Tafarkin sunnah



Yüklə 2,75 Mb.
səhifə15/51
tarix28.10.2017
ölçüsü2,75 Mb.
#17506
1   ...   11   12   13   14   15   16   17   18   ...   51

Amma ka sani, babu wani daga cikin malaman ahnlus –sunna, irin waxanda ake shiga xaka da maganarsu, da ya yi imani da cewa Yazidu da makamantansa na kafaxa-da-kafaxa da halifofin Manzon Allah, irin su Abubakar da Umar da Usmanu da Ali. Raliyallahu Anhum a daraja da xaukaka. Ko alama. Hasali ma ahlus- sunna riqe suke da hadisin nan da ke cikin: As –sunanu, wanda ke cewa: “Halifancin annabta zai qare bayan shekaru talatin, mulkin gargajiya ya maye gurbinta.”


Wannan kenan. Idan kuma xan Shi’ar na so ne ya ce waxannan mutane da ya kira sashen Ahlus-Sunnah sun yarda da Yazidu, har quryar zukatansu, a matsayin Sarkin Musulmi kuma halifa a zamaninsa, mai wuqa da nama. Kamar yadda suka aminta da sauran halifofi; Umawiyyawa da Abbasiyyawa, to, babu wata jayayya a cikin haka. Duk wanda ma ya ce ba zai yarda da haka ba, to ya tabbata kangararre. Domin kuwa gaba xayan duniyar musulunci ta ji kuma ta yarda da bai’ar da aka yi wa Yazidu bayan rasuwar mahaifinsa Mu’awiyah. qasashen musulmi da suka hada da Sham da Masar da Iraqi da khurasan da sauransu duk, suka kasan ce qar qashin ikonsa.

Ka ga da haka ne ya zama shugaba kuma halifa kuma Sarkin Musulmi. Babu kuma wani dalili da za a iya riqo dashi, a hana shi zama haka. Yadda kasan dole ne a kira mai ba mutane salla da sunan liman; ko anqi ko anso. Domin dazarar kowa ya yalla ido ya ga mutum ya rungume hannuwa gaban sahu, to wautace wani ya qi yarda da kasancewarsa liman gare su. Shi kuwa zancen kasancewarsa mutumin kirki ko asharari, wata maganace daban.

To, a kan wanan ma’auni ne Ahlus-Sunnah suka yi imani da kasan cewar Yazidu da Abdulmalik da Mansur da wasunsu sarakunan musulunci. Shi kuwa duk wanda ke musun haka, dai-dai yake da wanda ke musun halifancin Abubakar da Umar da Usmanu. Da mulkin kisra da qaisar da Najjash, da wasu sarakuna.

Amma cewa xaya daga cikin waxannan halifofi da sarakunan musulunci ma’asumi ne. Ko kuma adali ne a cikin gaba xayan al’amurransa; baya sava wa Allah fai da voye, wannan ba aqidar malamai da shugabanin musulunci ba ce.

Sanya wannan mala tukuna.

Shi kuwa Husaini Raliyallahu Anhu a wurin Ahlus-Sunnah, ko shakka babu kisan da aka yi masa zalunci ne. Kuma Allah Subhanahu Wa Ta’ala ya karvi shahadarsa. Wannan kisa nashi a wurinmu daidai yake da na duk wanda aka kashe bai ji bai gani ba, sai don kawai ya ce Allah! Kuma duk wanda ya aikata wannan mugun aiki ko ya taimaka cikin tabbatuwarsa ko ya yi farin ciki da haka, to ya sava wa Allah ya kuma cutar da Manzo. Don ya yi tarayya da maqiya Allah a cikin jefa musulunci cikin fitina.

Amma kuma a wuri xaya, kamar yadda muka faxa, hakan ta zama sanadiyyar samun shahada da daraja da xaukaka ga Husaini Raliyallahu Anhu. Allah Ta’ala ya nufi cewa shi da xan’uwansa za su sami irin wannan babban rabo, da ba a samu sai da zufan goshi. Eh! Tsuntsu ne daga sama gasashshe suka samu. Don ba su ga abubuwan da wasu daga cikin mutanen gixansu suka gani ba na hawa da gangara. Domin kuwa ko da aka haife su yabanyar musulunci ta qetare siraxin fari. Suka rayu cikin girma da aminci, sai ga shi cikin ikon Allah xayansu yara su ta hanyar shayar da shi guba. Xayan kuma ta hanyar kisan ga-ni-ga-ka. Da haka ne kuma suka sami shiga sahun manyan shahidai.

Amma kuma daxa, duk da haka, zunubin wannan kisan gilla da aka yi wa Husaini da ‘xan’uwansa, bai kai girman zunubin kisan gillar da waxansu al’ummomi suka yi wa Annabawa ba. Ka tuna irin yadda Allah Ta’ala yake ba mu labarin irin yadda bani’isra ila ke karkashe Annabawa ba li ba la. To, musiba da zunubin da ke cikin kashe ba annabe sun yi wa wanan fintinqau. Kai! Ko kisan gilar da aka yi wa halifa Ali da Halifa Usmanu Raliyallahu Anhuma duk sun fi wannan girman zunubi da musiba.

To, tunda kuwa har haka ne. Ashe ka ga kenan babu abin da ya wajaba a kan musulmin qwarai a cikin waxannan lokuta na sabkar musibu, sai haquri da mayar da al’amari a wurin Allah. Kamar yadda Allah da Manzonsa ke so,

Amma a maimakon haka, sai gashi wannan kisa na Husaini Raliyallahu Anhu ya sa wasu mutane sun biye wa qixan shexan. Inda hakan ta zama sanadiyar tsiruwar waxansu bidi’oi guda biyu: bidi’ar zama cikin baqin ciki da jimami tsawon yinin ranar Ashura, tare da mare maren kai da kai, da hargowa da koke- koke da bege da rera wakokin ta’aziyya. Tare da wannan kuma, sai ka taras sun buge ga: Bidi’a ta biyu wato zagin magabata da la’antar su, tare da shafawa waxanda ba su ji ba su gani ba daga cikinsu kashin kaji. Wanda hakan kan kai su ga zagin uwayen tafiya (Assabiqunal auwaluna) A qarshe kuma su zauna xandali suna qaranta yadda al’amarin abin ya faru wai. Wanda mafi yawan labarun da suke faxa wa mutane a kan hakan qarya ce tuburan.

Kuma kar ka daxa kar ka qara.’Yan Shi’a sun tsiri waxannan abubuwa ne tare da mayar da su wata sunna tasu, don kawai su haifar da fitina a cikin musulmi tare da raba kanunsu. Gaba xayan musulmi sun yi itifaqi a kan cewa, ko ga matsayin mustahabbi waxannan abubuwa da suke yi a wanan rana ba su kai ba balle wajibi. Kai! Hasali ma fita hayyaci da jimami saboda wasu musibu da suka daxe da faruwa a rayuwa, na daga cikin manyan abubuwan da Allah da Manzonsa suka haramta. Kamar yadda suka haramta matsanacin xoki da annashawa tare da fita hayyaci saboda wani abu na farin ciki.

Ita kuwa cewar da xan Shi’ar ya yi wai an ribace mata da ‘ya’ya matan Husaini Raliyallahu Anhu An kuma xauke su a kan raqumma babu ko siridda, aka zagaya qasa da su, qarya ce lafiyayyarta.

Alhamdu lillahi. A iya saninmu da tarihin musulunci, musulmi ba su tava ribace wata Bahashima ba. Hasali ma babu wani lokaci da aka tava jin al’ummar Muhammadu Sallalahu Alaihi Wasallama ta halatta ribantar wani Bahashime. Amma dai muna jin qarya ce – qarya cen da wasu jahilai ma’abuta son zuciya ke yaxawa. Kamar yadda muka ji wata qungiya daga cikinsu na cewa wai Hajjaju, ya tava kashe sharifai (Banu Hashim).

Haka kuma cewar da ya yi wai babu wani dutse da za’a xaga, a kan wata lalura a duniya, a ranar da aka kashe Husaini face an taras da jini qundum a qarqashinsa, ita ma qarya ce bayyananna.

Amma ka ga cewar da ya yi imamu Az-zuhri ya ce: Babu wan da yara ge daga cikin waxanda ke da hannu a cikin kisan Hussai Raliyallahu Anhu face Allah ya azabtar da su tun duniya.

Wannan abune mai yiyuwa. Domin ta tabbata cewa zalunci shi ne zunubin da Allah ke gaggauta azabtarda wanda ya yi shi tun duniya.babu kuwa zaluncin da ya kai kisan Husaini Raliyallahu Anhu girma.

Amma kuma ko shakka babu, cewar da ya yi wai, a kan Hassan da Husaini ne ayarda ke cewa: Ka ce, Bani tambayar ku wata ijara a kansa face dai soyayya ta cikin zumunta. (42:23) ta sauka qarya ce lafiyayya.

Dalili kuwa shi ne; ita dai wannan aya tana cikinsurar shura ne. Ita kuwa wannan surar ko shakka babu a Makka ne ta sauka; wato tun kafin a aurar wa Ali da Fatima Raliyallahu Anhama har su haifi Hasan da Husainin. Tarihi ya tabbatar da cewa an yi wannan aure ne bayan anyi Hijra zuwa Madina da she karu biyu. Kuma ba suyi baiko ba sai bayan yaqin Badar, wanda akayi a cikin watan azumi na sheqarar.

Abin da wannan aya ke nufi, kamar yadda xan Abbas yabayyana, Imamul Buhari kuma da waninsa suka riwaito, shi ne; Allah (S W A) na magana ne da harshen Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama da cewa ; ka ce musu ba ka neman wani sakamako daga wurin su a kan alherin da ka zo masu dashi na musulunci,face su dubi abin da ke tsakaniku na zumunta;kada su cutar da kai.

Xan Abbas ya qara da cewa, hakan kuwa ta faru ne: saboda babu wata qabila daga cikin qabilun Quraishawa, wadda Manzon Allah ba yada zumunci da su. Ka ji xan xangi.

Amma kuma duk da haka munji wasu marubuta daga cikin Ahlus-Sunnah wal jama’a da ‘yan Shi’a, daga cikin muqarraban imamu Ahmad da wasunsu na yayata wani qagaggen hadisi, wanda kecewa wai: A lokacin da wannan aya ta sauka, Sahabbai sun tambayi Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama cewa: su waye ma kusantan naka? Wai sai ya ce: Ali da Fatima da ‘Ya’yansu guda biyu.

To, malamai ma’abuta ilimin hadisi sun yi ittifaqi a kan cewa, wannan hadisi qagagge ne.


2.9.20 Yazidu Bai Cancanci La’anta ba

Xan Shi’ar ya zargi wasu daga cikin Ahlus-Sunnah, waxanda hankalinsu bai natsu da cancantar Yazidu da shiga sahun sarakunan musulunci ba. Amma kuma tattare da haka ba su yarda da a la’ance shi ba. Amma kuma wai, A cewar xan Shi’ar, sun yarda da kasancewarsa azzalumi. Tunda ya kashe Husaini ya kuma yi awon gaba da duk abin da ya mallaka.

To, wai ko sun manta da faxar Allah Ta’ala: To, La’anar Allah ta tabbata a kan azzalumai. (11:18)?

Kuma ga shi Abul-Faraji Ibnul-Jauzi, xaya daga cikin malaman mazhabar hanbaliyyah ya ce: An samo daga xan Abbas Raliyallahu Anhu wanda ya ce wai: Allah Ta’ala ya yi wahayi zuwa ga Muhammadu Sallallahu Alaihi Wasallama cewa: Na karvi rayukan mutum dubu saba’in akan kashe Annabi Yahya xan Zakariyya. Zan kuma karvi rayukan mutum dubu xari da arba’in akan kashe jikanka.

Haka kuma As-suyudi, xaya daga cikin mutane masu girma a wurin Ahlus-Sunnah ya bayar da labarin cewa: “Watarana na sauka karbala ina xauke da kayan abinci na na kasuwanci a inda wani mutun ya karvi baqunci na. Bayan mun qare cin abincin dare, sai muka xauko hirar kisan gillar da aka yi wa Husaini a wannan wuri. Sai ni da fatake yan uwana muka ce: “ Ka ko ga babu wanda bai yi mutuwar qasqanci ba, daga cikin waxanda ke da hannu a cikin kisan Husaini.” Sai mai masaukinnan namu ya kada baki ya ce: “Lallai kune sarakunan qaryar duniya! To, ni xin nan dake gabanku tare da ni aka kashe shi, Amma kuma gani daram”. Ah! Ai dare na tsalawa; alfijiri na gab da ketowa, sai kawai muka ji ana cewa kai baqi ku tashi ba lafiya. “Muka ce me ya faru?”

Sai aka karva mana da cewa: Ai jiya da dare mai masaukin nan namu yana gyaran a-ci-bal-bal xinsa, sai kawai yatsansa ya lashi wuta. Nan take wutar ta bi ta jinin sa ta kone shi qurmus. Wallahi haka muka taras da gawarsa baqi qirin kamar gawayi.

Xan Shi’ar ya ci gaba da cewa: kuma Muhammad xan Yahya ya tambayi Ahmad xan Hambali watarana, a kan Yazidu. Sai ya karva masa da cewa: Shi ne wanda ya aikata aika-aikan nan.ya ce: “sai na ce masa; meya aikata?” sai ya karva mani da cewa: Keta alfarmar Madina ya yi.

Kuma wai watarana Salihu, xaya daga cikin ‘ya’yan Ahmad xan Hambali ya ce wa mahaifin nasa: Baba naji wasu mutane na cewa muna daga cikin waxanda suka yarda da jivintar Yazidu. Sai wai shi kuma ya karva masa da cewa: Haba Salihu, ai ba wanda ke yarda da jivintar Yazidu, sai wanda bai yi imani da Allah da ranar lahira ba. Ko me kace? Sai Salihun ya ce masa: To baba me ya sa ban ji kana la’antar sa ba? Sai wai shi kuma ya karva masa da cewa: Me ko zai hana in la’anci wanda Allah ya la’anta a cikin littafinsa? Ba ka dai dace da hakan ba ne. Sai kuma ya sake ce wa uban: To, baba a ina Allah ya la’ance shi? Sai ya karva masa da cewa a cikin faxar sa: To, shin kuna fatar idan kun juya (daga umurnin) za ku yi varna a cikin qasa, kuma ku yanke zumuntarku? Waxannan su ne waxanda Allah ya la’ane su, sannan ya kurumtar da su, kuma ya makantar da ganinsu (47:22-23).

Xan Shi’ar ya ci gaba da cewa: To, akwai zalunci da varnar da ta kai kamar kisan kai da keta alfarmar birnin Madina tsawon kwana uku tare da ribance mutanen da ke cikinta? Tare kuma da kashe wasunsu da dama, da suka haxa da Quraishawa da Ansaru da Muhajiruna, waxanda adadinsu bai kasa xari bakwai. Da wani adadin na bayi da ‘ya’ya da mata da ba a san iyaka ba. Aika-aikar da tasa sai da gawawwaki suka yi iyo a cikin gulbin jini. Wanda kuma ya kai har ga qabarin Manzon Allah Sallalahu Alaihi Wasallama; raudarsa ta cika maqil da jini. A qarshe kuma suka koma suka harbi Ka’aba da manjaniqu, ya roshe, suka kuma liqa mata wuta; ta ci ta canye. Akwai varnar da ta kai ga haka?

Me zai sa waxannan mutane su yi shayin la’antar mai irin wannan aiki? Ko sun manta da cewar da Manzon Allah Sallalahu Alaihi Wasallama ya yi: Allah zai sanya duk wanda ya kashe Husaini a cikin wani akwati na wuta, ya kuma yi masa rivin azabar da zai yi wa ‘yan wuta. Ta hanyar xaure hannuwansa da qafafunsa da wata sarqa ta wuta, a tungumi akwatin a jefa wuta ya yi qasa.Ya dinga wani wari da ko ‘yan wuta sai sun roqi Ubangiji tsari daga gare shi. Haka zai tabbata cikinta har abada, yana shan azaba mai raxaxi. Duk lokacin da fatar jikinsa ta nina ta kware, sai Allah ya mayar da ita sabuwa fil, don azabar ta shigeshi sosai; da minti xaya ba za’a sassafta masa ba.Ana yi ana shayar da shi ruwan zafin jahannama.Kaico qaryar maqaryata ta qare sun shiga hannun Allah.

Xan Shi’ar ya rufe da cewa: Kuma wai Manzon Allah Sallalahu Alaihi Wasallama ya ce: “Hushin Allah da nawa sun tsananta a kan wanda ya zubar da jinin zuri’ata ya kuma lave da su ya cutar da ni”.
Martani:

Babu wani dalili da zai sa a la’anci Yazidu shi kaxai domin kuwa bai cancanci hakan ba; duk kuwa wanda ya dage akan tabbatar da la’ana a kansa to kamar yana cewa ne takwarorinsa daga cikin wasu sarakuna da halifofin musulunci duk la’anannu ne, kai sun ma fishi zama haka. Domin kuwa duk wanda ya san tarihin musulunci, ya san cewa akwai dayawa daga cikin shugabanni waxanda Yazidu yafisu dama-dama, kamar: Mukhtar xan Abu Ubaidu as-saqafi, sarkin Iraqi.Wanda ya tsaya kai da fata akan xauko wa Husaini fansa ta hanyar azzabtar da waxanda suka kashe shi.Wanda qarshe yai da’awar cewa Jibirilu ya zo masa da wahayi .haka kuma Yazidu yafi Hajjaju xan yusuf dama.

Domin kuwa gaba xayan mutane sun yi ittifaqi a kan cewa zaluncin Yazidu bai ko kama qafar nasa ba.

To, kuma dai duk da tabbatar haka,qololuwar hukuncin da ake iya yanke wa Yazidu da waxannan sarakuna takwarorinsa da makamantansu, shi ne na kasancewa “fasiqai” amma ba a la’ance su ba.Domin kuwa babu inda shari’a tayi umurni da la’antar wani fasiqi.

Nau’in mutanen da Sunnah ta zo da lafuzzan la’antar su sanannu ne. Kamar cewar da Annabi Sallallahu Alaihi Wasallam ya yi: Allah ya la’anci varawon da zai saci qwarar qAai har a yanke masa hunnu. Da cewar da ya yi:Allah ya la’anci wanda ya qirqiro bidi’a ko ya daurewa mai qirqiro ta gindi. Da kuma cewar da ya yi: Allah ya la’anci mai cin riba da kuma mai bayar da ita da mai rubuta ta da mai shaida akan ta. Da kuma cewar da ya yi: Allah ya la’anci mai auren xibar wuta da wan da akeyinsa don shi. Haka kuma da cewar da ya yi: Allah ya la’anci giya da mai shirya ta da kayan haxinta da xan dakon ta da abin da ake xaukar ta a ciki, da mai rarraba ta ga mashaya, da wanda yaci kuxinta.

To, ka ga ba zancen la’anta kenan,ga wanda ba xaya da ga cikin waxannan mutane ba.

To, kuma kowancan abu da mutane ke ta yakutar Yazidu a kansa. Wato abin da ya aikata wa mutanen Al-harrah, ai akan hujja ya yi shi. Domin kuwa bai xauki wani mataki a kansu ba bayan sun yaya ta yimasa tawaye da qorar xan ginsa da ke wakiltarsa a can, sai da ya aika masu Manzo bayan Manzo, yana neman su dawo suyi masa da’a. Amma hakan ta ci tura. A qarshe dai ya yanke shawarar aika Muslimu xan uqbata al-mariyyu, ya kuma umurce shi da keta alfarmar Madina tsawon kwana uku waxanda ya halatta yaqi a cikin ta idan ya yi nasara a kansu. Haka kuwa akayi. To kaji abin da mutane ke qyama matuqa a cikin al’amarin Yazidu. Wanda har watarana aka cewa Ahmad: ko zaka iya karvar hadisin da aka samo da ga Yazidu? Ya ce Allah ya sawwaqe. Ashe ba shi ne ya yi wa mutanen Madina abin da ya ga dama ba?!

Wannan kam gaskiya ne ya tabbata.Amma bai sa aka qarar da irin sharifan ba. kuma adadin waxanda aka kashe bai .kai dubban xaruruwa ba. Kuma jini bai malala har hubbaren Annabi Sallallahu Alaihi Wasallama ba, balle ya maqare raularsa. Artabin da aka yi ma a lokacin ba a cikin masallaci aka yi shi ba.

Wannan kenan. Ita kuwa Ka’aba da ya ce wa an rusa an qona, wannan ba gaskiya ba ne. Domin kuwa Allah ya riga ya xaukaka ta ya girmamata, ya bata cikakar kariya, ta hanyar sakata qarqashin kulawar sa.

Babu wani lokaci; kafin musulunci ko bayansa, da Allah ya taba yar darwa wani tozarta wannan xaki nasa mai alfarma. Ai ka dai ji irin yadda ya yi biji-biji da ashabul fili, A lokacin da suka yi nufi tava dakinsa. Duk duniya babu wanda bai ji har gowar su ba.

Kuma tarihi ya tabbatar da cewa, ba a tava samun wani daga cikin sarakunan musulunci ba. Tun daga Umawiyyawa har Abbasiyawa da hakimansu, wanda ya tava nufar Ka’aba da wani mugun nufi; Babu wani daga cikin wakillan Yazidu ko Abdulmalik; Hajjaju xan Yusuf ko waninsu da ya tava nufatar haka.

Abin da ya tabbata shi ne, gaba xayan musulmi, na matuqar girmama wannan daki na Allah. Abida ma yakawo Ka’aba a cikin wannan mas’ala shi ne shigar da Ibn Zubairu ya yi a cikinta, wanda shi ne dakarun Yazidu suka so datsewa, har suka har ba masa manjariqu. Amma ba a Ka’abar sukayi niyyar harbi ba.

Wani abu da kuma zai qara tabbatar maka da cewa ba Ka’abar ce sukayi niyyar harbi ba shi ne, shigar da sukayi cikin masallacin bayan sun kashe xan Zubairu, suka yi xawafi. A matsayin hajjin wannan shekaara, a qarqashin jagorancin Hajjaju wanda ya gudanar da ibadar akan tafarkin xan Umar, ba tare da ya sava masa ko da a mas’ala xaya ba, kamar yadda Abdulmalik xan Marwanu ya hore shi da yi.

Ka ga a hankalce, da a ce sun zo ne da nufin tozarta Ka’aba da keta alfarmarta, da sun mayar da ita labari,tunda sun sami galaba da iko a kan haka. Kamar dai yadda suka aika da Zubairu lahira da ya shiga hannun su.

Haka kuma hadisin da xan Shi’ar ya kawo, wanda ya bayyana halin da wai, wanda ya kashe Husaini zai sami kansa a ranar qiyama, qar ya ce lafiyayya, tun daga far kon sa har qarshe ( ina fatar baka manta da hadisin ba).

Ko shakka babu wannan hadisi maganace irin ta shaqiyyan mutane maqaryata, waxanda basu jin kunyar yi wa Manzon Allah Sallahu Alaihi Wasallam yaye-yayen qarya. Ah! To, idan ba haka ba,ya za’ace a hukunta wa wani mutum xaya xaukar rabin azabar gaba xayan ‘yan wuta kan wani laifi? Wa ma ke iya kimanta rabin azabar ta su? balle Kadubi irin azabar da Allah ya tanadar wa Alu Fir’auna da Alu ma’idata da munafukai da sauran kafiran duniya. Haxa da wadda ya tanadarwa waxanda suka kashe Annabawa ba li ba la, da waxanda suka kashe nagartattun bayi magabata. Al’amarinfa na da matuqar girma.

Na kuma tabbata cewa baka musun kasancewar zunubin waxanda suka kashe halifa Usmanu, ya fi na waxannan da suka kashe Husaini Raliyallahu Anhu girma nesa ba kusaba. To, irin wannan wuce gona da iri a cikin sha’anin Husaini ta wannan fuska, daidai yake da azarvavin Nasibawa da suke raya cewa matsayin Husaini daidai yake dana Harijawa (‘yan tawaye) sa boda haka in an kashe shi an kashe banza. Dalilinsu kuwa a kan haka wai shi ne cewar da Annabi sallallahu Alaihi Wasallam ya yi: duk wanda ya taras da ku qar qashin jagorancin mutun xaya,ya so ya xaixaitaku, to ku sare kansa da takobi, ko xan waye. Muslimu ne ya riwaito hadisn, kai ka ji.

To, amma mu Ahlus-Sunnah wal jama’a, mun yi Allah wadai da waxannan ra’a yoya guda biyu na ‘yan Shi’a (‘yan Shi’ah) da Nasibawa; ba mu tare da kowannensu.

Mu a wurin mu, Kisan gillar da aka yi wa Husaini zalunci ne, kuma ya yi shahada. Waxanda kuwa sukayi karen aikin mutanen banza ne tantirai. Sannan kuma hadissan da Annabi Sallallahu Alaihi Wasallam ya yi umurni cikinsu da kashe duk wanda ya yi nufin xaixaita al’ummarsa, ba su shafi Husaini ba.

Ah! Ta yaya ko za su shafe shi Raliyallahu Anhu tun da bai yi nufin fasa taron jama’ar Amada ba. Kuma ko da aka kashe shi yana bisa niyyar xayan abubuwa guda uku ne: ko dai ayar de masa ya koma inda yafi to, wato garin su. Ko ya yi sansani a wani wuri, a matsayin mai ribaxi. Ko kuma abashi dama ya yi tozali da Sarkin Musulmi Yazidu.

Ka ga babu xaya daga cikin waxannan abubuwa uku, da za’a iya fahimta a matsayin wariya da yuqurin basa garke, ko da akan tawili. Tafi munji waxanda ya nemi xaya daga cikin waxannan da mamaki daga gare su, adadin su bai tava kara ya karya ba, idan akayi la’akari da gaba xayan jama’ar Yazidu, na gida da dawa. Amma duk da haka, tunda har ya roka, to ya zama wajibi a karva masa.

Babu wani dalilin da zai sa ayi kunnen uwar shegu da shi, a matsayinsa na jikan Manzon Allah. Domin kuwa a hankali da shari’a, ko wanda bai kai darajarsa ba, ya nemi alfarmar xaya daga cikin waxancan abubuwa, ba ya halatta aqi saurarensa, Balle abashi baya ko a tage shi, Daxa balle a aikashi lahira.

Wannan ita ce aqidar Ahlus-Sunnah wal jama’a a kan wannan mas’ala.

Wannan kenan, haka kuma cewar da xan Shi’ar ya yi wai Annabi Sallallahu Alaihi Wasallama ya ce: Hushin Allah da nawa ya tsananta a kan duk wanda ya zubar da jinin wani daga cikin dangina ko ya lava ga zuri’a ta ya cutar da ni. qar ya ce.

Magana ce da babu wan da zai yarda da ta fito daga bakin ma’aiki Sallallahu Alaihi Wasallama sai jahili. Domin kuwa imani da tsoron Allah Subhanahu WaTa’ala ne ya kamata agindaya a matsayin garkuwa da gambun tsari ga ran Hasan da Husaini, da ma kowane musulmi, ba dangantaka ba, ina fatar ka gane. Ah! Yau da wani daga cikin mutanen gidan Annabi Sallallahu Alaihi Wasallama zai aikata wani laifi, da hukuncinsa kisa ne ko datse hannu sai a ce: a’a tunda Ahlul baiti ne shi ya sha! Halas ne bisa haxuwar musulmi, Kai! Wajibi ne a zartar masa da hukuncin yadda za’a zartar wa kowa. Ko banza ingantattar magana ta zo daga shi Annabi Sallallahu Alaihi Wasallama yana cewa: Haqiqa abin da ya halakar da waxanda suke a gabanin ku shi ne kasancewar suna qyale wanda ya yi sata daga cikinsu idan xan wane ne. Amma idan ya-ku-bayi ne, nan take za su zartar masa da haddi. To, ku sani wallahi da yau Fatima ‘yar Muhammadu za ta yi sata (Allah ya tsare) wallahi sai na yan ke hannunta.

Subhanallahi! Allah ya daxa tsira gare ka da aminci.

Ka ga shugaban talikai ya tabbatar maka da cewa da Fatima za ta faxa cikin wannan tarko, ba zai tsamo ta ba don tana ‘yar cikin sa. Ka kuwa san, babu wanda Annabi ke so a cikin iyalansa kamarta.

Kuma idan baka sani ba. A kan haka ne malaman musulunci suka haxu a kan wajabcin jefe Bahashime har lahira, da zai yi zina, yana kuma da aure ko ya tava yi, da kashe shi, da zai kashe wani akan ganganci, babu sixixi ba saxaxa. Ko da kuwa wanda ya kashe bahabashe ne, ko barume ko baturke ko badaulame.

Kuma ai ta tabbata cewa: Annabi Sallalahu Alaihi Wasallama ya ce: Farashin jinanen musulmi xaya ne.

Wato ma’aiki na cewa ne: jinin bahashime baifi na waninsa tsada ba. Matuqar dai sun yi tarayya a qarqashin lemar xiyauci da musulunci. Kuma a kan haka ne gaba xayan al’ummar musulunci ta sandare. Ka ga kenan hukuncin da za’a zartar wa wanda ya zubar da jinin bahashime shi za’a zartar wa wanda ya zubar da na wanda ba shi ba, matuqar dai ba da alhakinsu ba.

To, idan kuwa haka ne, ka ga ba wanda ya isa, ko xan uban waye. Ya ce mana wai Annabi Sallalahu Alaihi Wasallama ya ware mutanen gidansa da wata daraja, ta tsanantar hushin Allah a kan wanda ya zubar da jininsu. Ai adinin musulunci ba shegantaka ne ba.

Abin da Allah Ta’ala ya haramta shi ne kashe wata rai ba akan haqqi ba. Amma duk wanda za’a kashe a kan wani haqqi na shari’a, ko shi xan waye ko jikan wa, Bahashime ne ko waninsa, ba ruwan Allah balle har hushinsa ya tsananta a kan wanda ya zartar da hukuncin kisan a kansa.

Wanda Allah ke hushi, ya kuma ya la’anci wanda ya kashe shi, tare da tanadin azaba mai girma ga makashi, da yanke masa hukuncin dawwama cikin wutar jahannama, shi ne muminin da aka aika lahira bai ji bai gani ba.

Abin da ke sa jinin mutum ya tsira ko ya halatta a shari’ar musulunci, abu ne da ya kundume bani hashim da wanda ba su ba.

Irin waccan magana ta banza, babu wanda ke jingina ta ga Manzon Allah Sallalahu Alaihi Wasallama sai munafuki. Wanda ke son gurvata tsarkaken ruwan annabcinsa. Idan kuwa har ba munafuki ba ne, to lalle kuwa jahili ne, wanda bai san irin adalcin da Allah Ta’ala ya aiko Muhammadu don tabbatarwa ba.

Cewar da xan Shi’ar ya yi, hushin na Allah da manzon sun haxa da: wanda ya lave ga zuri’ar manzo ya cutar da shi.

To, duk da yake gaba xayan hadisin bai ingantaba. Amma ai ana iya lavewa ga al’ummar Manzon Allah Sallalahu Alaihi Wasallama ko sunnar sa a cutar da shi domin kuwa ko shakka duk wanda ya keta alfarmar waxannan abubuwa biyu, dai dai yake da wanda ya keta ta zuri’arsa, kuma duk cutarwa ce gareshi Sallalahu Alaihi Wasallama yin haka kuwa haramun ne tabbas.


Yüklə 2,75 Mb.

Dostları ilə paylaş:
1   ...   11   12   13   14   15   16   17   18   ...   51




Verilənlər bazası müəlliflik hüququ ilə müdafiə olunur ©muhaz.org 2024
rəhbərliyinə müraciət

gir | qeydiyyatdan keç
    Ana səhifə


yükləyin