Tafarkin sunnah


Halifa Abubakar Bai Damu Ba



Yüklə 2,75 Mb.
səhifə20/51
tarix28.10.2017
ölçüsü2,75 Mb.
#17506
1   ...   16   17   18   19   20   21   22   23   ...   51

2.30 Halifa Abubakar Bai Damu Ba

Xan Shi’ar ya ci gaba da cewa wai: A lokacin da ajalin Abubakar Raliyallahu Anhu ya qaraso, halifan yayi nadamar karvar halifancin da ya yi, inda ya ce: kaicona! Na so ace na samu damar tambayar Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama; shin ko Ansaru nada wani haqqi a cikin wannan al’amari( halifanci)?

Xan Shi’ar ya kammala da cewa wai: Wannan shi ke nuna cewa ko da Abubakar ya karvi halifacin yana cike da kokwanton cancantarsa da shi; yana kuma jin naxa shi da aka yi kuskure ne.

Martani: Wannan magana qarya ce xan Shi’ar ya yi wa Abubakar; ko ban za bai ambaci isnadin ta ba. Kuma sannen abune cewa wajibi ne ga duk wanda ya kafa hujja da wata riwaya, ya kawo isnadinta matukar yana son hujjarsa ta zama karvavva. Balle wanda ke son tabbatarwa duniyar musulmi da cancantar keta alfarmar Sahabbai. Sai kuma ya buge ga kafa hujja da wata shegiyar hikiya; maras uba balle kaka da kakanni.

Sannan kuma muna tabbatarwa da xan Shi’ar cewa, da yana da hankali da wayo da bai kawo wannan magana ba. Domin .kuwa tana qaryata iqirarin da suke yi ne, na cewa Annabi Sallallahu Alaihi Wasallama ya bar sallahun Ali ya gaje shi, a nassance. Ka ga kenan da akwai wancan nassi da suke tutiya, da Abubakar Raliyallahu Anhu bai nemi sanin ko Ansaru nada wani haqqi cikin al’amarin ba. Wannan idan mun qaddara tabbata da ingancin wannan shegiyar riwaya keNan.

Wannan magana tabbas ce.
2.31 Tsananin Tsoron Allah Ne

Xan Shi’ar ya ci gaba da cewa wai: wani abu kuma dake nuna cewa Abubakar Raliyallahu Anhu ba kowa bane shi ne cewar da ya yi lokacin daya kai gargara : kaicona! Ina ma ace mahaifiyata bata haifeni ba, ina ma ace buntu aka yoni a yi dawun kungu da ni.

Xan Shi’ar ya ce: kaji abin da Abubakar ya ce: Tattare da kuma kasancewar Ahlus-Sunnah sun riwaito daga Annabi Sallallahu Alaihi Wasallama wanda ya ce: babu wanda zai kai gargara daga cikin mutane face Allah ya nuna masa mazauninsa na aljanna da wuta.

Martani: Cewa halifan ya faxi wannan magana a wannan lokaci abu ne ba a tava ji ba. Saboda haka ko shakka babu wannan ba gaskiya ba ne.

Amma dai ya inganta cewa, nana Aisha Raliyallahu Anhu tazo wurinsa. Yana gargara, tana mai maita wani baitin waqa dake cewa:

Wadata ba tada wani amfani ga mutum,

Idan qirjinsa ya buwayi numfashinsa zuwa,

Ya dawo yana gargara a maqogwaro.

Tana faxar haka sai halifan Raliyallahu Anhu ya kware fuskarsa ya ce: bari wannan magana kamata yayi ki ce: Kuma mayen mutuwa yaje da gaskiya. Wannan shi ne abin da ya kasance daga gareshi kana bijirewa (50:19)

Wannan alokacin da ya kai gargara kenan. Amma alokacin daya ke lafi yayye, an tava jin yana cewa: kaicona! Ina ma a ce mahaifiyata bata haife ni ba. Wannan kuwa tsananin tsoron Allah ne, in har ta tabbata ya ce hakan.

Kuma irin wannan kalami dake nuna tsoron Allah mai shi, ba Abubakar Raliyallahu Anhu ne farau ba. An riwaito mutanen kirki da dama, sun furta irin haka, saboda tuna irin tashin hankali da firgita da ranar tashin qiyama ta qunsa. Har wani daga cikinsu ya ce: Da za’a bani zavi, tsakanin in mutu ayi min hisabi, tare da lamanar shiga aljanna, ko a mayar dani turxa? Dana zama turxa.

Imamu Ahmad ma ya riwaito cewa Abu Zarri ya tava cewa: Wallahi na so ace ni wata itaciya ce da ake taunawa a furzar.
2.32 Ja Da Baya Ba Tsoro Ba

Xan Shi’ar ya ci gaba da cewa: Abubakar Raliyallahu Anhu ya kuma ce: Kaicona dana sani dana marawa xayan mutanen nan biyu baya ( Umaru xan Haxxabi da Abu Ubaidat xan al-Jarraru) a ranar taron sa’idata, ya zama shugaba. Ni kuma inzama wazirinsa.

Xan Shi’ar ya ce: To ka ga wannan magana, tana tabbatar da cewa Abubakar bai cancanci halifancin ba. Tunda gashi; da kansa yana da ya sani; da bai karva ba.

Martani: A hankalce, wannan magana, idan ma har ta tabbata cewa Abubakar xin yayi ta. To tana kawai nuna cewa ba Ali Raliyallahu Anhu ne ya cancanci halifanci ba. Kuma ya faxe tane, shi abubakar Raliyallahu Anhu xin, saboda tsoron kada alfarmar halifancin ta tozarta kuma ko da Allah zai kaddari haka, to shi dai ya fi son haka ta kasance hannun wani ba shi ba. Wannan kuma na nuna irin yadda ya san girman shugabancin. Kuma wannan abu da ya yi, jada baya ne ba tsoro ba.

Wato ya fi son ko da zai kasance da hannu a cikin shugabancin, to kada ya wuce na wazirci. Ta yadda nauyin ba zai tattara a kansa ba. Kuma haka baya nuna wani tsoro ko kasawa. Domin kuwa qarshen ta dai nauyi kansa ya qare.

Kuma ka ga inda nassin halifancin Aliyu Raliyallahu Anhu ya inganta, Abubakar Raliyallahu Anhu ba zai kudurta marawa waxancan mazajen baya ba. Don yin haka tare da sanin waccan masaniya tozarta alfarmar halifancin ne. Kuma kenan shi zai kasance wazirin halifa mai shigar kutse. Wato ya sayarda lahirarsa kenan, saboda duniyar waninsa ta gyaru.

Ka kuwa san ba irin Abubakar Raliyallahu Anhu ba. Duk wanda ke tsoron Allah, yake kuma fatar gamawa lafiya ba zai yi haka ba.


2.33 Wani Jihadin ne ya Tsayar Da Siddiqu

Wani qoqarin kashe isa, da xan Shi’ar yayi ga Siddiqu, shi ne cewar da ya yi wai Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama ya ce, watarana yana jinyar ajali. Yayi yana maimaitawa: ku tabbata da ganin rundunar Usamatu ta xaga. Kuma Allah ya la’anci duk wanda ya bari jirgin wannan rundunar ya bar shi tasha.

Kuma wai a wannan lokacin halifofin can uku na kafin Ali Raliyallahu Anhu na tare da Manzon Amma wai qarshenta Abubakar ya hana Umar Raliyallahu Anhu halartar yaqin.

Martani: Gaba xayan masana tarihin musulunci da mazajensa, sun yi ittifaqi a kan cewa wannan magana qarya ce. Kuma babu wani daga cikin ma’abuta ilimi da ya riwaito cewa Abubakar da Usmanu Raliyallahu Anhu na daga cikin waxanda Manzo ya umarta da fita tare da rundunar Usamatu. Abin da dai aka riwaito shi ne ya umarci Umar da yin haka.

To, yama kamata duk mai hankali ya tambayi kansa cewa: yaya za a yi Annabi Sallallahu Alaihi Wasallama ya tura Abubakar xin Raliyallahu Anhu tare da waccan runduna ta Usama, Alhali ya riga ya xaura masa nauyin ba musulmi sallah. Matuqar shi ba zai iya ba saboda rashin lafiyar da yake fama da ita?! Kuma ingantattun riwayoyi mutawatirai sun tabbatar da cewa sai da manzon ya share kwana goma sha biyu kwance yana jinya. Bai kuma sa wani Sahabi bayar da sallar ba, baya ga AbubakarRaliyallahu Anhu.

Ka ga kenan ba wai sallah xaya ce ko biyu, ko ta yini xaya ko biyu ba, Abubakar Raliyallahu Anhu ya waqilci Annabi Sallallahu Alaihi Wasallama bayarwa balle a zaci yiwuwar faruwar wannan dama lissafin da ‘yan Shi’ah ke qoqarin haifarwa. Har ma suna qarawa da cewa; wai ‘yarsa ce Aisha, don dai hilqon tsiya ta tura mahaifin nata ga bayar da sallar; Annabi bai ji bai gani ba.

To ba haka al’amarin ya kasance ba. Manzo ne da kansa ya hore shi da hakan. Kuma tsawon kwanukan jinyar sa.

Ko ka gane. Gaba xayan mutane sun yi ittifaqi a kan cewa tsawon kwanakin da Annabi Sallallahu Alaihi Wasallama yayi yana jinya, Manzon bai samu fitowa limanci ba. Babu kuma wanda ke waqiltarsa a kan haka sai Abubakar Raliyallahu Anhu kuma ya share tsawon kwanaki yana wannan waqilci. Lokaci da malamai suka kimanta mafi qaramcin sallar da Siddiqu ya jagoranta a cikinsa da sallah goma ce; sallar isha’i ta daren Jumu’a. Aka wayi gari kuma ya jagoranci juma’a, tare da yin khuxubar ta.

Wannan shi ne abin da ingantattun hadisan mutawatirai suka tabbatar:

Haka kuma Siddiqu Ya ci gaba da ba musulmi sallah, bayan wannan salla ta jumu’a, har safiyar ranar litinin. Ranar da yana cikin limancin sallar subahi dinta Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama ya yaye labulensa, yayo dogon haske; ya dubi tsayuwar sahun almajiran da ya yaye, a jami’ar farko ta musulunci, suna koyi da jami’insu Siddiqu.

A lokacin da Sahabbai suka ji a jikinsu cewa ana kallon su. Suka kuma daga kai suka ga Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama kaxan ya rage hankalin su ya rabu biyu. Shi kuma ma’aiki daya fahimci haka sai ya saki labulen.

Wannan shi ne gani na qarshe da suka yi wa Manzon, yana raye hantsi na gab da qarewa a wannan rana ya ce ga garinku nan.
2.34 Ba Rashin Yarda Ba Ne

Xan Shi’ar ya ci gaba da cewa kuma wai: Annabi Sallallahu Alaihi Wasallama bai tava wakilta Abubakar ba a kan wani al’amari, tsawon ra yuwarsa. A maimakon haka ma sai dai ya shugabantar da Umar xan Asi a kansa, wani lokaci. Wani lokacin kuma yasa shi qarqashin jagorancin Usama. Qarewa da qarau ma, ko lokacin da Manzon ya tura shi isar da saqon surar Bara’a,ba afi kwana uku ba, Allah ya yi wa manzon wahayi da ya karvi saqon daga gare shi ya ba wani (Ali RA). Wai haka kuma aka yi.

Xan Shi’ar ya kammala da cewa wai: to ya za a yi mai hankali ya yarda da shugabancin wanda Annabi Sallallahu Alaihi Wasallama bai yarda da shi ba. Kuma ma har Allah da kansa yayi horo da dakatar da shi daga isar da saqon ayoyi goma kacal daga cikinsurar Bara’a? Wai ya za a yi mai hankali ya yarda da irin wannan mutum a matsayin shugaba?!

Martani: Ko shakka babu wannan magana qarya ce feqaqqa. Domin masana tarihin musulunci, da malaman tafsiri, dana sira, da na hadisai da fikhu, da wasunsu duk sun tabbatar da cewa Abubakar Raliyallahu Anhu ne ya waqilci Annabi Sallallahu Alaihi Wasallama a hajjin sheqara ta tara; hajji na farko a tarihin musulunci, wanda musulmi sukayi daga birnin Madina. Idan a kwai wani, hajji da za’a ce musulmi sunyi kafin wannan, sai fa wanda suka yi bayan anci garin Makka da yaqi nan take, a qarqashin jagorancin Asyad xan Abilt-Asi xan Umayyata, mutumin da Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama ya shugabantar a kan mutanen Makka, bayan wannan nasara. Wannan hajji da aka yi a qarqashin jagorancin wannan Sahabi anyi shi ne a cikin shekara ta takwas. Shekara na dawowa kuma sai Annabi Sallallahu Alaihi Wasallama ya tura Abubakar Raliyallahu Anhu bayan sun dawo daga yaqin Tabuka, don ya jagorancin hajjin wannan shekara. Ya kuma Umarce shi da shedawa kafiran Makka cewa: daga wannan shekara an haramta wa da wani mushriki aikin hajji, balle xawafi uryan.

Ta kuma tabbata cewa babu wani daga cikin Sahabbai da Manzon Allah ya tava naxawa irin wannan waqilci sai Abubakar Raliyallahu Anhu ka ga wannan abin godiya ne ga Allah. Wani abin ma shi ne, Ali Raliyallahu Anhu na cikin waxanda Abubakar xin Raliyallahu Anhu ya jagoranta a lokacin. Wanda ma a lokacin da ya isa Makka, sai Abubakar Raliyallahu Anhu ya tambaye shi: kazo ne a matsayin shugaba ko talakka? Shi kuwa ya ce: A‘a na zone a matsayin talakka.

Haka wannan aikin hajjin ya guda na; Aliyu na sallah bayan Abubakar Raliyallahu Anhu tare da sauran musulmi, ya na kuma sauraron umurninsa kamar yadda kowa ke saurare; babu wani abu da musulmi suka yi wa Abubakar Raliyallahu Anhu a wannan lokaci face ka ji amon muryar Ali Raliyallahu Anhu a ciki.

Haka kuma Abubakar Raliyallahu Anhu ne mutum xaya kwal daga cikin Sahabbai , wanda Annabi Sallallahu Alaihi Wasallama ya waqilta ya riqa bawa musulmi sallah tsawon kwanakin jinyarsa ta ajali.

Ka ga waxannan waqilce- waqilce biyu da Abubakar Raliyallahu Anhu ya yi wa manzo, darajoji ne guda biyu daya kevanta dasu. Savanin irin waqilcin da wasu Sahabbai suke yi masa; irin su Ali Raliyallahu Anhu da wasunsa; Babu wani nau’i na waqilci da Ali Raliyallahu Anhu ya yi wa manzon, face wasu Sahabbai sun yi masa irinsa ko wanda ya fishi.

Wannan kenan. Haka nan kuma Annabi Sallallahu Alaihi Wasallama bai tava shugabantar da Usamatu ko Amir xan Asi a kan abubakar ba Raliyallahu Anhu a matsayin waqillai. Nagartattun malamai sun yi itfaqi a kan haka.

Ita kuwa qissar jagorancin Amir xan Asi ga Abubakar da sauran Sahabbai Raliyallahu Anhu Xan Shi’ar yasa son zuciya a ciki.

Yadda al’amarin ya faru a haqiqa shi ne: Watarana ce Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama ya tura Amru xin ya jagoranci yaqin zatis- salasilu, wanda za a yi da Bani uzurata; kawunnan shi Amru xin. Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama ya yi haka ne don wataqila, hakan ta zama sanadiyar musuluntarsu, ganin xansu gaba-gaba.

Tafiyar su keda wuya kuma sai Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama yayi shawarar qara kabrin jagorancin rundunar. A inda ya tura Abubakar da Ubaidatu harma da Umar Raliyallahu Anhu da wasu Sahabbai daga cikin Muhajiruna. Ya kuma yi masu gargaxin cewa: ku haxa kai dashi kada ku bari a ji ku.

Bayan sun isa, Ubaidatu madugun wannan ayari na biyu ya cewa Amru: Manzon Allah ya turomune mu kama muku wannan daga. Saboda haka idan lokacin sAllah ya yi, sai kowanenmu; ni da kai, ya jagaranci rundunarsa Salla. Don gashin kanmu muke ci. Sai Amru ya ce: A’a, ashe ba cewa kayi manzo ya turoku ne ku kama mana daga ba? Ya ce : Eh, haka ne.

Sai Amru ya ce: To ai, ba batun cin gashin kai kenan za ku yi Sallah ne a bayana. Sai Ubaidatu, ganin irin yadda Amru ya kafe, ya ce: To ba komai, da ma Annabi Sallallahu Alaihi Wasallama ya umarce ni da cewa, kada inyarda ajimu da kai. Nan take Abubakar ya qara daddale wannan magana ta haxa kai tare da qarawa Ubaidatu qwarin gwiwa a kanta. Wannan ra’ayi kuwa na Abubakar shi ne mafi dacewa.

Daga nan sai suka ci gaba da Sallolin su bayan Amru a matsayin liman. Amma kuma kowa yasan cewa darajarsa ba ta kai tasu ba.

Amma cewar da xan Shi’ar ya yi wai Annabi Sallallahu Alaihi Wasallama ya karve isar da saqon suratul bara’a daga hannun Abubakar Raliyallahu Anhu bayan kwana ukku, wai saboda rashin yarda da aminci. Kuma wai ma Allah Subhanahu WaTa’ala ya yi masa wahayi da hakan.

Wannan magana ko shakka babu qarya ce, da kowa ya san qarya ce. Amma kuma babu mai musun cewa xauke saqon waccan sura (ayoyi) daga hannun abubakar zuwa na Ali Raliyallahu Anhu umurni ne daga Allah, amma ba rashin yarda ba ne. Bari kaji yadda abin yake, ya kai jahili uban jahilai.!

Sayyidi Abubakar Raliyallahu Anhu ya waqilci Manzo a hajjin wannan shekara ta tara kamar yadda ya ummarce shi. Bai dawo garin Madina ba sai da anka qare aikin hajji. Ya kuma shelantawa kafiran Makka saqon manzo na shekara; cewa kada mushrikin daya sake aikin hajji daga wannan shekara ,balle yayi xawafi uryan; abin da suka al’adanta. Abubakar ya shelanta wannan saqo kowa naji, sauran Sahabbai na yi masa amshi, har ma da Sayyidina Ali Raliyallahu Anhu a cikinsu.

To dama akwai daddalallin arkawwura tsakanin Annabi Sallallahu Alaihi Wasallama da mushrikan Makka. Dawowarsu Abubakar Raliyallahu Anhu daga wannan aiki na hajji keda wuya, sai nan take Manzon ya sake tayar da Ali Raliyallahu Anhu don ya koma ya walwale waxancan arqawwulla, tunda mushrikan sun kasa tsare alfarmarsu.

Dalilin kuwa da ya sa Manzon, bai bari Abubakar radiyallahu anhu ya qarqare ayyukan wannan shekara na sakwanni a matsayin waqilinsa ba shi ne: da ma a al’adar Larabawa babu wanda ya isa a kulla wani arqawari da shi ko ya walwale shi, daga cikin wasu mutane, sai shugabansu ko wani daga cikin danginsa na jini. Saboda haka ne Manzon ya tura Ali Raliyallahu Anhu ba don komai ba; kuma iyakar abin da ya tura shi yayi kenan. Saboda haka ne ma Alin ya kasance yana Salla bayan Abubakar Raliyallahu Anhu yana kuma biyar sawunsa a cikin ayukan hajji kamar yadda sauran musulmi keyi saboda shi Abubakar xin ne waqilin Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama na wannan shekara.
2.35 Siddiqu Ba Jahili Ba Ne

Sai kuma xan Shi’ar ya ci gaba da cewa wai: kuma saboda tsabar jahilci Abubakar ya tava sa aka yanke hannun hagun wani varawo; saboda bai san na dama ne ake yankewa ba.



Martani: ko shakka babu cewa Siddiqu jahili ne, bai san cikin da wajen wannan mas’ala qanqanuwa ba, qarya ce bayyananna. Inda ma har cewa aka yi yana ganin yanke hannun hagun varawo shi ne mafi dacewa, bisa ga na dama. Da maganar tafi xan shiga. Domin kuwa babu inda Alqur’ani ya bayyana cewa lalle ne idan za’a yanke hannun varawo a yanke na dama, balle.

Xan Mas’ud ne, a salon qira’arsa ya tafi a kan yanke hannun dama; ba na hagu ba. Kuma sai kawai daga nan abin ya zama “sunna”. Shi a wurinsa, maimakon a karanta ayar kamar haka: “Faqda’u Aidihima”( ku yanke hannayensu) sai ya karanta ta da: “Faqda’u Aimanahuma” ( ku yanke hannayensu na dama). Ka ga kenan mas’alar ta ijtihadi a salon qira’a ce.

Kuma ma duk aje wannan jerangiya. A wane littafi, ko daga bakin waye xan Shi’ar ya naqalto cewa, Abubakar Raliyallahu Anhu ya yanke hannun hagun varawo. Ya faxa masa asalin maganar da isnadinta. Mu dai mun bi diddigin littafan masana tarihin musulunci na haqiqi, amma ko misali mislin wannan magana babu a ciki. Kai! Ko malaman da suka shahara da tattara wandararrun magangannu (al-ikhwabat) basu naqalto wannan magana ba. Su ne kuma gaba-gaba a fagen jinjinawa Abubakar da ganin girmansa Raliyallahu Anhu .

2.36 Aliyu Mai Wuta Aljihu

Xan Shi’ar ya ci gaba da cewa: Wani abin kunya kuma da Allah waddai da Abubakar ya yi, wai shi ne qone Fuja’atis-salami da ya yi a wuta. Alhali Annabi Sallallahu Alaihi Wasallama ya hana horo da wuta.



Martani: Idan dai har qone wanda ya cancanci qonewar, kunya ne da Allah waddai to Ali Raliyallahu Anhu ya fi cancanta da qunyar. Don shi ne mai wuta aljihu a jerin Sahabban Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama Domin kuwa akwai ingantattar magana da ke tabbatar da cewa ya qone wasu mutane masu yawa daga cikin Shi’ah Gullatu. Harma da labarin haka ya kai kunnen xan Abbas, Sahabin yayi Allah waddai dashi har ya ce: Da nine shi, ba zan qone su a wuta ba. Saboda Annabi Sallallahu Alaihi Wasallama ya hana yin azaba da abin da Allah ke azaba dashi. A maimakon haka sai dai in sare kawunansu. Saboda cewar da Annabi Sallallahu Alaihi Wasallama yayi: ku kashe duk wanda ya canza addinin sa.

Da wannan magana ta kai kunnen Alin, Sai ya ce: kash! Yanzu xan Ummul-fadhli zai yi wannan magana?!

Ka ga kenan Ali Raliyallahu Anhu shi ya fi dacewa da wannan suka da xan Shi’ar ya yi wa Abubakar Raliyallahu Anhu Don shi ne ya qone dubban jama’a da wutar dake aljihunsa. Idan kuwa har ‘yan shi’a za su iya shafe shi da mai su haxe tattare da haka, to kuwa Abubakar Raliyallahu Anhu yafi cancanta su fara shafawa suhaxiye. Domin kuwa kowanensu ya xauki matakin da ya xauka ne, a matsayinsa na shugaba mai wuka da nama.
2.37 Barewa Ba Ta Gudu Xanta ya yi Rarrafe

A nan kuma xan Shi’ar ya soki lamarin Abubakar Siddiqu Raliyallahu Anhu da cewa, wai masaniyar da yake da ita da hukunce-hukuncen shari’a ba ta taka qara ta qarya ba.

Ga abin da yake cewa: mafi yawan hukunce-hukuncen shari’a sun gagare shi (Abubakar) sani; don bai san hukuncin kalalah ba. Don riwaito shi (Abubakar) da kansa yana cewa: A kan abin da ya shafi kalalah, sai dai in faxi ra’ayina kawai. Idan nayi muwafaqa, to nufin Allah. Idan kuma na kuskure to sharrin sahaixan ne.

Xan Shi’ar ya ce: saboda haka ne, sau saba’in yana bawa kaka haqqin kalalah. Ka ga wannan, na nuna tatatarsa(Abubakar) a faqon dimi.

Ka ji kai!

Martani: ko shakka babu, wannan magana qarya ce hamshaqiya.

Da gaskiya ne Abubakar ya jahilci mafi yawan hukunce- hukuncen shari’a, Annabi Sallallahu Alaihi Wasallama ba zai ba shi damar yin fatawa da Alqalanci a gabansa ba, ba tare da kuma ya ba wani Sahabi irin wannan dama ba. Har kuma ya kasance yana shawara da ganawa da shi fiye da kowa daga cikin Sahabbai, Umar na rufa masa baya.

Abubakar Raliyallahu Anhu nefa, da yawa daga cikin malamai, irin su: Mansur xan Abdul Jabbar as- Sam’ani da wasunsa, suka riwaito cewa kan malamai ya haxu a kan kasancewarsa mafi ilimi a cikin wannan al’umma. Wannan kuwa tabbas ne. Domin kuwa a lokacin halifancinsa, babu wata mas’ala da musulmi za su shiga tajin- tajin a kanta, face ya walwale masu zare da abawarta. Ta hanyar amfani da iliminsa da kafa masa hujjoji daga cikin Alqur’ani da sunna.

Misalin wannan shi ne irin yadda ya tabbatar masu da rasuwar Annabi Sallallahu Alaihi Wasallama; ya ceci imaninsu, ta hanyar kafa masu hujja da ayar Alqur’ani. Sannan ya bayyana masu inda ya kamata a yi wa Manzon makwanci. Ya kuma wayar masu da kansu a kan halacci da wajabcin yaqar waxanda suka hana zakka. Wanda kafin haka har ruxani ya kama Umar Raliyallahu Anhu shi ne kuma, a taron da aka yi a saqifafatu Bani Sa’idu, ya tabbatar wa Sahabbai da cewa: lallai idan ba Quraishawa aka danqawa halifanci ba; kowa an kaba shi da sakal. Wannan, a yayin da wasu kejin cewa ana iya bayar da shi ga waxanda ba Quraishawa ba. Ko ma sune suka fi su cancanta da haka.

Wannan kenan. Kuma ai da Abubakar Raliyallahu Anhu jahili ne, da Annabi Sallallahu Alaihi Wasallama bai waqiltar da shi ga aikin hajjin farko a tarihin musulunci, daga birnin Madina ba. Ka kuwa san mas’alolin aikin hajji sune mas’aloli mafi sassarqiya a cikin mas’alolin ibada. Da kuwa bai naqalcesu nakalta ba, ba abin da zai sa Manzon ya shugabantar da shi a ibadar. Haka kuma waqilcin daya sa shi na limanci. Ka ga shi ma ba a sa jahili. Ta kuma tabbata cewa shi ne kawai Sahabin da Annabi Sallallahu Alaihi Wasallama ya waqilta ga jagorancin aikin hajji da limancin salla.

Bayan wannan kuma. Littafin da Abubakar Raliyallahu Anhu ya wallafa a kan sanin makamar zakka, shi ne littafi mafi inganta a wannan hauji. Shi ne kuma wanda Anas ya karva daga hannunsa. Shi na kuma madogarar malaman fikhun musulunci a kan sha’anin zakka. To in ji.

A taqaice babu wanda zaice ma, komai iliminsa, ga wata mas’ala ta shari’a da Abubakar Raliyallahu Anhu yaci tuwon gigi a cikinta, kamar yadda wasu Sahabbai suka ci.

Za mu yi wannan magana idan lokacin ta yayi.

Ita kuwa cewar da xan Shi’ar yayi, wai Abubakar bai san hukuncin kalala ba. Saboda haka ne yayi amfani da ra’ayinsa...

To sai muce: ai barewa bata gudu xanta yayi rairahe; A matsayin Abubakar Raliyallahu Anhu na xan hannun daman Annabi Sallallahu Alaihi Wasallama kuma babban almajirin makarantarsa, hukuncin kalala ya yi masa kaxan.

Amfani da ra’ayinsa da ya yi a cikin wannan hukunci, na daga cikin abubuwan dake nuna zurfin iliminsa. Kuma haka ne tasa junhurun malamai suka karvi ra’ayin nasa da hannun biyu- biyu, ba yan rasuwarsa, a matsayin tsayayyen hukunci a kan al’amarin kalalah; wato wanda ba yada mahaifa ko ‘ya’ya raye.

Kuma amfani da ra’ayi (hasashe) a cikin hukuncin shari’a ba gare shi farau ba. Umar da Usman da Ali kansa, da xan Mas’ud da Zaidu xan Sabitu da Mu’azu xan Jabalu Raliyallahu Anhu duk suna amfani da hasashensu a cikin hukunce- hukunce. Kuma a duk lokacin da hasashen mutum ya dace da gaskiya, Allah zai bashi lada biyu; kamar dai irin wannan hasashe na Abubakar Raliyallahu Anhu. Shi ne kuma mafi alheri bisa ra’ayin da mai shi zai kafe kansa, tattare kuma da sanin qundin ladarsa xaya ce. Wato kamar dai ra’ayin da Ali Raliyallahu Anhu ya kafe kansa na neman tilastawa Mu’awiyah ya yi masa bai’a a matsayin halifa. Ra’ayin da a qarshe ya yi sanadiyar zubar da jini da rasa rayuka .

Eh! Ra’ayinsa ne shi kadai tallin tal. A kan haka nema aka riwaito cewa Karsu xan Ubaidu ya ce masa, kafin wuta ta kama: ina son in gane ya Ali, shin wannan ra’ayi da ka yi tsaye kyam a kansa, Umurnin Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama ne koko dai ra’ayin qashin kanka ne? Sai ya karva masa da cewa: Ra’ayina ne dai.

Abu Dawuda da wasunsu duk sun riwaito wannan magana.

To ka ga idan har irin wannan ra’ayi daya zama sanadiyar salwantar rayuka, bai hana jama’a yarda da kasancewar mai shi halifa ba. To qaqa za’ayi da jumhurun malamai suka karva hannu biyu-biyu, kuma bai zama sanadiyar kashe ko kiyashe ba, ya zama dalilin qin yarda da mai shi, ko abin suka a kansa?!

Ita kuwa cewar da ya yi wai sau saba’in Abubakar na hukuntar da hukuncin kalalah ga kaka, maganace ta qarya Xan Shi’ar ya yi. Wadda kuma ke tabbatar da kasancewarsu (‘yan Shi’ah) imaman jahilai da maqaryata.

Wannan hukunci bana Abubakar Raliyallahu Anhu ne ba, babu wanda ya tava riwaito shi daga gare shi.


Yüklə 2,75 Mb.

Dostları ilə paylaş:
1   ...   16   17   18   19   20   21   22   23   ...   51




Verilənlər bazası müəlliflik hüququ ilə müdafiə olunur ©muhaz.org 2024
rəhbərliyinə müraciət

gir | qeydiyyatdan keç
    Ana səhifə


yükləyin