

Haka ma cewar da ya yi wai, Ali Raliyallahu Anhu ya yi shaida cewa, an ba ta aka qi karvar shaidarsa don yana mijinta. Duk ba gaskiya ne ba. Amma bisa qaddara an yi hakan, to, ba aibi ba ne. Don shaidar miji ga matarsa ba a aiki da ita a wurin mafi yawan malamai. Wanda kuma suka yarda a karve daga cikin malaman cewa suka yi sai idan an samu qari akan mijin, kamar a samu wani namiji xaya ko kuma mata biyu.

Hadisin da ya kawo cewa, Ali na tare da gaskiya, ita ma gaskiya tana tare da Ali duk inda ya juya ba za su rabu ba har ya zo mani a wurin Alkausar. Wannan magana ce ta qarya da jahilci. Don ba ta da madogara ko daidai yanar gizo. Ka ga kuwa akwai muni matuqa, mutum ya qaga qarya ya jingina ga Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama kuma ya ce wai, duk malaman Sunnah sun san da ita a matsayin gaskiya.

Sai maganar da ya jingina ga Fatima cewa ta fusata da Abubakar kuma ta rantse ba zata sake yi masa magana ba, shi da abokinsa. A zatonsa yana yabonta ne, alhalin kuwa suka ce mai girma a gare ta. Ina abin fushi a nan? Abubakar bai yi wani hukunci ba da ya sava ma gaskiya. Kuma gama-garin musulmi na iya haqurin karvar irin wannan gaskiya, to, ina ga Fatima ‘yar gidan Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama? Ba yabo gare ta a nan, ba aibantawa ga Abubakar.

A bisa imaninmu da iya saninmu, yawancin abubuwan da ake riwaitowa game da Fatima da wasu Sahabbai irin waxannan qarairayi ne. Wasu hikayoyin kuma suna da fassara mai ma’ana wadda ke fitar da su daga zargi. Idan kuma har xayansu ta tabbata cewa, ya aikata kuskure ko laifi, to, ai su ba ma’asumai ba ne, waliyyan Allah dai ne, ‘yan aljanna da Allah Ta’ala ke gafarta ma zunubbansu.

Haka ma abin da ya ambata na cewa ta yi wasicci da Ali ya rufe ta da dare don kada xayansu ya yi mata sallah. Jingina wannan irin wasicci ga Fatima shi ma jahilci ne da wauta. Me zai sa Fatima ta yi wannan wasicci? Ai kowa ya san sallar musulmi qarin alheri ce da lada ga mamaci. Kuma mafificin halitta ba zai cutu ba koda mafi sharrin halitta ya yi masa sallah. Ga dai Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama, kowa ya yi masa sallah; muminai da fajirai. Kai har ma da munafikai. Irin wannan in bai amfane shi ba, ba zai cutar da shi ba. Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama kuwa ya san cewa a cikin al’ummarsa akwai munafukai amma bai yi wasicci kada wani ya yi masa sallah ba.

Hadisin cewa, Allah na fushi da fushin Fatima, kuma yana yarda da yardarta. Shi ma qarya ne irin wancan. Babu shi a cikin ko xaya daga cikin littafan hadisi. Ba shi kuma da wani sanannen isnadi daga Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama ba. Mu dai mun sheda cewa Fatima yar’aljanna ce, kuma tabbas Allah ya yarda da ita. Muna kuma irin wannan shedar ga Abubakar da Umar da Usmanu da Ali da Xalhatu da Zubairu da Sa’adu da Sa’idu da Abdulrahaman xan aufu da Abu Ubaidata. Mun kuma aminta da abin da Allah Ta’alah ya ba da labari a wurare da yawa game da su; cewa ya yarda da su. Kamar in da maxaukakin Sarkin ya ce:

ﭽ ﭑ ﭒ ﭓ ﭔ ﭕ ﭖ ﭗ ﭘ ﭙ ﭚ ﭛ ﭜ ﭝ ﭼ التوبة: ١٠٠



Magabata na farko daga cikin Muhajiruna da Ansaru da waxanda suka bi su da kyautatawa, Allah ya yarda da su, su ma sun yarda da shi. Attauba 100.

Da cewar da Allah Ta’ala ya yi:

ﭽ ﮎ ﮏ ﮐ ﮑ ﮒ ﮓ ﮔ ﮕ ﮖ ﮗ ﭼ الفتح: ١٨

Haqiqa, Allah ya yarda da muminai a lokacin da suke yi ma ka mubaya’a a qarqashin itaciya. Suratul Fathi: 18.

Mun kuma yarda da abin da ya tabbabata cewa, Manzo Sallallahu Alaihi Wasallama ya rasu yana mai yarda da Sahabbansa. Kuma mun san duk wanda Allah ya yarda da shi da Manzo, to fushin wani ko wane ne ba zai cutar da shi ba.

Hadisin da ya kawo cewa, Fatima sashen Manzo ce. Wanda duk ya cuta mata ya cuta masa. Duk da yake ya yi qari a cikinsa. Amma dai Annabi ya faxe shi ne a lokacin da Ali Raliyallahu Anhu ya nemi auren xiyar Abu Jahali. Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama ya hau mimbari a kan haka, ya yi huxuba yana cewa: “Haqiqa mutanen gidan Hashimu xan Mugirata sun nemi in ba da izinisu aurar da ‘yarsu ga Ali xan Abu Xalib. To, ba zan yi izini ba, kuma ba zan yi izini ba, kuma ba zan yi izini ba. Domin Fatima shashena ce; duk abin da ke damun ta yana damu na. Sai dai in Ali yana son ya saki xiyata ya Auri tasu.

Sai cewar da ya yi, in da gaskiya ne da bai halatta Abubakar ya bar alfadarin Manzon Allah da takobinsa da rawaninsa wurin Ali ya hana ma Abbas shi lokacin da ya nema. Sai a ce masa: Wa ya ce Abubakar da Umar sun ba Ali don ya mallaka? Ai sun bar su ne a hannunsa kamar yadda suka bar sadakarsa wurin Ali da Abbas don su ba da ita ga waxanda Shariah ta ce a ba.

Maganar tsarkake Ahlul-Baiti daga cin sadaka. Da farko, Allah Ta’ala bai ce ya tsarkake dukkan Ahlul-Baiti ba. Ku ma kun san cewa akwai daga cikin Banu-Hashim waxanda ba a tsarkake daga savo ba, musamman ma a gun ku ‘yan-sha-biyu, da ke xaukar duk wani dangin Banu-Hashim da ke son Abubakar da Umar a matsayin wanda ba tsarkakakke ba.

Abin da dai Allah Ta’ala ya ce yana son haka gare su, kamar yadda ya ce yana son haka ga muminai cikin ayar taimama. Allah na son haka, kuma ya yarda da haka, ya yi umurni a kan haka. Wanda ya aikata, to, ya cimma muradin da aka so masa, wanda kuma bai aikata ba, to, ba zai sami muradin ba.

Sai maganar sadaka xin da aka haramta masu. Abin da aka haramta masu shi ne sadakar wajibi, ita ce Zakka. Amma sadaqoqi na ganin dama ba laifi ba ne a kansu in sun amfana da su. Ai suna shan ruwan rijiyoyin sadaka misali, waxanda ake ajiyewa tsakanin Makka da Madina. Da kansu kuma suna faxin cewa, sadakar farilla ce aka haramta mana, ba a haramta mana sadakar nafila ba. To, in ko haka ne, me zai hana su amfana da sadakar Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama ga jama’ar musulmi? Wannan dukiyar ba zakkar da aka farlanta wa Manzo Sallallahu Alaihi Wasallama ba ce. Kuma na haramta masu zakka ne don tana dauxar mutane. Amma abin da Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama ya bari na ganimar da Allah ya ba shi halal ce ga re shi, kuma ya sanya sashenta ya zama sadaka ga musulmi. Don haka Ahlul-Baiti na iya cin moriyarta kamar sauran musulmi.

Game da tsokacin da ya yi kan karvar da Jabir Raliyallahu Anhu ya yi ga alqawarin da Annabi Sallallahu Alaihi Wasallama ya yi ma sa daga wurin Abubakar. Jabir dai bai raya cewa yana son haqqin wani ba, ya dai nemi wani abu ne daga baitul-mali, shugaba kuma na da damar xaukar sa ya ba shi, ko da kuwa Manzo Sallallahu Alaihi Wasallama bai yi masa alqawari ba. Ka ga ba a buqatar shedu a nan.

A gaskiya, duk maganganun da suke yi game da Fatima Raliyallahu Anha cewa ta nemi Fadak kuma ta kafa sheda akan Annabi Sallallahu Alaihi Wasallama ya ba ta ita. Duk wannan suka ce suke yi gare ta a fakaice ba yabo. Kuma Allah ya raba ta da waxannan qazuffa nasu, ya nisantar da ita daga gare su.


Yüklə 2,75 Mb.

Dostları ilə paylaş:
1   ...   8   9   10   11   12   13   14   15   ...   51




Verilənlər bazası müəlliflik hüququ ilə müdafiə olunur ©muhaz.org 2024
rəhbərliyinə müraciət

gir | qeydiyyatdan keç
    Ana səhifə


yükləyin