Tafarkin sunnah


Wata Sabuwar Tatsuniya Tasu



Yüklə 2,75 Mb.
səhifə19/51
tarix28.10.2017
ölçüsü2,75 Mb.
#17506
1   ...   15   16   17   18   19   20   21   22   ...   51

2.22 Wata Sabuwar Tatsuniya Tasu

Shi kuwa hadisin da xan Shi’ar ya kawo. Inda ya ce: Allah Ta’ala ya halicci wani mala’ika a cikin siffar Ali Raliyallahu Anhu don ya kashe wa wasu manyan mala’iku (Jibrilu, Israfilu da Mika’ilu) kwandar shauqin da suke yi wa Ali Raliyallahu Anhu wanda ya zamar masu kamar ciwo, sanadiyar jin irin falalolin da yake dasu. Da cewar da Annabi Sallallahu Alaihi Wasallama ya yi ma shi: Baka fatar matsayin ka a wurina ya zama kamar matsayin Haruna a wurin Musa?

Ka ga wannan magana, tatsuniya ce da jahilai irin waxanda ko qarya ta gagare su iyawa kan yi. Domin kuwa babu wani musulmin kirki wanda bai san cewa mi’irajin da a kayi da Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama, anyi shi ne ba, tun ana Makka; kafin ayi hijra zuwa Madina kamar yadda Allah Ta’ala ya ce: Tsarki ya tabbata ga wanda ya yi tafiyar dare da bawan sa, da dare daga masallaci mai alfarma zuwa ga masallaci mai nisa,wanda muka sanya albarka a gefensa domin mu nuna masa daga ayoyinmu. Lalle shi, shi ne maiji, mai gani (17:1)

Ka ga kenan daga masallacin Makka ne aka yi wannan tafiya.

Haka kuma Allah Ta’ala ya ce: Ina rantsuwa da tauraron, a lokacin da ya faru. Ma’bucin ku bai vata ba kuma bai qetare haddi ba. Kuma baya yin magana daga son zuciyar sa.(maganarsa) ba ta zamo ba, face wahayi ne da ake aikowa (53:1-4). Har zuwa inda ya ce: Shin za kuyi masa musu a kan abin da ya gani? Kuma lalle ya ganshi, haqiqatan, a wani lokacin saukarsa. A wurin da magaryar tukewa take(53:12-14). Har kuma zuwa inda ya ce: Shi kunga lata da uzza? (53:19)

Ka ga duk waxannan ayoyi a Makka suka sabka bisa haxuwar kan malamai da almajiran sanin makamar Alqur’ani da tafsirinsa.

Kuma ka ga cewar da ya yi manzon ya ce wa Ali: Ba ka fatar matsayinka a wurina ya zama kamar matsayin Haruna a wurin Musa? Magana ce da manzon yayi alokacin yaqin Tabuka; yaqi na qarshe a shekara ta tara bayan hijira. Shi kuwa mi’iraji in baka mantaba kafin hijira aka yishi. To ta yaya za’a ce mala’iku sunji wannan magana shekaru da yawa kafinta. Ko sun san gaibi ne?
2.23 Bajini Xan Bajini Xan’uwan Bajini

Haka kuma daga cikin irin waxannan hadisai na wofi, da xan Shi’ar ke tuma goda dasu, akwai wanda ya ce wai: An samo daga xan Abbas, wanda wai ya ce: Watarana Al-Musdafa Sallallahu Alaihi Wasallama na cikin nishaxi, sai muka ji yaqata ya ce; Ni bajini ne xan bajini kuma xan ‘uwan bajini.

Kuma wai sai xan Abbas xin ya ce: Annabi na nufin shi ne bajinin Larabawa, xan bajinin Annabawa; wato Annabi Ibrahim Alaihis Salamu wai saboda Allah ya ce:

ﭧ ﭨ ﭷ ﭸ ﭹ ﭺ ﭻ ﭽ ﭣ ﭤ ﭥ ﭦ ﭧ ﭨ ﭩ ﭪ ﭼ الأنبياء: ٦٠



Munji wani saurayi yana ambatar sa. Ana ce masa Ibrahim (21:60). Xan’uwan nasa kuwa shi ne Ali. Wanda shima wani bajinin ne. Wai kuma wannan magana ta ma’iki itace fassarar abin da Jibrilu ya ce a lokacin yaqin Badar, daidai lokacin da yake kutsa hatson samaniya. Inda ya ce: Duk wani takobi yau idan ba “zul-qifani” ne ba, labari ne. Duk kuma dakaren da ba Ali ba, shi ma labari ne.

To bari ka ji.

Na farko dai, kan malaman hadisi ya haxu a kan cewa wannan hadisi qagagge ne. Kuma kasancewar sa qarya na tabbatar da bayyana ta fuskoki kamar haka:

Fuska ta farko: duk da yake kalmar “al-fata” Balarabiyar kalmar ce wadda aka ce manzon yayi amfani da ita a cikin wannan kirari na nufin “bajini” a babin. Wadda kuma ke nuna “yabo”. Sai dai a harshen al-qur’ani da Hadisi; (sunnah) da abin da harshen Larabci ya al-adanta(?) kalmar bata nufin “yabo” ko “ suka”. A kan yi amfani da ita ne kawai a waxannan wurare da nufin alamta: matashi ko saurayi ko dattijo, ko wani abu mai kama da haka. Domin ai waxanda suka cewa Ibrahim Alaihis Salamu “ al-fata” a cikin wanccan aya, kafirai ne. Ka kuma san ba yabonsa suke nufin yi ba.

Ka ga a nan kalma ta “al-fata” na nufin “saurayi” ko “ matashi”.

Wata fuskar kuma itace: Annabi Sallallahu Alaihi Wasallama yafi qarfin yin alfahari ( kirari) da ka kansa da xan ammin sa.

Kuma ko alama Annabi Sallallahu Alaihi Wasallama bai qulla zumunci da Ali Raliyallahu Anhu ko wani ba. Hadissan dake nuna haka, da waxanda ke nuna qulla zumunci tsakanin Abubakar da Umar duk ka gaggu ne. Abin da dai ya tabbata shi ne, Annabi Sallallahu Alaihi Wasallama ya qulla zumunci ne tsakanin Muhajiruna da Ansar. Amma bai qulla shi tsakanin Muhajiruna da xan’uwansa Muhajiri ba.

Kuma cewa wannan abu ( kirarin) ya faru ne a ranar yaqin Badar, yama fi komai zama qarya.

Kuma. Aliyu bai tava mallakar wani takobi mai suna “zul-qafari” ba. Abin da ya tabbata a tarihi shi ne, shi wannan takobi yana daga cikin takubban Abu Jahil. Wanda ya faxa a cikin ganimar da musulmi suka samu a wurin yaqin na Badar. Ka ga kenan takobin a wannan rana ba mallakar musulmi ba ne. Na kafirai ne. Kamar yadda Ahlu-sunan: Imamu Ahmad, Tirmizi, xan Maja suka riwaito daga xan Abbas cewa: takobin Annabi Sallallahu Alaihi Wasallama na ganawa na abu Jahil (zul-qafari) azaba, ta hanyar yi masa giyavu, idan sukayi karon battar karfe (majaz).

Kuma. Xan Shi’ar ya manta cewa shekarun Annabi na bayan Annabta, shekaru ne na manyanci; ya wuce a ce masa “saurayi” a lokacin, balle ya cewa kansa, tunda ba magori bane shi.
2.24 Son Ali Da Sauran Sahabbai Duk Wajibi Ne

Shi kuwa hadisin da xan Shi’ar ya riwaito daga Abu Zarri, hadisi ne mai gajeren asali (maukit) ; nan zariyarsa ta tuqe ga Abu Zarri xin. Darajar sa ba ta kai ta marfu’i ba (hadisi mai cikakken asali) saboda haka ba a shiga xaka da shi, balle kafa hujja watarana.

Kuma cewa ma an riwaito shi daga Abu Zarri, magana ce da keda xan mirtsi-mirtsi.

To kuma ma duk aje wannan. Ko da hadisin ya inganta, to abin da ya qunsa xin can bai kebanci Ali ba. Domin kuwa son sauran Sahabbai, da suka haxa da: Abubakar da Umar da Usman Raliyallahu Anhu da Ansaru wajibi ne, yadda son Ali Raliyallahu Anhu yake wajibi a kanmu.

Wani abu dake tabbatar da wannan magana tamu shi ne ingantaccen hadisin da ya ce Annabi Sallallahu Alaihi Wasallama ya ce: Son Ansaru shi ne alamar imani. Kamar yadda qin su yake alamar manafucci.

Haka kuma wani ingantaccen hadisi a cikin sahihu Muslim ya ce; Ali Raliyallahu Anhu ya ce: Annabin nan da bashi da malami sai Allah ya yi mini busharar cewa: duk wanda yaso ni mumini ne. Wanda kuma duk ya qini munafuki ne.


2.25 Son Aliyu Bai Isa Shinge

Xan Shi’ar ya ce daga cikin darajojin Ali Raliyallahu Anhu wai akwai hadisin da marubucin littafin: al-fiddausi ya riwaito daga Mu’zu xan Jabalu, wanda ya ce wai: Annabi Sallallahu Alaihi Wasallama ya ce: Son Ali wani kyakkyawan aiki ne mai silke. Wanda mugun aiki ba ya hudawa, balle ya cutar da mai shi. Haka kuma qinsa, wani mugun aiki ne mai sida, wanda ran mai shi bai daxa shi da komai ba.



Martani: Muna tabbatar wa da wannan xan Shi’ar cewa wannan hadisi qarya ne. Kuma wannan littafi na: al-fiddausi cike yake makil da ka gaggun hadisai. Tattare kuwa da kasancewar mawallafinsa; Shirawahi xan Shahradaru ad-Dailami xaya daga cikin mafarauta hadisi da riwayarsa. Hakan bata hana wannan littafi nasa zama maqoshin kolo ba, ta hanyar tarkata duk hadisin da yaci karo dashi a ciki, tare da share isnadinsa, ba kuma tare da kula da kasancewar sa ingantacce ko mai rauni ko qagagge ba. Saboda haka ne ma su gizo da qoqi suka sami ranar shanya jikakken garin su a cikin littafi, barkatai.

Babu wani musulmi na qwarai da zai yarda cewa Annabi Sallallahu Alaihi Wasallama ya furta wannan magana. Domin kuwa sanin kowane son Allah da manzonsa sun fi son Ali falala nesa ba kusa ba. Amma duk da haka ba su hana a kama mai su da laifin mugun aikin daya aikata. Ka ga ashe kenan son Ali baya isa shinge.

‘Yan Shi’ah suna ina, Annabi Sallallahu Alaihi Wasallama kansa a yi wa Abdullahi xan Hammaru xan karan duka, saboda yasha giya, tattare kuwa da shaharar da ya yi da son Allah da manzonsa? Son Allah da Manzonsa kuwa wajibi ne a kan kowane mumini. Amma kuma hakan ba zata hana a kama shi da laifin wani mugun aiki ba; za’a kama shi da shi harma a hukunta shi .

Kuma abu ne sananne ga xaukacin jama’ar musulmi; sani na lalura, a sakamakon kasancewarsu musulmi, cewa duk wanda ya rayu ya kuma mutu yana shirka, kashin sa ya bushe; Allah ba zai gafarta masa ba, ko da kuwa yana lasan dugadugan Ali Raliyallahu Anhu saboda tsananin so da qauna.

Ai ka ga son da mahaifin Ali; wato Abu Xalib, da Shi’ah al-Galiyya ke yi wa Alin bai hana su shiga wuta ba a matsayin kafirai.

A ta kaice wannan aqida kafirci ce bayyananne , irin wanda Allah ke sauraron mai ita idan ya tuba. Kuma haramun ne ga duk wanda ya yi imani da Allah da ranar qarshe ya kudurta haka, balle furta shi.

Wannan kenan. Haka nan kuma cewar da ya yi wai Annabi ya ce: qin Ali wani mugun aiki ne mai sida, wanda wani aiki na mai shi, ba zai amfane shi da komai ba. Magana ce da ke son a kalleta sau biyu.

Ah! Sau biyu mana. Ai ko shakka babu, sai dai kafircin kafirin da yaqi Ali, ya zame masa qarqiya daga shiga Aljannah, ba kin Alin ba. Kamar yadda imanin mai imani zai zame masa sanadin shiga aljannar, ko yana qin Alin kuwa. Don ba shi ne ma’auni ba.

Haka kuma malaman hadisi sun yi itifaqi a kan cewa hadisai biyu da xan Shi’ar ya riwaito daga xan Masa’udu inda ya ce wai Annabi Sallallahu Alaihi Wasallama ya ce: ladar son Alu Muhammadin ta yini xaya ta fi alheri bisa ga ibadar shekara xaya. Kuma wai duk wanda ya mutu a kan sonsu xan aljanna ne.

Da kuma xayan da ya ce a cikin sa: Ni da wannan (Ali) hujjar Allah ne a kan halittar sa. Duk hadisai ne ka gaggu. Domin ai ibadar shekara xaya ba wasa bace; dubi girman imani da sallah biyar kowace rana da azumin watan Ramadana, har na tsawon shekara xaya. Ko a kansu xai aka tsaya. Waxanda saboda girmansu ne kan masulmi ya haxu a kan cewa sun fi qarfin son Alu Muhammadin na tsawon zamani, balle kwana xaya, a lada.

Sannan kuma ai hujjar Allah akan bayinsa , ta riga ta tabbata sakamakon aiko manzanni kawai. Dubi abin da Allah Ta’ala ke cewa:

ﭧ ﭨ ﭷ ﭸ ﭹ ﭺ ﭻ ﭽ ﭾ ﭿ ﮀ ﮁ ﮂ ﮃ ﮄ ﮅ ﮆ ﮇ ﮈﮉ ﮊ ﮋ ﮌ ﮍ ﮎ ﭼ النساء: ١٦٥

Domin kada wata hujja ta kasance ga mutane a kan Allah bayan manzanni (4:165)

Ka ga bayan manzanni Allah bai lava imamai ko waliyyai ko wasunsu ba ko?

Haka kuma nagartattun malamai; ma’abuta ilimi da kishin addini sun haxu a kan cewa, cewar da xan Shi’ar ya yi wai Annabi Sallallahu Alaihi Wasallama ya ce: Da gaba xayan mutane za su haxu suso Ali Raliyallahu Anhu da Allah Subhanahu WaTa’ala ya shafe wuta. qarya ce gangariya. Suka kuma qara tabbatar da cewa da mutane za su haxu suso Alin baki xaya. Hakan ba zata amfane su da komai ba ranar qiyama. Matukar ba su yi imani da Allah da mala’ikunsa da littafansa da manzaninsa da Ranar lahira, suka kuma aikata aikin qwarai ba.

Da zarar haka ta samu daga gare su, to aljanna gare su har quryar xaki, ko dako basu tava sanin ko waye Ali ba, balle su soshi ko su qishi.


2.26 Hadisan Gizo Da Qoqi

Kusan mafi yawan hadisan da wannan xan Shi’ar yake shawagi dasu, a sararin samaniyar qoqarin tabbatar da fifikon Ali Raliyallahu Anhu hadisai ne na gizo da qoqi.

Daga cikin waxannan hadisai, akwai wanda xan Shi’ar ya ambaci wani arqawari da Allah ya yi a kan Ali Raliyallahu Anhu. Da cewa shi tutar shiriya ne kuma shugaban sahun masoya Allah (waliyai) kuma wai Ali shi ne abu xaya da Allah ya wajabtawa masu tsoronsa so a matsayin wata xaya-xayan kalma... har dai qarshen hadisin.

To, malamai masana sirrin hadisi da makamar sa sun yi itfaki a kan cewa wannan hadisi qagagge ne. Kuma baya zama ingantacce don kawai mawallafin littafin al:Hilyah ya riwaito shi, ko wani mai kama dashi. Domin tabbataccen abune shi wannan malami ya riwaito hadisai masu yawa a cikin wannan aiki nasa. Waxanda kusan duk masu rauni ne, a kan darajojin, Abubakar da Umar da Usmanu da Ali da wasu waliyai da wasunsu. Kai! Wasunsu ma ka gaggi ne bisa haxuwar malamai. Duk da yake shi da takwarorinsa daga cikin “huffaru” amintattu, ma’abuta hadisi, amintattu ne a karan kansu, a kan duk abin da za su riwaito daga shehunninsu. Illar tare da su shehunan.

Haka ma hadisin Ammaru da na xan Abbas, waxanda xan Shi’ar ya kawo duk na gizo da qoqi ne.
2.27 Sun Mayar Da Sahabbai Dalga

Sahabbai a wurin ‘yan Shi’ah ba kowa bane. Saboda haka suka mayar da su dalga. Ta hanyar kai masu ko wacce irin suka, da zuba masu kowacce irin qazanta kamar salga.

A qoqarin tabbatar da wannan manufane , xan Shi’ar ya ce wai: Jumhurun malamai sun riwaito abubuwan kunya da basu kida yuwa a kan Sahabbai. Wanda har wani marubuci mai suna al-qalibi ya wallafa littafi mai suna. Ababen kunyar Sahabbai wai. Amma bai ambaci wani abun kunya ko xaya ba, ko wata naqasa dangane da Ahlul-Baiti a cikin littafin.

To ka ga irin wannan xanyen aiki na ‘yan Shi’ah abin yayi hattara ne da.



Martani: To, kafin mu shiga walwale wannan qullin maqodo filla - filla, muna tabbatar wa xan Shi’ar da cewa, duk wani abu da wani zai ga la’arin Sahabban Manzon Allah a kansa, bai kamata a kira shi abin kunya ba. Sai dai wata qila ko qorafi.

Amma daxa ga dalilai na:

Qorafe-qorafen da a kanyi kan Sahabbai nau’i biyu ne:

Ko dai su kasance: 1) qarya zalla. Wato an qaga masu ne; ba su ji basu gani ba. Ko kuma 2) lauje cikin naxi. Wato abubuwan sun faru a cikin nagartattar sura. Amma sai magabata suka sake masu fuska. Ta hanyar rage wasu abubuwa daga cikinsu ,da qara wasu. Ta yadda za su bayyana a matsayin miyagun ayukka ga idon duniya. Waxanda a qarshe za su tsirar da itatuwan suka da zargin waxannan bayin Allah.

To mafi yawan korafe - korafen da ake riwaitowa a kansu, na qarqashin wannan kashi na biyu ne. Kuma za ka taras da cewa, waxanda ke riwaito sun, mutane ne da suka shahara da qarya; kamar su Abu Mukhnif; Lud xan Yahya, da Hisham xan Muhammad as-Sa’ibi al-kalibi, da wasu maqaryata takwarorin su. Kuma ka ga dashi wanna al-kahbin ne xan Shi’ar ya kafa mana hujja. Alhali kuwa limami ne daga cikin limaman qarya a duniyar Shi’ah. Kuma duk abin daya riwaito kan biyo takan mahaifisa ne daga hannun abu Muhnif xin can. Waxanda dukansu biyun ba a shiga xaka da maganarsu.

Nau’i na 3), kuma daga cikin waxannan qorafe - qorafe, shi ne, : Tantagaryar gaskiya. Wato abubuwa waxanda tabbas Sahabbai sun aikatasu a matsayinsu na ‘yan adamu. Amma kuma suna da uzuri a kan haka. Wanda la’akari dashi, ke xauke ayyukan daga zama tantagaryar zunubi, zuwa matsayin ijtihadi. Irin wanda mai shi ke samon lada biyu idan ya yi muwafaka. Yake kuma samun xaya idan yayi kuskure.

To gaba xayan abin da ya inganta, daga cikin qorafe - qorafen, na qarqashin wannan inuwa ne.

Kuma duk ma qorafin da aka qaddara wa wani tantagaryar zunubi, za ka taras ba wata alka da yake iya yi wa Sahabban, idan akayi la’akari da darajojinsu da kyawawan ayukkansu, da kasancewarsu ‘yan aljanna tun duniya. Domin ba garesu kawai ba. Ga kowa ma, tantagaryar zunubai kan zama labari a lahira, a yayin da mai su ya sami xaya daga cikin waxannan lanbobi ko masu kama dasu, tun duniya:



  1. Tubar wankan tsarki. Kamar yadda ta tabbata daga bakin malaman Shi’ah ‘yan-sha-biyu cewa, waxannan Sahabbai sun yi irin wannan tuba ga Allah Subhanahu WaTa’ala a kan duk kurakuran da suka aikata.

  2. Kyawawan ayyuka. Kamar yadda ta tabbata cewa kyawawan ayyuka na wanke zunubai. Kuma Allah Ta’ala ya ce: Idan kuka nisanci manyan abubuwan da ake hanaku aikatawa, to, za mu kankare muna nan ayukanku daga gare ku (4:31)

  3. Manyan musibu. Waxanda ta tabbata suna kankare zunubai

  4. Addu’ar muminai waka junansu. Da kuma ceton da Allah zai ba su damar yi wa junan nasu gobe qiyama.

Kai! Babu wani abu dake zaman dalilin kwaranyewa, wani daga cikin al’ummar nan wani zunubi ko wata azaba, face waxannan Sahabbai sun fi cancanci da shi a kan kowa. Sune kuma ya kamata su zama sha yabon masu yabo, varin varin masu vari kafin kowa.

Bayan xan Shi’ar ya qare waccan dunqulallar maganar, sai kuma ya ce: Al-Kalbi ya ambaci waxancan abubuwa na kunya masu yawa. Bari in xan gutsuro maku kaxan daga ciki. Sai ya ce: An riwaito cewa watarana Abubakar Raliyallahu Anhu na kan munbari sai ya ce: haqiqa Annabi ya kasance yana samun gudunmuwar wahayi a kan duk abin da yake aikatawa. Ni kuwa shexan na iya dagula mani lisafi. Ina fatar za ku mara mani baya a duk lokacin da kuka ga na kama hanya shararra. Za ku kuma kevo ni, idan na kama daji.

Ka ji qarshen maganar Siddiqu.`

To sai xan Shi’ar ya ce: To ta yaya za’a yarda da shugabancin wanda ke da buqata da taimakon talakawa, alhali kuma su suna da bukata da nasa taimakon? An yi haihuwar guzuma kenan.


Martani:

Ai wannan hadisi aya ne, dake tabbatarwa da nuna xaya daga cikin manyan darajojin Abubakar Sidiku Raliyallahu Anhu. Kuma ba wani abin da ke nuna kasancewarsa wanda ba ya nufin homa da varna a bayan qasa kamar wannan magana da ya yi. Dama kuma bai nemi shugabancin ba, bai kuma tava sha’awar zalunci ba. Bai kuma da nufin yin mulkin mallaka a halifancinsa. Saboda haka ya kama hannun mutane ya haxa dana Allah da manzonsa; ya ce subi su.

Tabbas abida yake nufi kenan. Don fassarar waxancan kalmomi da ya yi amfani dasu itace: idan kun ga na tsayu a kan xa’a ga Allah, to ku agaza mani a kan haka. Idan ko kun ga na bar tafarkin gaskiya to (don Allah) ku ceto ni. Kamar yadda wata magana daya tava yi ke tabbatarwa, in da ya ce: kubi ni matuqar na bi Allah, idan kuma nayi kuskure daga yi masa xa’a ku yi ta kanku.

Allahu Akbar!!! Ka ji baraden musulunci.

Kuma cewar da halifan yayi, shexan na iya dagula masa lissafi, magana ce da bai kamata mai hankali da ilimi ya yi wa kallo biyu ba. Saboda abu ne dake iya faruwa ga kowane xan Adam. Don babu wanda Allah bai sawa abokin zama daga cikin mala’iku da shexanun (aljannu) kowane xaya-xaya ba.

Ka ga a nan Siddiqu na sone ya faxawa duniya tun da asuba, cewa fa shi ba ma’asumi ne kamar Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama ba. Wannan kuma gaskiya ne.

Wannan kenan. Ita kuma cewar da xan Shi’ar ya yi wai: ya za’a amince da shugabancin wanda keda bukata da agajin talakawansa don ya dawo ga hanya. Maganace irinta waxanda suka jahilci tantagar yar manufa da ma’anar shugabanci (Imama)

Ai a tsarin musulunci shugaba ba Ubangijin talakawansa ne ba, balle ya kasance baya da bukata dasu. Kuma ba Manzon Allah bane, zuwa gare su, balle ya zama hamzatul-wasali tsakanin suda Allah. A’a, ko alama. Shi, shugaba ne, kuma abokin tarayyar talakawa cikin duk abin da zai tabbatar da nagartar rayuwar su ta addini da duniya; dolene su yi masanyar hannuwan gudunmuwar alheri a tsakaninsu. Wato ya zama kamar dai madugun tafiya, wanda ayari zaibi baki alaikum, idan ya kama lafiyayyar hanya. Su kuma faxakar da shi idan yaci tuwon gigi; su dawo dashi a kan hanya madaidaiciya. A qarshe kuma idan wani abu; mutum ko dabba ya kawo masu hari, to sai ayi ba babba ba yaro; dashi dasu duk sun tuve ayi ta katakka. Idan an qare lafiya, ya koma ya nax a rawaninsa ya fike amawali ya buxe mahuta.

Amma kuma tattare da haka akwai bukatar duk wanda zai shugabanci jama’a ya kasance mafificinsu kamala a ilimi da kudura da jinqai, don ya zama masu rariya matatar komai.
2.28 Tawali’u Ne Ba Rashin Cancanta Ba

Daga cikin abubuwan da xan Shi’ar ke sukar lamarin Sahabi Abubakar Raliyallahu Anhu dashi akwai cewar da ya yi wai, Abubakar Raliyallahu Anhu ya yiqoqarin butsewa a lokacin da aka zave shi matsayin halifa, saboda sanin da ya yi cewa bai cancanci muqamin ba; Don ba haqqin sane ba. Wai sai ya ce: (Don Allah) ku fita ba tuna, tunda ga Aliyu na raye, ai ba ni da wani matsayi. Balle a dage a kan sai Ni.

Daga nan ne xan Shi’ar ya ce: Idan dai har Abubakar na jin cewa ya cancanci wannan shugabanci, kuma haqqinsa ne, to qoqarin bultsewar nan da ya yi savo ne. Idan kuwa har kamuyamiya ce zai faxa wa; kamar yadda shi da kansa ya hango haka, har yayi qoqarin bultsewa. Kuma tattare da haka ya ci gaba da riqe mukamin, to abin kunya ya tabbata a kansa.

Lalle, kai kasan kafiri dai bai san kunya ba!!!



Martani: Babu inda wannan magana ta fito a cikin littafan hadisi ingantattu. Babu kuma mai cewa ga isnadinta. Saboda haka qarya ce kawai.

Abubakar Raliyallahu Anhu baice: “Tun da Aliyu na raye---ba”) Ingantattar maganar da dai ta tabbata itace, cewar da ya yi a ranar da sukayi taro a “saqifa”: ya ku jama’a ina kiranku ga ku naxa xaya daga cikin: Umar xan khaxxabi da Abu Ubaidatu xan Al-Jarrar . yana qare faxar haka sai Umar ya yi kazazam ya ce: A’ah! Kai dai za’a naxa. Ko banza mun daxe da gamsuwa da zaman ka shugaba a gare mu, kuma mutum mafi alheri da soyuwa a wurin Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama kuma wallahi da za’a rataye ni a sare kai na, in tafi wurin Allah ina tsarkakakke, ya fi soyuwa gareni. Bisa ga a naxani shugaban mutanen da kake cikinsu.

Kaji iyakar abin da ya gudana a wannan taro ta wannan haujin.

To kuma tafi naji. Muqaddara cewa Abubakar xin Raliyallahu Anhu ya ce: “kuma Aliyu na raye” kamar yadda xan Shi’ar ke son ya ce. To ai wannan shedar da Umar ya bayar a kansa ta isa ta cancantar da shi ga halifancin fiye da kowa. Haka kuwa akayi, ka gani ko?!

To kuma mu dawo ga cewar da xan Shi’ar ya yi wai: Da Abubakar na jin halifancin haqqinsa ne, ya kuma nemi ya butse, to ya aikata savo.

To abin da za mu cewa a nan shi ne: Mu qaddara cewa Abubakar xin Raliyallahu Anhu ya nemi ya butse. Hakan bata nuna rashin kasancewar ta haqqi gare shi. Domin kuwa zaman abu haqqi ga mutum na nufin ko dai 1) halas ne gare shi. Ko kuma 2) Wajibi. Babu kuwa inda barin halas don kunya (fillanci) ya zama laifi, balle a ce. Na farko kenan. Kuma ka ga zancen aikata sabo bai taso ba.

Na biyu kuma, halifanci na zama wajibi a kansa, idan sauran Sahabban suka qi janye naxin da suka yi masa balle su naxa wani. Rashin yin haka kuwa da suka yi ya tabbatar da shi a haka.

Kuma ai ka ga da yawa mutum ka qulla ciniki ko jinga, ta yadda wanzar da su zai wajaba, amma kuma ya iya fasawa. Kamar haka ne. Abu ne mai yiwuwa ya kasance Abubakar ya nemi ya butsewa shugabancin ne saboda tawali’u da irin nauye - nauyen dake kansa. Tattare da kasancewar babu wanda yafi shi cancanta da ita a wurin dama wani wuri. Kuma ai tawali’u bai tava kayar da haqqi ba.


2.29 Abu Ne Daga Allah

Xan Shi’ar ya ci gaba da cewa wai: Umar ya ce: Mubaya’ar da suka yi wa Abubakar Raliyallahu Anhu a matsayin halifa baqar qaddara ce. Wadda ba don da Allah ya tsare ba. Da hakan ta saukar da wata alloba. Saboda haka, duk wanda ya sake irin wannan gigi ku kashe shi.

Xan Shi’ar yaci ka da cewa: Ka ga inda shugabancin Abubakar ba baqar qaddara ce ba, Umar bai cancantarwa wanda ya sake irinta da kisa. Idan kuwa ya yi haka to abin kunya ya tabbata gare shi. A yayin da tabbatar zamanta baqar qaddarar, da rashin cancantar Abubakar da ita, zai tabbatar da abin kunya a kansu su biyu.

Kai ka ji magana kamar ta mai ilimi da imani.



Martani: Za mu kawo wa mai karatu cikakken martanin wannan hadisin, mu kuma fexe shi har wutsiya. Saboda gaskiya ne abu ya faru, amma mutumin naku (Xan Shi’ar) ya yi halin nasa.....

Kafin haka ga dai ingantaccen abin da Umar xin Raliyallahu Anhu ya ce a cikin hadisin: kada in qara jin wani daga cikinku yayi varin bakin cewa ba Abubakar ne aka shirya yi wa bai’a ba, illa dai abune daga Allah. Eh! Ko shakka babu haka ne. Kuma sai ga shi Allah ya sa ta zama alheri ga mutane. Don babu wanda mutane ke goyon bayansa daga cikinsu kamar Abubakar.

Wato yana bayyana irin yadda mutane suka yi ta yin tururuwa suna kai caffa ga Abubakar Raliyallahu Anhu ba tare da wata inda - inda ba.

Babu wani abin mamaki ko kaxan a cikin haka. Domin kuwa Sahabbai sun riga sun sallama wa Abubakar fai da voye, tun Annabi na raye. Musamman ganin irin yadda Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama ke gabatar da shi ga al’amurran zahiri da baxini. Saboda haka Sahabbai a wannan lokaci ba su bukatar wata shawara ko jinkiri kafin suyi wasa bai’ar. Savanin wani, wanda ba shi ba, da ba ta yiwuwa (halatta) a yi masa mubaya’a haka nan ba tare da an xanyi wani batun zucci ba, da ‘yan shawarwari.

Saboda haka duk wanda ya yi wa Abubakar mubaya’a, a wannan lokaci, ba tare da wata ida-inda ba, daidai yake. Saboda ai nuni ya ishi mai hankali.


Yüklə 2,75 Mb.

Dostları ilə paylaş:
1   ...   15   16   17   18   19   20   21   22   ...   51




Verilənlər bazası müəlliflik hüququ ilə müdafiə olunur ©muhaz.org 2024
rəhbərliyinə müraciət

gir | qeydiyyatdan keç
    Ana səhifə


yükləyin