Tafarkin sunnah



Yüklə 2,75 Mb.
səhifə22/51
tarix28.10.2017
ölçüsü2,75 Mb.
#17506
1   ...   18   19   20   21   22   23   24   25   ...   51

Sayyidina Umar:

2. 44 Umar: Mai Gani Da Hasken Allah

A wani yunquri kuma da xan Shi’ar yayi na bice haske da martabar Umar Raliyallahu Anhu, sai ya xauko zancen rubuta wasiyya, a matsayin makami, inda ya ce: Mawallafan ingantattun littafan hadisan na shida, sun riwaito daga Musnadin xan Abbas, wanda ya ce: Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama ya nemi Sahabbai, a lokacin da yake jinyar ajali, dasu kawo masa alqalami da farar takarda don ya rubuta masu abin da idan suka yi riqo da shi, ba za su vace ba a bayansa. Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama na bayar da wannan umurni, sai Umar ya ce: ina sa ran magagin mutuwa ne ya kama shi. Kuma ai littafin Allah ya ishe mu.

Umar na qare faxin haka sai wuri ya kece da hayaniya. Jin haka sai Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama ya ce: ku watse ku ba ni wuri, bai kamata kuna rikici gaba na ba. Daga nan kuma sai xan Abbas ya ce: Amma dai ba mu ji daxin hana Manzon Allah ya rubuta mana wannan wasiyya ba.

Abu na farko kenan.

Abu na biyu kuma inji xan Shi’ar shi ne, wai a lokacin da labarin rasuwa Manzon Allah ya bazu Umar Raliyallahu Anhu bai yarda ba, har ya ce: Muhammadu Sallallahu Alaihi Wasallama ba zai mutu ba sai ya yanke hannaye da kafafun wasu mutane. A nan ne Abubakar Raliyallahu Anhu ya ce ya kama bakinsa, ya kuma karanta masa ayar dake cewa: lalle kai mai mutuwa ne, kuma suma lalle masu mutuwa ne (39:30) da kuma wadda ke cewa: ashe idan ya mutu ko kuwa aka kashe shi, za ku juya akan dugaduganku? (3:144)

Qare karanta waxannan ayoyi da Abubakar Raliyallahu Anhu yayi ke wuya, sai Umar ya ce: Na ji kamar ban tava jin su ba .

Kafin mu shiga walwale bakin zaren wannan magana a matsayin martani, bari mu fara shimfida darajojin Umar Raliyallahu Anhu waxanda suka tabbata a cikin ingantattun hadisai. Waxanda za su sa mai karatu ya gane matsayinsa na wanda ke gani da hasken Allah. Kuma cewar da ya yi “wata qila magagin mutuwa ne ya kama Manzon Allah” hasashe ne irin na masu ilimi da hangen nesa.

Sayyidina Umar nada darajojin da babu wanda keda irinsu daga cikin Sahabbai in ba Abubakar Raliyallahu Anhu ba.

Ya zo a cikin sahihu Muslimu daga Aisha Raliyallahu Anhu wadda ta ce: Annabi Sallallahu Alaihi Wasallama ya kasance yana cewa: An yi mutane masu kyakykyawan hasashe a cikin al’umomin da suka gabace ku. Idan akwai irinsu xaya a cikin al’umma ta, to, Umar ne.

Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama yayi amfani ne da kalmar “muhaddisuna” a cikin wannan hadisi da wanda zai biyo bayansa. Kalmar Larabci wadda muka fassara da “kyakykyawan hasashe”. Mun yi haka ne ta hanyar shiga rigar arzikin malam da Wahabi, wanda ya ce: kalmar na nufin “waxanda Allah ke yi wa ilhamu”.

Haka kuma Buhari ya riwaito daga Abu Hurairata, wanda ya ce Annabi Sallallahu Alaihi Wasallama ya ce: An yi mutane masu kyakykyawan hasashe a cikin al’ummomin da suka gaba ce ku. Idan akwai wani irinsu a cikin wannan al’umma tawa to Umar xan Haxxabi ne.

A wani matakin kuma Buhari cewa yayi Annabi ya ce: An yi wasu mutane a cikin Bani Isra’ila; waxanda suka gabace ku, waxanda ke magana ta zama kata’un, tattare kuma da cewa su ba Annabawa ba ne. Da akwai xaya daga cikinsu cikin al’ummata , to Umar ne.

Haka kuma yazo a cikin wani hadisi ingantacce hadisi daga xan Umar, wanda ya ce, Annabi Sallallahu Alaihi Wasallama ya ce: watarana yayi mafarkin an zo mani da wata kwarya cike da nono. Na sha na qoshi, har a kaihuna suka nuna. Da na rage sai na miqawa Umar xan Haxxabi.

Sai Sahabbai suka ce: To da me ka fassara wannan nono ya Manzon Allah? Ya ce: Da ilimi.

A wani hadisi kuma sahihi, wanda aka samo daga Sa’id, wanda ya ce, Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama ya ce: watarana nayi mafarkin wasu mutane sanye da ‘yan guntayen tagguna da basu wuce qirazansu ba. Wasu kuma nasu sun xan gota nan. Can sai ga Umar xan Haxxabi tasa rigar har tana jan kasa.

Sai Sahabbai suka ce: To da me ka fassara wannan riga ta Umar ya Manzon Allah? Ya ce: Da faxaxxiyar addini a hannunsa.

Wannan kenan. To mu koma kan asalin wannan magana kuma. Wato abin can da Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama yaso ya rubuta wa Sahabbai a matsayin wasiyya. Wannan abu sananne ne baga Umar kawai ba. Domin kuwa Aisha Raliyallahu Anhu ta faxa a cikin wani ingantaccen hadisi, cewa Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama ya ce mata a liqacin da yake jinyar ajali: kira mani mahaifinki (Abubakar RALIYALLAHU ANHU) da xan’uwanki. Zan rubuta masu wata takarda. Don ina tsoron wani mai guri yayi guri, kuma mai cewa ya ce: Ni ne mafi cancanta. Amma Allah da muminai su qi kowa sai Abubakar.

Ya kuma zo a cikin sahihul Bukari daga Kasim xan Muhammadu, wanda ya ce: Aisha Raliyallahu Anhu ta xaga murya watarana tace: Boni ko zai ci fatun lihidda! Sai Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama ya ce: idan ina raye zan yi maki istigfari in kuma yi maki addu’a. Sai tace: kaicona! Wallahi ina zaton dai kana sone in mutu. Ina tabbata maka idan haka ta faru zan ci gaba da zama rataye ga wasu daga cikin matanka. Sai Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama ya ce: kenan ni bonin zai ci ba fatun lihidda ba. Haqiqa nayi nufin in aika wurin Abubakar da xansa don in danqa masa amana. Don kada gobe wani mai faxa ya faxa ko mai guri ya gurata. Qarshe kuma Allah da muminai Abubakar za su zava.

Ka ga kenan Annabi Sallallahu Alaihi Wasallama ya riga yayi ishara da abin can da yake son rubutawa, tare kuma da bayyana dalilansa a kan haka.

Wannan darga ta qare qarau ga mai hankali. Shi kuwa Umar kokwanto ne ya kama shi a kan haqiqanin matsayin waccan magana da Annabi Sallallahu Alaihi Wasallama yayi; shi yayi ta ne a sakamakon zafin ciwo da kusantowar ajali, koko yana cikin hayyacinsa?!

Wannan hasashe da Umar Raliyallahu Anhu yayi ba laifi ba ne. Domin tabbas Annabawa na arashin lafiya. Kuma ko ba komai halin da Manzon ke ciki ya isa tabbatar da haka. Kuma kalmar “ina sa rai” wadda ya yi amfani da ita a lafazin nasa, na nuna cewa bai yanke wa matsalar hukunci ba; a’a yana dai kokwanto da hasashe ne. Ka kuma sani Umar bai fi qarfin kokwanto ya kama shi ba, tun da shi ba Annabi Sallallahu Alaihi Wasallama ne ba, wanda Allah ya ba lasisin ma’asumanataka. Kuma wannan kokwanto daya kama shi, an yi sa’a yana wurin zama a cikin al’amarin, tunda ga Annabi kwance kuma ribxe a cikin zafin masassara. Saboda haka yayi hasashen ko zafin ciwo ne yasa shi maganar, ta yadda ake iya yin wani xan batun zucci kafin a saurareta kai tsaye. Koko karvar ta nan take wajaba, ba tare da wani nazari ba?! Kamar dai yadda ya yi kokwanton tabbacin mutuwarsa daga baya, har sai da ya gama gane lalle dai ya rasun, sannan ya miqa wuya.

Kuma ka ga cikin ikon Allah, sai abin can da Umar Raliyallahu Anhu ke hasashe ya tabbata. Wato abin can da manzo yaso rubutawa, ya riga ya faxawa Nana Aisha Raliyallahu Anhu shi. Saboda haka ne ma daya ga ruxani ya shiga tsakanin Sahabbai a kan abun, ya kuma san ko da ya nace a kan sai ya rubuta maganar, hakan ba zai kawar da ruxanin ba, tunda ya riga ya faru, sai ga fita batun hakan. Ya kuma san cewa Allah zai haxa kansu a kan abin da ya yi niyyar rubuta masun. Kamar yadda ya riga ya faxa cewa: qarshe kuma Allah da muminai Abubakar za su azaba Raliyallahu Anhu.

Ita kuwa cewar da xan Abbas yayi: Bamu ji daxin hana Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama ya rubuta mana wannan wasiyya ba..... magana ce dake nuna rashin jin daxin zai tabbata cikin qirazan waxanda ba su yarda da halifancin Abubakar Raliyallahu Anhu ba samsam. Ko kuma suka yi shakkunta. don tabbas da rubutun ya yiwo, da abin da ya farun nan bai faru ba.

Amma duk wanda ke da masaniya da barwa Abubakar Raliyallahu Anhu amanar al’umma, da Annabi yayi, ba wani rashin jin daxi gare shi.

Alhamdu lillahi

Rashin jin daxi na nan ga waxanda ke zaton cewa Annabi Sallallahu Alaihi Wasallama yaso ne ya rubuta cewa Ali Raliyallahu Anhu ya gade halifarsa kai tsaye bayan ya qaura. Kuma vattatu ne bisa haxuwar kan gaba xayan malaman sunna da na Shi’ah.

Eh! Tabbas haka wannan magana take. Domin kuwa malaman sunna sun haxu a kan cewa Abubakar Raliyallahu Anhu shi ne mafifici a cikin Sahabbai, kuma shi ne mafi cancanta da halifanci a lokacin. A yayin da su kuwa malaman Shi’ah, waxanda ke ganin cewa Ali shi ne mafi cancanta da kujerar a lokacin, cewa suke yi Annabi Sallallahu Alaihi Wasallama ya riga ya daddale maganar kasancewar Alin yazama mai jiran gadon manzanci, da yankakken “nassi” tun kafin wannan lokaci na jinyar. Ka ga kenan ba bukatar wani rubutu.

To ina suka ga makama? Babu

Kuma da ‘yan Shi’ah za su ce: A’a akwai buqatar Annabi Sallallahu Alaihi Wasallama ya rubuta waccan naxi da ya yi wa Ali Raliyallahu Anhu duk da yake yayi shi ne a cikin dubu; Don gudun kada al’umma ta musa nan gaba.

To shi mu karva masu da cewa, duk al’ummar da ke iya musanta abin da aka yi (magana) cikin dubu, to musa wanda aka yi (rubutu) cikin ‘yan kwarorin mutane yafi sauqi da cancanta gare ta.

Kuma muna nan akan bakar mu, na cewa in dai har wancan nassi (magana) ya inganta, to babu buqatar wannan rubutu yanzu. Saboda baya halatta ga Annabawa su jinkirta wata magana (saqon Allah) har sai lokacin mutuwasu. kuma da wajibi ne a kan manzon ya rubuta waccan wasiya, shakku da kokwanto da hayaniyar da Sahabbai suka sami kansu a lokacin ba ta hana ya dage a kan sai an kawo kayan rubutun ya rubuta; maganar Umar Raliyallahu Anhu ko wani daga cikinsu duk ba za ta hana shiba, a matsayinsa na mafi xa’a ga Allah daga cikin bayinsa.

Ka ga fita batun rubutun da Sallallahu Alaihi Wasallama ya yi ya tabbatar da cewa ba wajibi ba ne. Ba kuma wani abu ne mai muhimmanci a addini ba, wanda rubuta shi a lokacin ke wajaba. Don da haka ne, da ya yi.

Kuma shi Umar ya riga ya gama leqen cewa abin ba wani abu bane. Don inda wani abu ne, kuma Annabi ya zartar da hukuncin lalle sai ya rubuta shi, lalle Umar Raliyallahu Anhu a matsayinsa na mai hasashe (ijtihadi) kawai ba zai yi gangancin wandarewa ba. Kokwanton da ya aure shi a kan gaba xayan lamarin ko sashensa; daga baya, ba zai ba shi damar yin haka ba. Ko banza kokwanto a kan kasancewar abin da yake gaskiya gaskiya, ya fi sauqi bisa ga yanke masa hukuncin zama qarya.

Ina fatar dai ka gane.

To kuma tafi naji. A matsayin Umar Raliyallahu Anhu na mai ijtihadi iyakar abin da za’a iya cewa yayi na rashin sa’a shi ne, kuskure. Allah kuwa ba ya kama mai ijtihadi da wani laifi don ya kuskure daidai. Kamar yadda ba zai kama Ali Raliyallahu Anhu da kuskuren da ya yi a cikin ijtihadi, ya wajabta ma wata mata da mijinta ya rasu yin iddar mutuwa ta tsawon mafi tsawon iyakoki biyu ba. Tattare kuma da abin da ya tabbata ya kuma inganta daga Annabi Sallallahu Alaihi Wasallama shi ne cewa a lokacin da aka ba shi labarin cewa Abus-Sanabilu ya yi wa Subai’atul-Aslamiyyah irin wannan fatawa. Sai Annabi ya ce: Qarya Abus-Sanabilu ke yi. Jeki ki auri duk wanda kike so kin halatta.

Annabi Sallallahu Alaihi Wasallama ya qaryata Abus-Sanabilu ne, saboda bai isa yin ijtihadi ba. Musamman ma da yake Manzo na kusa.

Amma ka ga ba za’a qaryata Ali da xan Abbas Raliyallahu Anhuma ba, saboda sun bayar da irin wannan fatawa. Domin sun bayar da ita ne bayan rasuwar Annabi Sallallahu Alaihi Wasallama kuma ba su da masaniya da wannan qissa ta Subai’atu.
2.45 Halifa Umar ba Azzalumi ba ne

A wani qoqari kuma na cin mutuncin Umar Raliyallahu Anhu da tozarta shi, sai xan Shi’ar ya yi masa qazafin zalunci, da wasu siffofi da halaye na naqasa. Inda ya ce wai, bayan da nana Fatima Raliyallahu Anha ta yi wa Abubakar Raliyallahu Anhu gargaxi a kan abin da ya shafi Fadak, sai halifan ya rubuta takarda, wadda ke nuna ya mallaka ma ta qasar; ta fita hannun kowa daga wannan lokaci. Wai kuma fitowarta daga wurinsa ke da wuya, sai ta yi kicivis da Umar Raliyallahu Anhu wanda ya qwace takardar daga hannunta ya qona. Wannan abu ya dugunzuma ranta sosai. Nan take ta yi ma sa baqar addu’a da “Allah ya isa”. Wai kuma sakamakon wannan addu’a ne, Abu Lu’alu’ata ya yi wa Umar abin da ya yi masa.

Kuma xan Shi’ar ya ci gaba da cewa: Haka kuma saboda rashin sanin hukunce-hukuncen shari’a, Umar ya yi wa haddin Allah wanda ya hau kan Mugiratu xan Shu’ubata targazo, ta hanyar qin hukunta shi. Kuma ya kasance yana bai wa sauran matan Annabi Sallallahu Alaihi Wasallama fiye da abin da suka cancanta daga Baitul-Mali. Amma sai ya ba wa Aisha da Hafsatu Raliyallahu Anhuma dirhami dubu goma kowace shekara. Ya kuma canza hukuncin Allah a kan waxanda aka kora.
Martani:

Ko shakka babu wannan magana baqar qarya ce, irin wadda ba masanin da zai kokwanton ta. Domin babu wani malamin hadisin da ya tava riwaito ta, balle a iya gane isnadinta. Kuma tabbataccen abu ne, Abubakar Raliyallahu Anhu bai tava tabbatar wa Fatima Raliyallahu Anha ko wani mallakar qasar Fadak ba. Kuma ba ta yi wa Umar wata baqar addu’a ba.

Kuma ko shakka babu abin da ya faru ga Umar Raliyallahu Anhu na kisan gillar da Abu Lu’alu’ata ya yi masa, wani karamci ne daga wurin Allah Ta’ala irin wanda Ali da Husaini Raliyallahu Anhuma ba su samu ba. Eh! Ba su samu wannan karimci ba mana. Tunda xan Muljamu da Yazidawa waxanda suka kashe su, musulmi ne ‘yan‘uwansu. Shi kuwa Abu Lu’alu’ata, makashin Umar Raliyallahu Anhu kafiri ne baqin. Ka kuwa san ba abin mamaki ba ne kafiri ya kashe musulmi, balle ma halifa sukutum. Ai ko banza babu abin da ke tsakanin mumini da kafiri sai yaqi.

Saboda haka ne shahadar wanda ya rasa ransa hannun kafiri ta fi ta wanda ya rasa nasa hannun musulmi xan’uwansa girma da karvuwa a wurin Allah. Kuma ta yaya ne ma za’a iya gane cewa addu’ar da Fatima wai ta yi wa Umar xin Raliyallahu Anhu ce sanadiyyar kisan nasa, tunda sayyidar ta rasu ne bayan halifancin Abubakar da wata shidda kafin qarewar na Umar Raliyallahu Anhu ka ga abin na da kamar wuya.

To, kuma ko qaddarawar muka yi Nana Fatima ta yi wa Umar xin waccan baqar addu’a, ta fatar ajalinsa ya kasance hannun kafiri. Ai wannan abin alheri ne da alfahari ta roqa ma sa. In kafiri bai kashe shi ba sai rayuwarsa ta xore? Ai irin wannan addu’a ce Annabi Sallallahu Alaihi Wasallama kan yi ga Sahabin da matsayinsa ya kai gare shi, wato ya roqar masa shahada. Har ma Sahabbansa suka gano cewa, da zaran sun ji Manzo ya ce: “Allah ka yi gafara ga wane”. To sun san shahadarsa ta kusa. Saboda haka ne ma, wani lokaci sukan katsi nunfashinsa, idan ya yi wa wani Sahabi irin wannan addu’a, su ce: ya Manzon Allah! Ba mu gaji da ganinsa ba.

Haka kuma a da ‘yan Shi’ah za su dage a kan cewa lalle sakamakon zaluncin da Umar Raliyallahu Anhu ya yi wa Fatimar ne da baqar addu’ar da ta yi masa, wancan abu ya faru gare shi. To, sai mu ce masu: Idan dai har hankalin masu hankali zai karvi wannan magana taku, to, ba zai kasa karvar ta wanda ya ce: kisan gillar da xan Muljam ya yi wa Ali Raliyallahu Anhu ya faru ne sakamakon zaluncin da ya yi wa mutanen Siffin da Harijawa da “Allah ya isa”r da suka yi masa. Kuma Abu Sufyana da Harisu ne suka yi wa Husaini baqar addu’a, ta zama sanadiyyar kashe shi a karbala.

Ita kuma cewar da xan Shi’ar ya yi, wai Umar ya yi wa hukuncin Allah targazo, ta hanyar qin yi wa Mugiratu xan Shu’ubata haddi, qarya ce. Domin kuwa jumhurun malamai sun karvi abin da halifan ya yi a cikin wannan sha’ani da hannu bi-biyu; wato yi wa sauran shedu haddin qazafi, idan suka kasa cika. Kuma sauran malaman da ke ganin ba haka ya kamata hukuncin ya kasance ba, sun gamsu da cewa mas’alar ta ijtihadi ce.

Sannan kuma, kamar yadda muka faxa a baya; abin da Ali Raliyallahu Anhu yayi na qyale makasan halifa Usmanu ba tare da ya hukunta su ba. Shi ne yi wa hukuncin Allah targazo, ba wannan ba. Idan kuwa kuna ganin mai wannan ra’ayi; na ganin laifin Ali, ya yi varna. To, wanda ke ganin laifin Umar Raliyallahu Anhu a cikin waccan mas’ala shi ne babban mavarnaci, bisa la’akari da matsayi da banbancin mas’alolin biyu.

Haka kuma, xan Shi’ar ya soki halifan da cewa, yana ba wa sauran matan Annabi Sallallahu Alaihi Wasallama fiye da abin da suka cancanta daga Baitil-Mali. Amma Nana Aisha da Hafsatu sai ya ba su dirhami dubu goma-goma kowace shekara...

Martani: Da Allah ya sa xan Shi’ar nan na cikin masu hankali, to da ya fahimci cewa, ai wannan abu da halifan ya yi, wani abu ne da ke nuna cikar taskai da adalci. Tare da haxuwarsa da Allah, ta hanyar hana zuciyarsa abin da take so.

Kai ka san in ba haka ba, babu abin da zai sa ya fifita wata a kan ‘yar cikinsa a cikin wannan sha’ani na dukiya. Shi a hankali da tunaninsa Hafsatu ‘yarsa da Abdullahi xansa, ba su isa su yi kafaxa-da-kafaxa da sauran matan Annabi Sallallahu Alaihi Wasallama da mutanen gidansa ba, balle su karvi daidai abin da su suke karva. Daxa balle ma su wuce su, don Ubansu ne halifa.

Tirqashi ka ji masu tuqen dabaibiya malam.

A fahimtar halifa Umar Raliyallahu Anhu arzikin qasa ana raba shi ne ga jama’a gwargwadon girma da xaukakarsu. Saboda haka ne shi, a duk lokacin da ya tashi rabo, sai ya fifita matan Annabi Sallallahu Alaihi Wasallama a kan sauran mata. Kamar yadda yake fifita Banu Hashim; wato Aliyu xan Abu Xalib da Abbas da sauransu, a kan sauran qabilun da ba su ba.

Duk wanda Umar Raliyallahu Anhu ya fifita a cikin wannan al’amari na rabon arzikin qasa, to za ka taras makusancin Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama ne. Ko kuma yana daga cikin na sahun farko a shiga musulunci. Ko kuma yana da wani abu na bajinta ko mai kama da haka, wanda zai sa ya cancanci wannan fifiko. Har ma an riwaito yana cewa: Babu wanda ya fi wani cancanta da wannan arziki a cikinmu; ina dai la’akari ne da buqatar mutum, ko hidimarsa ga addini, ko sammakosa a cikinsa, ko wadatarsa.

Waxancan mata na Annabi Sallallahu Alaihi Wasallama da xan Shi’ar ke zargin Umar Raliyallahu Anhu da basu kuxi mai yawa. Halifan bai yi hakan don tsoron wani abu ko rojin wani ba. Don babu wata dangantaka tsakaninsa balle a ce. Kuma ka ji irin ma yadda ya yi da ‘ya’yan cikinsa, da makaman tansu. Ba ya fifita mutum sai don wani dalili na addini tsantsa. Kuma ko a hakan ma yana fifita mutanen gidan Annabi Sallallahu Alaihi Wasallama tare da farawa dasu, a kan mutanen sauran gidaje. Kuma babu wanda ya bi sawun Umar Raliyallahu Anhu a cikin wannan kyakyawan aiki, daga cikin Usman da Ali Raliyallahu Anhu halifofin da suka zo bayansa, ko wasunsu.

Idan kuwa har za’ayi wani qorafi a kan Umar, kan fifita waxancan mata na Manzo, to sai a kuma yi qorafi a kan fifita Ahlul-Baiti da ya yi a kan wanda ba su ba, tare da gabatar da su. Koko?
2.46 Gargaxi ne ba Haddi ba

Xan Shi’ar ya ci gaba da cewa wai kuma: Umar Raliyallahu Anhu ya canza hukuncin Allah a kan waxanda ake kora saboda aikata wata kaba’ira.



Martani: Da xan Shi’ar nan ya san cewa, canza hukuncin Allah na tabbata ne a lokacin da aka xauke shi, aka kuma maye gurbinsa da abin da ke walwale shi. Kamar haramta abin da Allah ya wajabta ko halatta abin da ya haramta. Da bai faxi wannan magana ba.

Shi kuwa korar da shari’a ta yarda a yi wa wanda ya sha giya misali, gargaxi ne ba haddi ba. Kuma gargadi a shari’a wani fage ne na ijtihadi. Musamman a kan shan giya. Domin kuwa har Annabi Sallallahu Alaihi Wasallama ya kwanta dama, bai daddale haddin mashayin giya ba ta fuskar yawan abin da za a yi ko siffarsa. Iyakar abin da aka san ya bar wa musulmi a matsayin sunna, shi ne; dukan mashayin da ganyen dabino da takalmi da wutsan tufafi, har ya yi tivis. A yayin da ake bulale mai qazafi da mazinaci.

Abin da Sahabbai suka gada kenan a wannan vangare. Wato “dukan” mashayin giya. Amma vangaren adadin dukan (buloli) Sahabban sun yi amfani da basira, ilimi da gogewarsu, a matsayin ijtihadi. Wasu daga cikinsu suka yi bulala arba’in, wasu kuma tamanin.

Kuma hadisi ingantacce ya tabbata cewa, Ali Raliyallahu Anhu ya ce: kowane adadi aka xauka an yi Sunnah.


2.47 Allah Ne Kawai ba ya Mantuwa ba ya Kure

A nan kuma Xan Shi’ar cewa yake yi, wai Umar Raliyallahu Anhu kamar Abubakar ne. Shi ma masaniyar da yake da ita da hukunce-hukuncen shari’a ‘yar qanqanuwa ce; saboda wai ya yi umurni da a jefe wata mata da ke da juna biyu, saboda kama ta da laifin zina da aka yi. Sai wai Ali Raliyallahu Anhu ya ce ma shi, idan kana da hujjar sa a kashe ta, to ba ka da hujjar sa a kashe xan da ke cikinta. Wai saboda haka sai Umar Raliyallahu Anhu ya janye umurnin, har kuma ya ce: “Wallahi ba don Ali ba yau da Umar ya halaka”.



Martani: Babu wani abu qasa, da ke tabbatar da kasancewar wannan qissa gaskiya. To kuma ko da mun qaddara kasancewarta hakan, to lalle ne xayan biyu; ko dai ya kasance Umar bai san matar na da juna biyu ba, sai da Ali ya labarta masa Raliyallahu Anhu, ka ga kenan rashin sani ya shiga. Kuma faxakar da shi, da Ali ya yi a kan haka, kamar abin da aka saba ne na, muqarraban shugaba su faxakar da shi a kan abubuwan da suka shige masa duhu, na halayen talakawansa. Ko kuma irin abin da shedu zai bayyana a gabansa. Babu kuwa wani Annabi ko shugaba da ba ya da buqata da irin wannan gudunmawa ta alheri. Hakan kuma ba ya daga cikin hamshaqan hukunce-hukuncen shari’a.

Na farko kenan. Ko kuma a’a ya san da matar na da juna biyu. Amma ya sha’afa da cewa ba a jefe irinta sai ta sauka. Da kuma Ali Raliyallahu Anhu ya tunatar da shi, sai ya gamsu. Ka ga ba zancen rashin sani a nan, sai dai sha’afa. Don da ace ya riga ya gamsu da halaccin jefe irinta, to, babu wanda ya isa ya hana shi zartar da hakan, a matsayinsa na mujtahidi. Tattare da masaniyar da yake da ita da cewa, Annabi Sallallahu Alaihi Wasallama ya umurci Gamidiyyah da ta je sai bayan ta sauka, ta dawo a zartar ma ta da haddin zinar da ta yi iqirarin ta yi har ta xauki ciki.

To, kuma ai ba abin mamaki ba ne, don wannan mas’ala ta shige wa Umar Raliyallahu Anhu duhu. Kuma ba abu ne da ya kamata a soke lamarinsa a kai ba. Domin kuwa Allah ne kawai ba ya mantuwa ba ya kure, Subhanahu WaTa’ala. Kuma halifa irin Umar, barde, jarumi uban jarummai, kamata yayi a yi masa kyakkyawan zato. Musamman idan aka yi la’akari da yadda ya shugabanci musulmi da kafiran amana. Ta hanyar ba wa kowa haqqinsa, da zantar da haddoda. Da zama Alqalin gaba xayan jama’a, da irin yadda musulmi ya sami ranar baje garinsa a zamaninsa, irin yadda bai samu ba kafinsa.

Babu wani lokaci da za ka taras da halifa Umar Raliyallahu Anhu face, ko dai yana fatawa, ko yana Alqalanci. Ka kuwa san mai cikin cokalin ilimi ba zai iya haka ba ko alama ko?!

To tunda kuwa haka ne, ashe ba aibi ba ne don mai irin wannan fama, ya manta mas’ala xaya daga cikin mas’aloli dubu xari ko fiye, sai da aka tuna masa. Kai! xauki ma bai san ta ba sai da aka sanar da shi. Ai duk xan Adamu ajizi ne.

Kuma ai tabbataccen abu ne, cewa mas’alolin da suka shige wa Ali Raliyallahu Anhu duhu, daga cikin sunnar Manzon Allah, sun fi a qirga. Wasu ma har ya mutu bai san su ba.

Ina fatar baka jahilci haka ba?
2.48 Halifa Umar ba Jahili ba ne

Wata sukar lamirin kuma, mai kama da waccan itace cewar da xan Shi’ar yayi kai tsaye, wai halifa Umar jahili ne. Saboda ya yi umurni da a jefe wata mahaukaciya saboda samunta da laifin zina da aka yi. Sai da Ali Raliyallahu Anhu ya faxakar da shi cewa, an xauke Alqalami daga kan mahaukaci, har sai ya warke. Jin haka sai Umar ya janye umurnin, kuma ya ce: “Wallahi ba don Ali ba da Umar ya halaka”.



Martani: kafin mu shiga fashin baqin wannan magana a matsayin martani, muna tabbatar wa xan Shi’ar da cewa; Eh! Wannan mas’ala, gaskiya ne ta faru. Amma wannan magana ta cewa Umar xin ya ce ba don Ali ba da ya halaka qari ne; babu ta a cikin lafiyayyar ruwaya.

Nan kenan. Kuma lalle ne Umar Raliyallahu Anhu bai san waccan mata mahaukaciya ce ba. Ko kuma ya sani amma ya sha’afa. Saboda haka ya yi umurni da zartas ma ta da haddin. Amma da aka faxakar da shi ya gamsu ka ga ba abin sukar lamiri a nan.

Koko a’a, halifan ya fahimci cewa haddodin da ake zartarwa a kan masu lafiya, ana zartar da su ne, don alqinta rayuwar duniya, ta hanyar hana wani cutar da wani. Saboda haka babu dalilin da zai hana a hukunta mahaukaci, matuqar ya zo da wani mugun aiki da ke iya cutar da jama’a; waxanda suka haxa da masu hankali da mahaukata. To, tunda kuwa zina mugun aiki ce, da ke cutar da al’umma, lalle, idan mahaukaci ya yi ta a hukunta shi. Amma daga baya sai aka faxakar da shi cewa, irin wannan haddi na zina, haddi ne da Allah Ta’ala bai yi umurni da zartarwa ba, sai a kan mukallafai.

Wannan kenan. Wani abu kuma da ke iya zama madogara, ga halifan a kan wannan ijtihadi nasa, shi ne horon da shari’a ta yi na ladabtar da qananan yara, ta hanyar duka idan suka qi yin sallah. Har Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama ya ce: “Ku hori yara da yin sallah suna ‘yan shekara bakwai. Ku kuma doke su, idan suka qi, in sun shekara goma. Ku kuma rabe masu shinfixun bacci”.

Bayan wannan kuma, ai ba mutumin da ba ya da hankali ba, ko dabba, a shari’a idan tana fitinar jama’a, daidai ne a kashe ta. Haka idan mahaukaci na fitinar jama’a shi ma aka rasa yadda za ayi da shi a yi maganinsa, sai ta hanyar kisa, ya halatta.

Kuma, waccan dabba da za’a kashe bisa wancan dalili, idan ta gida ce kuma mallakar wani, ba za’a biya shi diyyarta ba, bisa ra’ayin Jumhurun malamai, irin su: Maliku da Shafi’i da Ahmadu da wasunsu.

A taqaice, duk abubuwan da xan Shi’ar nan ya ambata na suka ga Umar Raliyallahu Anhu ko waninsa daga cikin Sahabbai, na kawai tabbatar wa mai hankali da ilimi, xayan abubuwa biyu ne: 1) ko dai ya kasance xan Shi’ar ya faxe su, sakamakon fama da ciwon qarancin ilimi. Ko 2) tsanar wannan bawan Allah da qarancin kishin addini.

Dalili kuwa shi ne, ya xauka cewa halifan ya hana Fatima haqqinta, ya kuma yi son zuciya a cikin rabon arzikin qasa, ya kuma yi wa hukuncin Allah tasgaro da makamantan wannan.

Ka ga a taqaice yana so ne ya ce halifan ba adili ba ne. Alhali kuwa babu inda labarin adalcin Umar Raliyallahu Anhu bai kai ba a faxin duniya. Ta yadda har ma ake buga misali da shi; ana cewa: A yi koyi da rayuwar Umarora biyu. Maganar da malamai irin su Ahmad xan Hmbali da wasu malaman hadisi suka fassara da cewa; ana nufin Umar xan Haxxabi ne da Umar xan Abdulaziz. A ya yin da Abu Ubaidata da wasu malaman Lugga da Nahawu, suka ce: Umarun na biyu na nufin Abubakar ne Raliyallahu Anhu.

A taqaice dai, Umar xan Haxxabi ya tabbata adali.


Yüklə 2,75 Mb.

Dostları ilə paylaş:
1   ...   18   19   20   21   22   23   24   25   ...   51




Verilənlər bazası müəlliflik hüququ ilə müdafiə olunur ©muhaz.org 2024
rəhbərliyinə müraciət

gir | qeydiyyatdan keç
    Ana səhifə


yükləyin