Tafarkin sunnah


Mafi Yawan Mutanen Kufa Jahilai Ne



Yüklə 2,75 Mb.
səhifə21/51
tarix28.10.2017
ölçüsü2,75 Mb.
#17506
1   ...   17   18   19   20   21   22   23   24   ...   51

2.38 Mafi Yawan Mutanen Kufa Jahilai Ne

A qoqarin wannan xan Shi’a ne, na fifita Ali Raliyallahu Anhu Ya ci gaba da cewa: Ina Abubakar ina imamu Ali! Ai lizami yafi qarfin bakin kaza. Imamu Ali ne fa ya cewa mutane: ku tambayeni duk abin da kuke so, kafin ku nemeni ku rasa. Ku tambaye ni a kan duk abin da keda alaqa da sama’u. Ni kuwa in baku amsa daga nan qasa.

Xan Shi’ar ya kafa hujja a kan wannan magana tasa da cewa: Abul-Buhtari ya ce: Na ga Ali watarana a Kufa; a kan mimbari yana sanye da sillken Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama na yaqi. Yana kuma rataye da takobinsa, naxe da rawaninsa kuma sanye da zobensa Sallallahu Alaihi Wasallama a hannu. Nan take sai ya zauna ya kware cikinsa, ya kuma cewa jama’a: ku tambayeni duk abin da kuke so, kafin ku nemi ni ku rasa. Domin haqarqarina cike suke da tarin ilimi. Kuma cikin nan nawa salkar ilimi ce. Ni ne sirrin Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama shi ne ya tsatsageni da ilimi; ba wahayi ne aka yi mani ba. Wallahi da za’a shimfixa mani darduma in zauna a kai. Zan iya yi wa mutanen Attaru fatawa da Attaurarsu. In kuma yi wa mutanen linjila da linjilar su. Har Allah ya hukunci Attaura da magana, tace: lallai Aliyu yayi gaskiya. Haqiqa fatawar da ya yi maku dai dai take da abin da Allah ya saukar a cikina. Amma kuka kasa ganewa sai kace ba ku karanta al-qur’ani?!

Martani: Ba musun cewa, Aliyu ya ce: ku tambaye ni. Amma ai yana magana ne da mutanen Kufa. Kamar yadda riwayar ta nuna. Ya kuma ce masu haka ne,don su cika shi da tambayoyi, har yayin amsa su, shi kuma ya cika su da ilimin Addini , saboda mafi yawansu jahilai ne; ba suyi tozali da Annabi Sallallahu Alaihi Wasallama.

Amma ka ga mutanen da ke kewaye da mimbarin Abubakar Raliyallahu Anhu sune manya - manyan Sahabban Annabi Sallallahu Alaihi Wasallama waxanda kuma suka sha suka ya tatil da ilimi mai kabri na addini a hannun manzo Sallallahu Alaihi Wasallama wanda hakan ta sasu kasance mutane mabiya ilimi da kishin addini a cikin wannan al’umma.

A yayin da waxancan mutane da Ali Raliyallahu Anhu ke waccan magana dasu ya ku bayi ne, tabi’ai kawai. Kuma mafi yawansu ashararu ne ko a cikin tabi’an. Wanda hakan ta sa Alin kodayaushe yake yawan kuka da su, tare da xebe masu albarka. Hakan tasa aka wayi gari tabi’ai daga cikin mutanen Makka da Madina da Sham da Basara suka fisu nagarta.

Sannan kuma idan xan Shi’ar ba yada labari: Ai matsayin kowane daga cikin waxannan halifofi huxu a fagen ilimi ba abu ne voyayye ba. Domin kuwa malamai a wancan lokaci da sauran almajiran ilimi, sun hada hancin fatawowi da hukunce- hukuncen da kowane xaya daga cikinsu yayi. Qarshe dai aka jinjina na kowane, sai aka taras da cewa na Abubakar Raliyallahu Anhu sun fi haxuwa. Wanda hakan ke nuna irin yadda ya yi wa sauran fintinqau a fagen ilimi.

Bayan na Abubakar sai na Umar suka biyo baya Raliyallahu Anhu kuma shi ne dalilin da ya sa xan takin saqar da ake samu tsakanin fatawowin Umar da na Abubakar, idan aka xorasu akan ma’aunin nassi, bai taka qara ya qarya ba. Idan aka yi la’akari da yadda kodayaushe na Ali ke yin yamma a lokacin da na Abubakar xin Raliyallahu Anhu suka yi gabas maxauka lada. Da wuya matuqa a samu wani nassi da yaqi amincewa da wata fatawa ko wani hukunci da Abubakar Raliyallahu Anhu yayi.

Kuma ai Xan Shi’ar sanine bai yiba. Abubakar Raliyallahu Anhu ne wanda kodayaushe ke warwarewa waxannan Sahabbai (halifofi) zare da abawa duk wata mas’ala mai rikitarwa. Ba a kuma tava samun wanda ya tava bijire masa a kan haka ba, tsawon rayuwarsa. Sai bayan rasuwarsa ne aka fara jinsu, ana kuma ganin su rana a kan hukunce-hukunce. Don mai kwance daragar, Abubakar Raliyallahu Anhu ya kwanta dama.

Wannan kenan. To amma cewar da ya yi wai Ali Raliyallahu Anhu zai yi wa mutanen Attaura da Linjila hukunci da littafansu, magana ce da ke son nazari. Domin kuwa abu ne sananne kuma tabbatacce cewa al-qur’ani da hadisi da ijma’i sun haramta yin hukunci tsakanin Yahudawa da nasara; wa-su-wa-su sai da abin da Allah ya saukar wa Muhammadu. Ko da kuwa hukuncin bai yi daidai da abin da ke cikin littafin nasu ba.

To ka ga ashe kenan duk wanda ya ce Ali Raliyallahu Anhu ya yi waccan magana, har ya kwarzanta shi da ita. Ko dai ya kasance qaton jahilin addini. Wanda kuma bai san abin da kamata a ajinginawa lamirin Ali Raliyallahu Anhu a matsayin yabo. Ko kuma ya kasance zindiqi ne., da ya yi nufin sukar lamarin Alin. Ta hanyar jingina masa wannan magana da ke jawa wanda ya yi ta zargi da azaba maimakon yabo da lada.


2.39 Girma Ya Kai !

An dai gama ta xan Shi’ar nan ya cimma gavar abin da yake son tabbatar. Don ga shi yaba Ali Raliyallahu Anhu muqamin “shafe zane” ta hanyar amfani da wani qagaggen hadisi:

Bari ka ji abin da ya ce:

Wai baihaqi ya riwaito, da isnadinsa daga Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama wanda ya ce wai: duk wanda yake son yaga Adamu a cikin rigarsa ta ilimi da Nuhu a cikin rigarsa ta tsoron Allah, da Ibrahim a cikin rigarsa ta haquri, da Musa a cikin rigarsa ta kwarjini, da Isa a cikin rigarsa ta ibada, to yakalli Aliyu xan Abi Dalib. Wai Allah ya tarkata masa duk waxannan siffofi da ya rarraba wa waxannan. Annabawa

Ka ji kai. Lalle girma ya kai!

Martani: kafin komai muna son muja hankalin xan Shi’ar a kan cewa fa, ya manta ya ambaci isnadin wannan hadisi. Kuma idan bai sani ba Imamul-Baihaqi kan riwaito raunana, kai harma da ka gaggun hadisai, a kan abin da ya shafi falaloli. Kamar dai yadda takwararorinsa ma’abuta ilimi suka al’axanta.

Sannan abu na biyu: ko shakka babu wannan hadisi qarya ce aka yi wa Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama. Kamar yadda ma’abuta ilimi suka tabbatar. Saboda haka nema duk da irin kwaxayin da suke dashi ga tattara darajojin Ali Raliyallahu Anhu ba su riwaito wannan hadisi ba.

Ka ga nisa’i, a cikin littafinsa mai suna: “Al-khasais”, da Tirmizi a cikin tarin hadisan daya ambata a kan darajojin Ali, duk da kasancewar akwai masu rauni da qagaggu a cikinsu. Amma duk basu ambaci wannan hadisi da makamancinsa a cikin ayyukan nasu ba.
2.40 Ba Dai A Madina Ba

Bayan wannan kuma sai xan Shi’ar ya ci gaba da cewa: kuma Abu Umar Az-zahidi ya ce: Abu Abbas ya ce: Ba musan wani daga cikin Sahabbai ba, da ya bugi qirji saboda tarin iliminsa, ya ce wa musulmi, bayan Annabi ya kaura: ku tambaye ni duk abin da kuke so; na tun daga zamanin Annabi shisu har zuwa zamanin Annabi Muhammadu. Sai Ali Raliyallahu Anhu kuma a kan wannan dama ce da ya bayar, manyan Sahabbai irin su Abubakar da Umar Raliyallahu Anhuma da makamantansu, suka dinga yi masa ruwan bama - baman tambaya, yana ba su amsa, har ya shaqe su. Sannan ya ce: ya kai Kumailu xan Zayyad, ka sani tsatsage nake da tarin ilimin da, da zan sami mazaken qwarai da ke iya xaukar sa, da anga abu.



Martani: Wannan magana ba ingantatta bace. Domin kuwa ko shi Sa’alabu wanda ya riwaito ta asalatan bai ambaci isnadinta ba, balle ta cancanci zama abin kafa hujja. Kuma hasali ma, Sa’alabu baya cikin malaman da suka san kabli da ba adin hadisi, balle ya iya gane gangariyarsa da mai sanqara. Wanda hakan za ta iya ba wani damar iya bugun qirji ya ce: hadisi kaza ya inganta a wurin Sa’alabu. Kamar yadda ake iya yin garkuwa da riwayar Ahmad ko Yahya xan Mu’inu ko Axuwa uba Buhari, da matara kama da su.

To ko waxannan malaman, da makamantansu daga cikin waxanda suka yi malin sa’alabu a wannan fage. Kan ambaci hadisan da ba su da tushe. Balle makama, a cikin ayyukansu, balle shi. Muna iya yi wa Sa’alabu uzuri domin wannan magana, ya riwaito tane daga bakin irin mutanen nan da suka kware a fagen halin hankaka, na mayarda xan wani nata; don ba sukan ambaci sunayen waxanda suka samo magana daga gare su ba.

Wannan kenan. To kuma tafi, mu xauka cewa gaskiya ne Ali Raliyallahu Anhu ya yi wannan magana. To ba ko a Madina ba; daidai lokacin halifancin Abubakar ko Umar ko Usmanu Raliyallahu Anhu Ali Raliyallahu Anhu ya na da dama da sararin faxin haka amma a Kufa, lokacin da yake halifa. Don hakan ta zama wani qarani da salon jawo hankalin mutanenta zuwa ga qaratu da neman sanin duk abin daya kama ce su sani, daga wurinsa. Saboda asalatan su mutane ne masu tsananin ragganci da kasawa fagen neman ilimi.

Wani abu dake qara tabbatar da ingancin wannan fixa da muka yi wa wannan magana, shi ne, kasancewar kumailu nan tabi’i. Bai yi tare da Ali Raliyallahu Anhu ba sai a Kufa. Ka ga wannan na tabbatar mana da cewa leke su da Ali Raliyallahu Anhu yayi; ya gama fahimtar kasawarsu a fagen ilimi tasa ya yi waccan magana. Ko alama Ali Raliyallahu Anhu ba zai ‘iya buxa baki ya fadi irin wannan magana a cikin Muhajiruna da Ansaru ba. Allah ya daxa yarda da su, amin.

Sannan kuma cewa Abubakar Raliyallahu Anhu ya tava tambayar Ali Raliyallahu Anhu wani abu na ilimi wala. Amma da an tsaya ga Umar Raliyallahu Anhu to maganar na sauraruwa. Don shi ya kan yi shawara da Sahabbai irin su Usman da shi Aliyun da Abdurrahman da xan Mas’udu matsayinsu na ‘yan majalisar shawara.

Ka ga ko a haka akwai magana.


2.41 Akwai Abin Da Siddiqu Ya Gani

Har yau dai mutumin naku; sarkin jahilai bai gaji da xaukar zunubi ba a cikin haqqin Sahabbai. A nan kuma cewa ya keyi wai, Siddiqu ya yi wa hukuncin Allah zinbire tunda bai kama Khalidu xan Wahdu ya aika shi lahira, saboda ya kashe malik xan Nuwairatu, tattare da kasancewarsa musulmi ba. Wanda hakan har tabawa shi Khalidun damar aure matar Malikun, ya kuma yi baiko da ita a daren da tsohon mijin ta ya baqunci lahira. Kuma ma wai har sai da Umar ya jawo hankalin Abubakar xin Raliyallahu Anhu a kan wajabcin kashe Khalidun. amma wai saboda tsabar qin Allah, Abubakar Raliyallahu Anhu yayi shayulatin vangare da maganar tasa. Duk inji xan Shi’ar.

Farkon abin da za mu fara faskarawa xan Shi’ar a ka, a matsayin martani kan wannan magana shi ne: idan har akyale wanda ya kashe wani ba bisa haqqin shari’a ba, wani abin kunya da ashane ga shugabanni, to, lalle kuwa dangin Halifa Usmanu nada babbar hujja akan qayar bayan da suka tayarwa Ali Raliyallahu Anhu akan lalle ya bimasu kaxin jinin xan’uwansu. ya kuma qi. Ka kuwa san a matsayin Usmanu Raliyallahu Anhu na halifa ga musulunci. Wanda kuma aka yi wa kisan gilla; bai ji bai gani ba. Darajarsa ta linka ta Maliku xan Nuwaira ta fiye da sauran yawan qasa. Amma kuma duk da haka Aliyu yaqi kashe makasansa. Wanda hakan ya zama qwaqqwaran dalilin da dangin na Usmanu Raliyallahu Anhu suka riqa a kan qin yi wa Aliyu mubaya’a.

To. Idan kuwa har kuna ganin akwai wani uzuri na shari’a daya hana Alin kashe maka shin Usmanu Raliyallahu Anhu kashe makashin maliku shi ne mafi qarfi. Idan kuwa kuna ganin cewa abubakar Raliyallahu Anhu baya da wani dalili a kan haka, to ko, Ali Raliyallahu Anhu shi ne mafi zama marashin dalilin a kan yarda wa makasan Usmanu Raliyallahu Anhu ci gaba da rayuwa.

Ka ga kenan a haka, ta tabbata cewa jahilci ne daya yi wa ‘yan Shi’ah riga da wando, da kuma tinka da walwala, suka sa suna zargin Abubakar Raliyallahu Anhu tare da qorafi a kansa, a wannan ‘yar kankanuwar matsala. Alhali ga wata qasaitacciyar matsala can ta kewaye Ali Raliyallahu Anhu amma sun sa qafa sun taushe; kamar ba a yiba. Tattare da cewa duk mai hankali da basira isassa ya san cewa, lalle akwai abin da Siddiqu ya gani.

Ba a kan Abubakar Raliyallahu Anhu kawai suka tsaya ba. Sun soki lamarin halifa Usmanu Raliyallahu Anhu shi ma. A kan wai yaqi kashe Ubaidullahi xan Umar saboda kisan gillar da ya yi wa Hurmuzanu.

To, duk wannan martani, ya isa kariya ga waxannan halifofi biyu masu girman daraja.

Wannan kenan. To idan kuwa har ‘yan Shi’ah za su yi qarfin halin ce mana: To ai Ali Raliyallahu Anhu nada Uzuri a kan rashin kashe makasan Usmanu, kamar yadda muka qaddara yiwuwar su ce. Qarshe kuma suce mana uzurin kuwa shi ne: Rashin cikar sharuxxan dake wajabta qisasi; koko a’a, Aliyun bai san waxanda suka yi mugun aikin ba. Ko kuma ya sansu, amma sun fi qarfinsa saboda kasancewarsu buwayayyi. Ko kuma dai wani dalili mai kama da wannan.

To sai mu ce masu mu kuma: Eh! To mun ji, mun kuma yarda. Sai dai, su ma makasan Maliku da Hurmuzanu, duk babu wanda dalilan da za su wajabta qisasi a kansa suka cika. Saboda akwai shubuha (ruxani) a cikin mas’alolin nasu. Shubaha kuwa dalilice mai kwari da ke tunkuxe haddi.

Na san kuma saboda tsananin qarfin hali da kangara, suna iya sake cewa: Bawata shubuha dake ciki. Tunda har sai da Umar da Ali suka tabbatar wa Abubakar da Usmanu Raliyallahu Anhu rashinta, tare da wajabcin kashe makasan; wato Khalidu da Ubaidullahi. Amma suka qi.

To amsarmu a nan itace: Idan wannan na zama dalili, me ya hana Ali Raliyallahu Anhu kashe makasan Usmanu, tunda har sai da Xalhatu da Zubairu da wasu Sahabbai suka tabbatar masa da wajabci da yiwuwar haka? Me ya hana shi?

Kuma aje ma duk wannan. idan tonon silihi kuke so a yi, bisimillah...!

Kun mace cewa, Abubakar Raliyallahu Anhu bai kyale waxanda suka ba shi shawarar kashe khalidu haka nan ba; sai da ya kafa masu hujjar da ta gamsar da su, da cewa: qisasi bai wajabta kan khaladu. Saboda abu ne mai yiwuwa qwarai ya kasance a kan haqqin Allah na ya kashe Malikun. Saboda a mafi rinjayen zato dakare kuma barden musulunci irin Khaladu, ba zai kashe musulmi haka kaxai ba; saboda haka lalle ne akwai wani ijtihadi daya dogara a kansa, kafin ya aika shi lahira.

Amma rashin gamsuwar da Ali Raliyallahu Anhu yayi da waxanda su ka ba shi shawarar kashe makasan Usmanu, mummunan yaqi ta haifar tsakaninsu. Wanda muninsa yafi na kisan da aka yi wa Usmanu. Kowa yasan irin nauyin abin da ya faru a yaqin sibbaini da Jamalu.

To idan kuwa har za’a iya yi wa Ali uzri a nan, to yi wa Abubakar Raliyallahu Anhu uzuri a can shi ne mafi cancanta da dacewa. A matsayinsa na waxanda suka dogara a kan wani karvavven ijtihadi.

Na daxe da sanin cewa ‘yan Shi’ah na iya izgilin cewa, maganar kisan gillar da aka yi wa Usmanu, ba wata matsala bace, domin jininsa halattace ne. Saboda yadda ya tozartar da alfarmar dukiya da halifancin musulunci.

To, harwayau dai. Mu qaddara cewa waxancan abubuwa sun halatta jinin Usman xin Raliyallahu Anhu Amma babu mai hankali da musun cewa jinin Maliku xan Nuwairatu yafi cancanta da halatta. Domin kuwa, hasali babu wanda ke iya tabbatar da rashin cancantar Malikun da wancan kisa da khalidu ya yi masa ta fuskar shari’a; mu dai a wurinmu babu wannan dalili.

Amma halifa Usmanu Raliyallahu Anhu dalilai da nassosa daga cikin al-qur’ani da sunna sun tabbatar da cewa kisan da aka yi masa zalunci ne. Kuma kowa ya san fifikon da Usmanu yake dashi a kan xan Nuwairata, Allah kadai ne ya san iyakarsa.

Kuma babu ta yadda za a yi wanda ya halatta jinin Usmanu, ya iya haramta na Ali ko Husaini Raliyallahu Anhu Domin kuwa dalilan dake tabbatar da haramcin jininsa sun fi qarfi da bayyana bisa waxanda ke haramta nasu. Abubuwan da ke kaiwa ga sa a zubar da jinin mutum, qalilan ne matuka a cikin al’amarin Usmanu, idan sha’anin Ali da Husaini Raliyallahu Anhu kuma ruvavvun dalilan da makasan Usman suka lave bayansu, sun fi waxanda makasan Ali da Husaini suka lave bayansu nuqa da ruva.

Fara lissafi.

Ka ga dai halifa Usmanu bai kashe musulmi ko xaya ba. Bai yaqi kowa a kan rashin yi masa muba a ba; ko niyar haka bai kulla ba. Mu tsaya ma anan.

To ka ga renin hankali da ilimi ne, a ce wanda ya shaya daga da musulmi don neman shugabanci, jininsa haramtace ne. Don abin can da ya yi ijtihadi ne. Amma wanda bai yaqi ko sauro ba, a ce jininsa ya halatta, ko shakka babu Usmanu Raliyallahu Anhu shi ne mafi cancanta da kasancewa mai haramtaccen jini, kuma mujtahidi a cikin irin yadda ya riqa dukiya da halifancin al’umma.

Wannan kenan. Sannan kuma mun yarda da cewa jinin Malilku xan Nuwairata haramtacce ne asalatan. Amma khalidu ya halatta shi a kan wani tarihi, har ya aika shi lahira. To ai, wannan ba komai ba ne balle har ya halatta ko wajabta kashe khalidun.

Ah! Kun manta da Usamatu xan Zaidu ya kashe wani mutum a wurin yaqi, bayan ya furta kalamar shahada. Har Annabi Sallallahu Alaihi Wasallama ya ga laifinsa;. Ya ce: ya zaka kashe mutum bayan ya ce: La’ilaha illal-lahu?. Ya maimata haka ga Usama har sau uku.

Amma duk da haka Annabi bai nemi Usama da biyan wata diyya ko kaffara ba a kan haka, balle ramuwa, tunda ya yi kisan ne a kan wani tawili. Ya kuma yi nadama a qarshe.

Sannan zancen auren matar Maliku da yin bai ko da ita a daren da yabar duniya, da shi Xan Shi’ar ya ce khalid yayi, magana ce da bata inganta ba. Ko da kuma Allah yasa ta ingantan, to babu wani dalili da zai wajabtar da haddin jifa a kansa. Domin kuwa malaman fiqihu sun qara wa junansu ilimi ta hanyar kasuwa gida biyu a kan wajabcin iddar mutuwar miji kafiri tantagarya ko na tawili. Wasu suka ce wajibi ce, wasu suka ce ba wajibi ba ce. Kamar yadda ta faru tsakaninsu a kan wajabcin iddar a kan zawariyyar da mijin ta ya rasu. Sabanin iddar saki, wadda take wajabtarwa. Ita kan babu wani ka-ce-na-ce a kanta. Lalle ne sai an tsalkake mahaifa kafin ayi wani aure.

Amma ita iddar mutuwa, ta na wajabta ne, daga lokacin da aka tofa fatiha anka daura aure. Amma da mijin zai mutu a dai - dai lokacin da kuma yake kafirta asalan, iddar na ci gaba da zama wajibi kan matar ko qaqa? A nan ne malamai suka xan wasa kwakwalwa. Kamar yadda suka yi akan wajabcinta kan matar da irin wannan miji yayi baiko da ita bayan xaurin auren kuma ta yi wanki xaya bayan haka.

To amma idan qaddarar ridda ce ta fada masa, sai kuma ga mutuwa kwaram. A mazhabar Shafi’i da Ahmad da Abu Yusuf da M uhammad za ta yi idda, amma ba ta wadda mijinta ya rasuba, ta dai wadda aka rabu da ita, rabuwa ba’ina. Saboda aure na vaci da zarar miji yayi ridda. A wurin Shafi’i da Ahmad kuwa irin wannan rabuwa da ke faruwa saboda ridda, ba a ce mata saki. Saboda haka ne ma suka qi wajabtawa matar iddar rasuwa, sai dai ta rabuwa ba’ina.

Idan kuma dama bai yi baiko da ita ba, ya rasu to ba kowace irin idda a kan ta, a wurinsu. Kamar yadda ba zata yi iddar ba ko da sakin ta yayi, matukar dai bai .kusance ta ba.

Amma irin waccan rabuwa ta mutuwa, kamar rabuwa ce ta saki a wurin Maliki.

To, idan har ka fahimci wannan qullin makodo na malaman fikhu, zaka yarda da cewa lalle akwai abin da Siddiqu ya gani ya qi kashe khalid. Domin kuwa bai kashe maliku ba sai da ya gama yanke masa hukuncin ridda. Ka ga idan har anyi sa’a bai kusanci matar ba, shi Maliku. To ba za tayi wata idda ba, a matsayin gaba xayan malamai. Idan ma har koya kusance ta, to wanki xaya ya isa tabbatar da tsarkin mahaifarta, da ba dole sai ta yi cikakkar idda ba, bisa xayan zancen malaman; wanda xayan sun ke wajabta mata wanki uku.

Idan kuwa asalatan kafiri ne, matar ba za tayi idda saboda mutuwar sa ba, bisa xayan zancen waxannan malamai. Idan kuma har tsarkin mahaifar tata ba zai tabbata ba, sai idan tayi wanki bayan mutuwar mijin, to haka ba zata wajabta akan taba, sai idan ta tava wanki kafin baikon.

A haka ma, akwai malaman da ke jin wani sashe na kwanakin wanki ya isa tabbatar da tsarkin mahaifa.

A ta kaice dai mu a iyakar saninmu, duk yadda aka kixa kuma aka raya, ba yadda za a yi wannan mas’ala ta kasa karvar sallamar ijtihadi karvavve a idon shari’a. Kuma sukar wani da irin wannan al’amari xabi’a ce ta jahilai. Kuma abune da Allah da Manzonsa suka haramta.


2.42 Gadon Fatima Da Laqabin “Halifa”

Daga nan kuma sai xan Shi’ar ya ci gaba da cewa wai: kuma Abubakar ya savawa umurnin Annabi Sallallahu Alaihi Wasallama tunda har ya hana Fatima gadon mahaifinta, da Fadak. Kuma ya qaqabawa kansa laqabin “halifatu Rasulullahi” alhali ba Annabin ne ya zave shi halifansa ba.



Martani: Bari mufara da matsalar gadon Fatima. Wannan batu mun riga munyi magana a kansa. Mun kuma tabbatar wa duniya da cewa matakin da Abubakar Raliyallahu Anhu ya xauka a kansa shi ne madaidaici. Wanda saboda haka ne ma gaba xayan musulmi suka marawa baya a kai, in ban da wasu ‘yan Shi’ah. Haka kuma mun tabbatar wa ku da cewa matsayin nasa hukunci ne da Annabi Sallallahu Alaihi Wasallama yayi. Kuma abin da ‘yan Shi’ah nan ke yayatawa a kan wannan matsala, da ta Fadak, babu gaskiya a cikin ko kaxan.

Kuma halifancin da suka biyo bayan Abubakar Raliyallahu Anhu babu wanda ya tayarda wancan hukunci nashi. Kuma babu wani abu; ko da kwatankwacin Allura, da Abubakar da Umar Raliyallahu Anhuma suka xaukar wa kansu, ko suka ba iyalinsu daga Fadak xin, balle a ce. Kuma Fadak ba kome ba ce, idan aka yi la’akari da irin abin da waxannan halifofi suka mallaka wa Banu Hashim.

Kuma yau da wani daga cikin musulmi zai yi qorafi, da kafa hujja da cewa, ai Ali Raliyallahu Anhu ma ya hana wa xan Abbas da sauran Bani Hashim ko sisi daga cikin Baitil mali, har hakan ta sa xan Abbas xin ya dahe wasu kuxaxe a Busra yasa su mala. Na san ba abin da za kuce, a qoqarin bawa Alin kariya illa cewa, ya yi haka ne saboda tabbatar da gaskiya da riqon amana, a matsayinsa na shugaba adili; saboda haka bai kamata a zarge shi ba.

To ku sani Abubakar Raliyallahu Anhu shi ya fi dacewa da cancanta da irin wannan kariya. Domin kuwa son da yake yi wa Fatima da qoqarin tsare alfarmarta, sun fi waxanda Aliyu Raliyallahu Anhu ke yi wa xan Abbas. Kuma matakin da xan Abbas ya xaukarwa Aliyu Raliyallahu Anhu na nuna kasancewarsu qare ba a tsaga ba. Savanin Fatima ga Abubakar Raliyallahu Anhu. ko alama abin arzikin da ke tsakanin Ali da xan Abbas, bai kai wanda ke tsakanin Abubakar da Fatima ba Raliyallahu Anhu.

Shi kuwa laqabin “Halifa” da xan Shi’ar ya ce wai, Abubakar Raliyallahu Anhu ya qaqalawa kansa, qaryar banza ce. Duk wanda ya san tarihin musulunci yasan cewa musulmi ne suka yi wa shi wannan laqabi a qaran kansu.

Kuma idan kalmar “Halifa” na nufin wanda anka halifantar, kamar yadda maganar xan Shi’ar tazo, to ai cewa Abubakar Raliyallahu Anhu halifa ba laifi bane, don Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama ne da kansa ya halifantar dashi. Kamar yadda Ahlus-Sunnah suka yi imani. Idan kuwa kalmar na nufin wanda ya maye gurbin wani, ko da shi wanin bai yi umurni da hakan ba. kamar yadda jumhuru suka yi imani, to ai kuma babu sunan da ya kamata a ambaci Abubakar xin da shi in ba “Halifa” ba Raliyallahu Anhu .

Wannan ma’ana ta biyu kuwa, itace abin da Alqur’ani da sunna ke tabbatarwa. Bari ka ji. Allah Ta’ala na cewa: Sannan muka sanya ku masu mayewa (halifa) a cikin qasa daga bayansu, domin muga yaya kuke aikatawa (10:16).
2.43 Ya Kuma Dira A Kan Umar

Bayan kuma da wannan xan Shi’ar ya gaji da cin mutun cin Abubakar Raliyallahu Anhu sai ya dira a kan Umar Raliyallahu Anhu.

Ga alama haka zai bi manyan halifofi xaya bayan xaya.

Farkon abin da ya fara da shi, shi ne cewa wai; Daga cikin abubuwan dake tabbatar da cewa halifofin nan uku ba kowa bane, a wurin Allah, akwai abin da aka riwaito a cikin littafin: “Hilyatul-auliya’u”. Marubucin littafin; Abu Nu’aimi al-Hafiz ya ce wai anji Umar na cewa, a lokacin da ya kai gargara: kaicona ina ma dai rago Allah ya yi ni, daga cikin ragunan dangina. Su yi ta kiyona har kitse ya rufe mani qoda. Qarshe su yanka ni liyafa ga mafi soyuwa daga cikin baqinsu. Su soya rabin namana rabi kuma suyi romo. A taru ayi mani kaf, in zama turoso ba mutum.

Xan Shi’ar ya ce: To ka ga wannan magana ta Umar, wai tayi dai - dai da ta kafircin da zai buxa baki gobe lahira ya ce: kaitona dama dai na zama turxaya (79:40).

Daga nan kuma sai ya koma kan xan Abbas, ya ce wai shima ya ce,

a lokacin da ya kai gargara: wallahi dana mallaki zinarin da ya yi yawan qasa da na bayar dashi, don in tserewa tashin hankalin ranar lahira.

Mutumin naka ya ce ita kuma wannan magana wai dai - dai take da cewar da Allah Ta’ala ya yi: kuma da waxanda sukayi zalunci suna da abin da ke cikin qasa gaba xaya, da misalinsa a tare dashi, lalle da sun yi fansa dashi daga mummunar azaba (39:47).

Sannan ya ce: To don Allah muna son masu hankali su dubi waxannan maganganu, na waxannan mutane biyu, su kuma auna su dacewar da Ali Raliyallahu Anhu yayi:


  • “Wai yaushe ne mutuwa zata xauke ni, in sadu da masoyana;... Muhammadu da rundunarsa.

  • Wai yaushe ne zan yi tozali dasu ... in kuma ga yadda za a yi tawayya da marasa arziki daga cikinsu”

Da kuma kalimar da ya yi a lokacin da xan Muljamu ya xora shi kan godaben zuwa lahira wadda ya ce:

  • “Wallahi na taki sa’a”

Wato xan Shi’ar naso ne ya ce, Umar kafiri ne. Xan Abbas kuma azzalumi ne Raliyallahu Anhu. wal’iyazu Billahi.

Martanin mu a kan wannan magana shi ne; ko alama wannan zance bai kai lasaba kuma wata alama ce, da ke nuna kabrin jahilcin xan Shi’ar. Domin kuwa ba Aliyu Raliyallahu Anhu ne aka tava jin ya furta irin waxancan kalmomi dake nuna jaruntaka da rashin fargaban zuwa lahira ba. Wasu Sahabbai da ba su kai darajar sa, balle ta Abubakar ko Umar ko Usmanu Raliyallahu Anhu har ma da wasu daga cikin masu kafirta Alin, daga cikin Harijawa, sun furta irin waxancan kalmomi.

An riwaito cewa Bilalu, Sahabin da Abubakar Raliyallahu Anhu ya yi wa hidima da karimcin “’yanci”, an ji yana yin aras da matarsa, a lokacin da ya kai gargara. Hankalinta ya tashi tana cewa: yau mun shiga uku mun lalace!. Shi kuwa yana cewa: can gareki ni kam farin ciki nake yi. Gobe zan haxu da masoyana; Muhammadu da rundunarsa

Bilalu kenan. Sahabin da Umar Raliyallahu Anhu ya yi wa “Allah ya isa” shi da wasu Sahabbai, saboda sun fitine shi, a kan lalle sai ya raba ko rayen tuxxan Iraqi ga mayaqa. Shekara kuwa bata zagayo ba sai da Allah ya karvi rayuwarsu gaba xaya.

Amma ka ji kalmomincan da Ali Raliyallahu Anhu ya furta basu fi waxannan da shi ya furta zaqi da qarfi ba.

Wani kuma abu dake qara tabbatar da cewa, ba Ali Raliyallahu Anhu ne farau a irin wannan baiwa ba shi ne abin da Abu Nu’aimi xin ya riwaito a cikin wanna littafi nasa “al-Haya” inda ya ce: kudai’i da Hasan xan Abudullahi da Amir xan Sayyaru da Abudul-Hamid xan Hushub, daga Abdur-Rahman xan Ganami, daga kuma Harisu xan Umairin, wanda ya ce: watarana an soki Mu’azu da Abu Ubaidata da Shuraihabilu xan Husnata da Abu Malik al-Ash’ari, a wurin yaqi. Sai Mu’azu ya ce: Ai wannan ba abin mamaki ne ba. Wannan suka da aka yi mani a rana xaya, muna kuma dangin juna, wata rahama ce daga wurin Ubangijinmu, wadda Annabinmu ya roqar mana. Kuma nagartattun bayi waxanda suka gaba cemu suka ce”Amin” a lokacin da Annabi ya ce: ya Ubangiji ka yanka wa mutanen gidan su Mu’azu babban rabo daga cikin irin wannan rahama.

Mu’azu Ya ci gaba da cewa; marece na gaba dayi, bayan wannan adu’a sai kuwa aka kaiwa xana Abdur-Rahmanu Bikrah; xaya daga cikin ‘ya’yana da nafi so, suka. Ina dawowa masallaci na same shi murtut da fuska, yana cikin zilla. Na ce masa me ya faru ne Abdurrrahman? Sai ya ce: Bari baba. Gaskiya ta tabbata daga Ubangijika, kada kuma ka zama cikin mutane masu ruxani.

Sai ni kuma nace masa: Ni kuwa da yardar Allah zan kasance daga cikin mutane masu haquri.

Mai riwaya Ya ci gaba da cewa: Haka Mu’azu Ya ci gaba da rungume wannan xa nasa, har zuwa lokacin da ransa ya fita. Safiya nayi aka yi jana’izarsa.

Anan kuma shiga ta kawo ga Mu’azu, shi ma aka soke shi. Ya shiga cikin wani irin magagi; ransa na zuwa yana dawowa. Amma hakan ba tasa ya fita hayyacinsa har yamanta da Allah. Duk lokacin daya farko za a ji yana cewa: Ya Ubangiji! A shirye nake mutuwa ta xauke duk lokacin daka shata. Kuma ka sani, wallahi ina matuqar son ka, har cikin quryar xakin birnin zuciyata.

Mu’azu kenan.

Haka ita ma cewar da xan Shi’ar yayi Ali Raliyallahu Anhu ya ce: “wallahi na taki sa’a” ba gare shi farau ba. An riwaito cewa Amiru xan fuhairiyatu; barwan Sahabi Abubakar Raliyallahu Anhu A wannan matsayi nasa, da bai kai na Aliyun ba. Shi ma ya faxi irin wannan kalma a lokacin da yake gab da xauke shexa, a wani wuri gab da Najdu, a sanadiyar sukuwar sallar da magabata suka yi kansa da makamai, a wannan wuri da Annabi Sallallahu Alaihi Wasallama ya tura shi tare da wata runduna.

Malaman tarihi suka ce, a wurin ne wani kafiri da ake cewa Jabbaru xan Salimi, ya kai masa suka ta qarshe, wadda ta kama jikinsa sosai, ya kuma tabbata lalle tashi ta qare. To a lokacin ne ya ce: “ wallahi na taki sa’a.” jin haka sai Jabbaru xin ya ce: me yake nufi da wannan magana? Sai Urwatu xan Zubairu ya ce: wannan sa’a ta tabbata domin kuwa mun ga mala’iku sun halarto jana’izarsa.

Haka kuma an riwaito cewa a lokacin da aka kaiwa Shubaibu al-Hariji suka, ta kama jikinsa sosai, shi ma ya ce: Allah ka karvi wannan shahada tawa.

To ba waxannan magabata ba. Ni xin nan na san wani mutum daga cikin amitattu, wanda a lokacin daya kai gargara sai aka ji yana cewa: ya masoyina ga ni nan isowa don mu sadu.

Wannan kalami ne Ya ci gaba da maimaitawa har ransa ya fita. Irin waxannan misalai akwai su da yawa.

Sannan kuma wancan tsoro da fargaba da suka kama Umar Raliyallahu Anhu a lokacin gargararsa, ba wani abu hakan ke tabbatarwa ba illa tsananin tsoron Allah, wanda ke tsatsage da birnin zuciyarsa. Wanda kuma ke nuna cika da kamalarsa a fagen ilimi. Saboda Allah Ta’ala ya ce: Malamai kawai ke tsoron Allah daga cikin bayinsa(35:28)

Kuma tsoron Allah da bayyanarsa sunna ce da ta samo asali daga Annabi Sallallahu Alaihi Wasallama Domin da yawa idan yana salla, ake jin qirjinsa na zavarvaka kamar tukunya ta tafasa, saboda tsananin kukan da yake shara.

Ita kuwa waccan magana ta Umar Raliyallahu Anhu da xan Shi’ar ya ce wai, daidai take da abin da kafiri zai ce gobe qiyama: Kaicona da ma turxaya aka yoni (79:40)

Wannan zumuncin da xan Shi’ar ya qulla tsakanin waxannan kalamai biyu, aiki ne irin na jahilai. Domin kuwa babu abin da ya haxa wannan magana da waccan saboda ta farko an yi tane a duniya; gidan da ake neman lahira a cikinsa. Kuma maganar na nufin tabbatar da tsoron Allah ne a cikin zuciyar Umar Raliyallahu Anhu ka ga kenan zai sami ladar haka daga wurin Allah. A yayin da ita kuma magana ta biyu za a yi tane a ranar qiyama; ranar da ba a karvar tuba kuma wani aiki mai kyau ba ya da wani anfani.

Ka ga ashe hanyar jirgi daban ta mota daban.

Kuma a irin wannan tafarki Sayyida Maryam tace: kaitona, da dai na mutu a gabanin wannan kuma na kasance wani abu walaqantacce wanda aka manta (19:23)

Ka ga babu mai hankali da ilimin da zai daidaita matsayin wannan gurin mutuwa da Maryam ta yi, a duniya, da wanda wani kafiri zai yi a lahira; kamar cewar da ‘yan wuta za suyi goben: Ya maliku! Ubangijinka ya kashe mu mana (maliku) ya ce, “ lalle ku mazauna ne (43:77) Da kuma gurin da waxanda sukayi zalunci a duniya za suyi a goben kamar yadda Allah Ta’ala ke cewa: kuma da waxanda suka yi zalunci suna da abin da ke cikin qasa gaba xaya, da misalinsa a tare dashi, lalle da sunyi fansa dashi daga mummunan azaba, a Ranar qiyama. Kuma abin da basu kasance suna zato ba, daga Allah ya bayyana gare su (39:47)

Ka ga waxannan ayoyi suna ba mu labarin halin da waxannan mutane za su kasance ne a ciki gobe qiyama ne kawai; ranar da tuba da tsoron Allah ba su da wani amfani.

Amma a nan duniya, sanannen abune cewa, a duk lokacin da bawa yayi tsoron Ubangijinsa, to yayi ibada. Wadda kuma Allah zai bashi lada a kai, Ya kuma amintar dashi gobe qiyama. Duk kuwa wanda ya daidaita matsayin wannan tsoron Allah da wancan, to, daidai matsayinsa yake dana wanda ya daidaita matsayin haske da duhu, ko inuwa da rana, ko na rayayyu da matattu.


Yüklə 2,75 Mb.

Dostları ilə paylaş:
1   ...   17   18   19   20   21   22   23   24   ...   51




Verilənlər bazası müəlliflik hüququ ilə müdafiə olunur ©muhaz.org 2024
rəhbərliyinə müraciət

gir | qeydiyyatdan keç
    Ana səhifə


yükləyin