Tafarkin sunnah



Yüklə 2,75 Mb.
səhifə4/51
tarix28.10.2017
ölçüsü2,75 Mb.
#17506
1   2   3   4   5   6   7   8   9   ...   51

Zango Na Xaya

Yan Shi’ah da Aqidunsu



1.0 Malamai ku Bayyana Gaskiya

Duk lokacin da mabiya suka fara la’antar magabata, bayyanar da ilimi ya zama tilas. A lokacin da aka isko ni da wannan littafi wanda malamin Shi’ah ya rubuta aka kuma neme ni da mayar masa da martani, da yake, ba a ce ma maci dambu ya sha ruwa, sai na feqe alqalami kuma na jawo tawwada na shiga rubutu, ina mai fatattakar varna da vatan da suke neman bazawa, domin kange muminai daga faxawa cikin tarkonsu. Rashin yin hakan kuma, yana sa ‘yan barandar, karkatattu su zaci ko kasawa aka yi. Shi ya sa na himmatu ga rubuta abin da ya sawwaqa don cika alqawarin nan da Allah ya riqa ga malamai, domin tabbatar da adalci da ba da shaida domin Allah. Kamar yadda Allah Maxaukakin Sarki ya ce;

ﭽ ﭑ ﭒ ﭓ ﭔ ﭕ ﭖ ﭗ ﭘ ﭙ ﭚ ﭛ ﭜ ﭝ ﭞ ﭟﭠ ﭡ ﭢ ﭣ ﭤ ﭥ ﭦ ﭧ ﭨﭩ ﭪ ﭫ ﭬ ﭭ ﭮﭯ ﭰ ﭱ ﭲ ﭳ ﭴ ﭵ ﭶ ﭷ ﭸ ﭹ ﭺ ﭼ النساء: ١٣٥

Ya ku waxanda suka yi imani! Ku kasance masu tsayuwa da adalci, masu shaida saboda Allah, kuma ko da a kan kawunanku ne, ko mahaifa da mafi kusantar zumunta, ko (wanda ake yi wa shaida ko ake shaida a kansa) ya kasance mawadaci ko matalauci. To Allah ne mafi cancanta da al’amarinsu. Saboda haka kada ku bibiyi son zuciya, har ku karkata. Kuma idan kuka karkatar da magana, ko kuwa kuka kau da kai, to lalle ne, Allah ya kasance Masani ga Abin da kuke aikatawa1

A cikin wannan aya an yi amfani da kalmar Layyu wadda ke nufin canzar da shaida da kuma kalmar I’rad; voye shaida da rashin bayyanar da ita, wanda dukan yin haka laifi ne da bijire ma gaskiya, wanda zai jefa mutane ga ramin halaka.

Babu shakka Allah ya yi umurni da abi gaskiya, a fayyace lamurra kamar yadda suke. Ya kuma yi hani daga yin qarya da kwana- kwana ko munaqisa ga abin da ya zama tilas ne a fitar da shi fili. Hadisi ya zo a cikin Buhari da Muslimu cewa; Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama ya ce “Masu cinikayya suna da zavi matuqar suna tare. Idan suka yi gaskiya sai a sanya albarka cikin cinikinsu. Idan kuwa suka yi qarya suka voye aibi sai a shafe albarkar cikinsu”.2

Wane mutum! Wannan fa game da ciniki kenan, ballantana ga voye Ilimi musamman irin lokacin da bidiar la’antar magabatan wannan al’umma ta bayyana. Ai ko alama, ba zai kyautu ba aji shiru kamar an aiki bawa garinsu. Bayani ya zo cikin wani hadisi cewa; “Duk sadda ‘yan bayan wannan al’umma suka la’anci magabatansu, dole ne masu ilimi su yi magana. Wanda ya voye ilimi a wannan lokaci, dai dai ya ke da wanda ya voye abin da Allah ya saukar wa Muhammadu Sallallahu Alaihi Wasallama”.1 Abin kulawa a nan shi ne, su fa jama’ar farko na wannan al’umma, su suka yi tsayuwar gwamin jaki a kan ganin cewa wannan addini ya samu kafuwa da yaxuwa a duniya baki xayanta. Don haka, duk wata suka da aka yi gare su ta na komawa ne kai tsaye ga addinin musulunci. Wannan kuwa shi ne ummul-haba’isin bijire ma abin da Allah ya aiko Manzonni da Annabawa da shi. Dama kuma shi ne matuqar gurin ‘yan Shi’ah; watsa gubar aqidar Shi’ancinsu a sassan duniya. Dabarun da suke yi kuwa domin su cimma nasara ga wannan baqar anniya tasu shi ne, sukan rava ne su zagayo ta bayan manyan kangararrun mutane maqiya addinin Allah. Sai su kai farmaki ga wuraren da suka fahimci cewa, musulmi suna da rauni, sai su baje kolinsu a wannan nahiya. Kaico! Abin tausayi da juyayi, shi ne irin yadda ‘yan Shi’ah ke ribantar wasu ta hanyar amfani da shubuhohi na jahilci da biyar son rai waxanda su ne manyan sinadarai ga kowane irin vata. Allah ya kiyashe mu. Allah Ta’ala Ya ce:

ﭽ ﭑ ﭒ ﭓ ﭔ ﭕ ﭖ ﭗ ﭘ ﭙ ﭚ ﭛ ﭜ ﭝ ﭞ ﭟ ﭠ ﭡ ﭢ ﭣ ﭤ ﭥ ﭼ النجم: ١ - ٤

Ina rantsuwa da tauraron, a lokacin da ya faku. Ma’abucinku bai vata ba. Kuma bai qetare haddi ba. Kuma ba ya yin magana daga son zuciyarsa. (maganarsa) ba ta zamo ba face wahayi ne da ake aikowa”.2

A nan ka ga sai Allah ya yabi Manzonsa yabo na musamman, ta hanyar tsarkake shi daga vata da halaka. Vata kuwa a nan, tana nufin jahilci. A yayin da halaka ke nufin biyar son zuciya. Kamar yadda Allah Mabuwayi ya ce:


ﭽ ﯫ ﯬﯭ ﯮ ﯯ ﯰ ﯱ ﯲ ﭼ الأحزاب: ٧٢

Kuma mutum ya xauke (amana). Lalle shi (mutum) ya kasance mai yawan zalunci, mai yawan jahilci”.3

Wannan aya ta fayyace sarai cewa, azzalumi halakakke ne, a inda shi kuma jahili vatacce ne, in ba wanda Allah ya yi wa gyaxar dogo ta hanyar tuba ba.

Na’am Wannan ba shakka shi ne halin ‘yan bidi’a waxanda suka nisanta kansu daga littafin Allah da sunnar Manzonsa tsira da amincin Allah su tabbata gare shi. Ba su biyar komi in ba zato ba da abin da rayukansu ke so.4 Qungiyoyin vata a wajensu ne jahilci da zalunci suka yanke cibiya, tun ma ba mafiya lalaci daga cikinsu ba, ina nufin ‘yan Shi’ah. Abin da ya kai su ga wannan matsayi kuwa shi ne, kai wa matuqa da suka yi wajen bayyana mummunar qiyayya ga manyan masoya Allah watau Sahabbai, muhajiruna da Ansaru. Allah ya yarda da su da duk waxanda suka bibiyi hanyarsu da kyautatawa.

Wani abin lura a nan shi ne, abu ne sananne cewa, ‘yan Shi’ah suna da qwaqqwarar hulxa da taimakekeniya a tsakanin su da kafirai da munafukai daga cikin Yahudawa da Kiristoci da Majusawa maqiya musulunci, da sauran fanxararrun qungiyoyi irinsu Nusairiyyah da Isma’iliyyah. Kuma kowa ya san cewa, sai hali ya zo daidai ake qulla abota. Ma’aunin gano wannan matsayi nasu kuwa abu ne mai sauqi. Za ka taras da su a duk lokacin da wani savani ya abku tsakanin Muminai da Kafirai suna gaugawar kai xauqi da agaji na musamman ga abokan faxan musulmi, kamar dai yadda aka sha ganin hakan a fayafayin tarihin duniya.

Sun tallafa wa maqiya musulunci na qasar Turkiyya a kan musulmin qasashen Khurasana da Iraqi da Jazira da kuma qasar Sham. Sun kai gagarumin taimako ga Kiristoci, aka yaqi Musulmi a qasar Sham da Masar da sauran qasashe, kuma hakan ta sha faruwa a lokuta daban- daban. Ai ko ka san ba zai yiwu musulmi su manta da irin wannan ta’asar ba. Da yawa-yawan ta’addancinsu ya abku ne a qarni na huxu da na bakwai, lokacin da kafiran Turkawa suka kutsa cikin garuruwan musulmi suka kashe adadi mai ximbin yawa, waxanda Allah ne kaxai masanin iyakar su. To, a wannan lokaci ‘yan Shi’ah sun taka rawa wadda babu waiwaye cikinta inda aka tursasa musulmi aka ci zarafinsu ainun, duk saboda gudummuwar shugabannin sharri na mabiya Shi’ah. wannan shi ne dalilin da ya sa ake yi musu suna da karnukan farautar Yahudawa.1
1.1 Zumuntar Shi’ah da Yahudawa da Nasara

Minhajul Karamah Fi Ma’arifatul Imamah, shi ne sunan littafin da nake baka labari a fasalin da ya gabata, wanda marubucin Shi’ah ya Wallafa. Ni dai a ganina da an ba littafin sunan Minhajun Nadamah da ya fi dacewa. Yadda abin yake shi ne, kamar mutum ne mai datti, qazami, Bamaguje mabiyi shexan, amma ya rinqa lissafa kansa daga cikin tsarkakan bayin Allah. Ai ka ga wannan abu ne mai nisa. Babu shakka zuciyar da ke cike da qyamar manyan-manyan waliyan Allah ita ce zuciya mafi muni da qazancewa a cikin halittun da ke bayan qasa. Bayan Annabawan Allah kuwa babu mahalukin da darajarsa ta yi ko kusa da ta Sahabbai. Wannan shi ne dalilin da ya sa Allah ya hana a ba kowa ganima a bayansu sai masu cewa;

ﭽ ﭖ ﭗ ﭘ ﭙ ﭚ ﭛ ﭜ ﭝ ﭞ ﭟ ﭠ ﭡ ﭢ ﭣ ﭤ ﭥ ﭦ ﭧ ﭨ ﭼ الحشر: ١٠



Ya Ubangijinmi! Ka yi gafara a gare mu, da kuma ga ‘yan’uwanmu waxanda suka riga mu yin imani. Kada ka sanya wani qulli a cikin zukatanmu ga waxanda suka yi imani, Ya Ubangijinmu! Haqiqa, kai ne Mai tausayi, mai jin qai.

Duba sarai malam ka gani, Shi’anci da Yahudanci sun yi kunnen doki wajen biyar son rai. In kuwa gefen faifayewa ne da kuma kantar jahilci, tsakaninsu da kiristoci ba a san gwani ba. Wannan ita ce haqiqanin shaidar da mutane suka bayar a kansu.

Malaman garin Kufa su suka fi kowa sani da tantance halayyar mabiya Shi’ah, saboda can ne tushenta. Bari mu ji wani malami daga cikinsu abin da yake cewa: “Duk a faxin duniya ba wanda ya fi Shi’ah sakarci. Kamar mujiya suke a duniyar tsuntsaye ko kuma jakkai a sashen dabbobi. Wallahi sun sha neman in fesa qarya a kan sayyidina Aliyu Raliyallahu Anhu wai don in qara bayyana darajarsa. Inda na yi haka ko to, da shirye suke su cika gidana da zinari da azurfa. Amma kash! Ni ba irin mai yin haka ne ba”1. In ji malam Sha’abi.

Haka ne. Wani malami ma mai suna Baban Hafsa wanda aka fi sani da Ibnu Shahin2 a cikin littafinsa mai suna Alluxfu Fis- Sunnati ruwitowa ya yi daga Imamus Sha’abi cewa: “Kashedinku da qungiyoyin bidi’a, musamman mabiya Shi’ah, waxanda suka shiga musulunci da qafar hagu; ba su shige shi saboda Allah ba, sai don huce haushi ga Musulmi. Wannan Shi ne babban dalilin da ya harzuqa sayyidina Ali har ya sa aka hura wuta aka rura ta sosai, ya ce a kama su xaya bayan xaya a rinqa jefawa a cikinta. Daga nan ya yunqura ya kai ma wasunsu xauki da hargagi, suka firgita. Suka cika wandunansu da iska, gudun fanfalaqi ya same su ba ji ba gani. Amma gwanin tsalle da nuna qwarewa cikin gudu a wannan rana Abdullahi xan Saba’i, ya tsira da rayuwarsa inda ya samu mafaka a Sabat ta qasar Iran, ya ko ci gaba da fesa gubarsa a can. Haka shi ma Abdullahi xan Yasaru da ya samu tserewa bai ci burki ba sai garin Khazar.

Su dai Mabiya Shi’ah, rashin lafiyarsu guda ce da ta Yahudawa. Bari mu hawar da su kan teburin misali ka ga yadda abin ya ke:

1.1.2 Jadawalin Zumuntar Shi’anci Da Yahudanci




Yahudawa Sun Ce
Babu maganar Jihadi sai ranar da Dujjal ya bayyana, kuma Allah ya aiko shi da takobi daga sama.
Ba wanda ya cancanci shugabanci sai zauri’ar Annabi Dawuda Alaihis Salamu.
Suna jinkirin sallar magariba sai bayan fitowar taurari.
Suna bauxe ma alqibla wurin yin sallah.
Suna rufe idanunsu wurin ibada.
Idda ba dole ba ce ga mata a wurin su.
Sun karkatar da ma’anar littafin At- Taurah.
An wajabta salloli 50 a kansu kowane wuni.
Suna birkice sallama ga musulmi su ce, Assamu madadin Assalamu suna roqon mutuwa ga musulmi.
Sun haramta ma kansu wasu nau’oin kifaye guda biyu; Tarwaxa ba Buku.
Ba su yin shafa a kan safa.
Sun halalta ma kan su cin dukiyar kowa in ba wasu-wasu ba. Kamar yadda Allah ya labarta mana cikin Alqur’ani.
Wajen yin sujada suna yin dungure. Wato, suna aza gefen goshi.
Ba su zuwa sujada kai tsaye sai sun fara wani irin sunkuyar da kai.
Suna qiyayya da mala’ika Jibrilu Alaihis Salamu.






Yan Shi’ah Sun Ce
Babu maganar Jihadi sai ranar da Mahadinsu ya bayyana, kuma sai sun ji anyi shela daga sama.

Ba wanda ya cancanci shugabanci sai Ali Raliyallahu Anhu da zuriyarsa.


Suna jinkirin sallar magariba sai bayan fitowar taurari1

Suna bauxe ma alqibla wurin yin sallah


Suna rufe idanu wurin sallah
Idda ba dole ba ce ga mata a wurin su.
Sun karkatar da ma’anar littafin Alqur’ani.
Su ma sun ce, salloli 50 aka wajabta masu kowace rana.
Su ma dai haka xin suke yi.

Su ma ‘yan Shi’ah sun ce, duk kifaye sun yi magana da Ali in ban da waxannan biyu. Don haka ba su cin su.

Su ma ‘yan Shi’ah haka.
‘Yan Shi’ah ma suna ganin cewa, dukiyar kowa halas ce gare su in dai ba xan Shi’ah ba ne.

Su ma ‘yan Shi’ah suna yin irin wannan sujada.

Su ma ‘yan Shi’ah haka suke yi.

A wajensu mala’ika Jibrilu ya yi kure wajen kawo ma Annabi Muhammadu Sallallahu Alaihi Wasallama manzanci maimakon Ali. Don haka su ma suna adawa da shi.


Aqidun Shi’ah ba da na Yahudawa kawai suka yi kama ba. Wasu aqidun nasu kama suke yi da na Kiristoci. Dubi auren ‘yan mishan, mine ne ba jin daxi kawai ba, tun da ko sadaki ba sa bayarwa? A gefe xaya kalli auren mutu’ar Shi’ah, ai ka ga biri ya yi kama da mutum ko?

Idan ka kalli wata fuska sai ka ga gara ma Yahudawa da Kirista a kan ‘yan Shi’ah. Domin kuwa duk Bayahuden da ka tambaya wane ne ya fi daraja a cikin mutane? Zai ce maka: “Sahabban Annabi Musa Alaihis Salamu”. Tambayi Kirista irin wannan tambaya, shi kuma zai ce maka: “Sahabban Annabi Isa Alaihis Salamu”. A yayin da idan ka tambayi xan Shi’ah, su wane ne suka fi kowa qasqanci a bayan qasa? Sai ya ce maka: “Sahabban Annabi Muhammadu Sallallahu Alaihi Wasallama.

A lokacin da Allah mai girma da xaukaka ya ba da umurni a nema wa magabatan musulmi gafara, a lokacin su ‘yan Shi’ah ke cika bakinsu da zagi na fitar arziki da cin zarafi gare su, ba kunya ba tsoron Allah. Don mi ba za a zare takobi a nufe su ba, daga nan har ranar da Allah zai naxe qasa? Allah ya tarwatsa gungunsu ya watse haxin kansu. Kamar yadda Allah ya ce:

ﭽ ﰉ ﰊ ﰋ ﰌ ﰍ ﰎﰏ ﭼ المائدة: ٦٤

Kuma kodayaushe suka hura wata wutar yaqi, sai Allah ya bice ta”1.

Waxannan jawabai da aka jiyo haka su ke. Domin kuwa dimun sun yi kama da duk abin da ya sifanta su da shi.

Sun yi fatar gurvata musulunci kamar Yadda Bulus xan Yusha’u wani basarake daga cikin Yahudawa ya rikirkita addinin Kiristanci. Duk da sallah suka yi ba ta zuwa ko ina don ba a amsarta. Bayani ya gabata cewa, Aliyu Raliyallahu Anhu sai da ya tarwatsa gungunsu har ma ya kai ga azabtar da su da wuta, lokacin da su Abdullahi xan Saba’i da Abubakar Al-Kurus suka yi gudun da muka faxa a xazu. Su ne kuma dai waxanda suka faifaye har suka Allantar da Aliyu wanda har ta kai yake cewa, a waqe:

Yayin da har lamarin wajensu ya kumbura

Sai nayyi gwami nak kirawo Qambara

Yad dinga jejjefa su xai-xai-xai ciki

Domin musulmi dagga nan su yi hattara



1.2 Mafarin Sunan ‘Yan Shi’ah “Rafilah”

Sanannen suna ne ga ‘yan Shi’ah da aka kira su da shi “Rafilah”. Asalin sunan kuwa shi ne, saboda a farkon lamarinsu sun kasance masu biyyaya ga imaminsu Zaidu xan Aliyu xan Husaini, amma daga baya sai suka wancakalar da shi suka yi watsi da lamarinsa. Wannan kuwa ya faru ne a lokacin mulkin Hisham wajejan shekara ta 121 bayan hijira. Kalmar Raflu mai ma’anar wancakalarwa ita ce ta bi su har aka san su da suna ‘yan Shi’ah.

Farkon al’amarin Shi’ah ta rabu ne zuwa gida biyu: Rafilah da kuma Zaidiyyawa, a lokacin yunqurin juyin mulkin da suka ingiza Zaidu xan Aliyu xan Husaini ya yi, a qarshe kuma suka dare masa.

Tarihin wannan suna na Rafilah ya samo asali ne bayan da suka tambayi Zaidu xin matsayin sayyidina Abubakar da Umar a wurinsa. Shi kuma sai ya faxi kyakkyawar magana game da su. Daga nan sai suka bijire masa suka ba shi baya don su nuna masa rashin jin daxinsu game da yabon da ya yi wa manyan Sahabban. A nan ne sai ya ce; Rafaltumu ni? Kun watsar da ni? Sai sunan kuwa na Rafila ya bi su har lahira. Su kuwa sauran waxanda suka zauna tare da shi sai mutane suka ba su sunan Zaidiyyawa saboda jivintar lamarinsa da suka yi. Har kwanan gobe kuwa Zaidiyyawa na makokin kashe shi a daidai itaciyar da aka tsire shi, sun ma mayar da wurin wajen yin bauta safe da marece.

Da haka suka kafu a matsayin qungiya mai aqidodi daban-daban da suka haxa da; rabke salloli a yi su lokaci guda har koyaushe ba tare da lalura ba. Ba su yin sallah sai a lokuta guda uku,1 wannan kuwa duk saboda kamanta kansu da Yahudawa.

A cewarsu, sakin aure ba ta yadda zai tabbata sai an kafa shaidu. Kuma duk wanda ba xaya daga cikinsu ba najasa ne. Ba su cin yankan kowa sai nasu. Sun ce duk da ruwan da musulmi ya yi amfani da su, ya zama najasa. Idan kuma ya ci abinci a cikin wani kwano ko akushi dole ne sai an wanke kafin xan Shi’ah ya ci a cikinsa. Duk sun xauko waxannan xabi’oi da aqidoji daga Yahudawa, musamman Samirawa, qungiyar Yahudawa mafi muni. Kuma a kan wannan dalili ne da yawan mutane ke kiran mabiya Shi’ah da sunan Samirawa. Manufa a nan ita ce, kamar yadda Samirawa suka bar addinin Yahudanci haka Shi’ah suka bar addinin musulunci.

Sun qware ga munafucci, wato Taqiyya kenan. Ga kuma sharri kamar Yahudawan asali.
1.3 Wautar ‘Yan Shi’ah

Akwai Labarun wauta da soki burutsu tattare da Shi’ah. Kaxan daga cikinsu su ne; Akwai wata rijiya wadda Zaidu bn Aliyu xan Husaini ya gina, shi ne aka samu wani sashe na mabiya suka haramta ma kansu shan ruwan rijiyar don qiyayya ga Zaidu, sun mance da cewa Annanbi Sallallahu Alaihi Wasallama da kansa tare da Sahhabbansa Allah ya yarda da su, sun kasance suna shan ruwan rijiyoyin da kafirai suka gina ballantana rijiyar da wani musulmi ya gina. Kuma akwai wasu daga cikinsu da ba su cin taura, wai don kawai a qasar Sham ake samun ta inda magoya bayan sayyidina Mu’awiyah suka fi yawa. Alhali kuwa, Annabi Sallallahu Alaihi Wasallama da kansa yana cin abincin da aka shigo da shi daga qasashen qetare. Ko da kuwa qasashen kafirai ne. Kamar yadda yake sanya tufafin da asalinsu kafirai ne suka xunka su.

Haka kuma ‘yan Shi’a sukan canfa lamba goma, suna matuqar qyamar ta, ta yadda ko gida za su gina ba za su yarda yawan xakunansa ya zamo goma ba. To, ko a masallatansu ma, ba su yin ginshiqai guda goma. Dalili kuwa, shi ne tsananin qyamar da suke yi wa Sahabbai guda goma da Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama ya yi masu bushara da aljanna.

Dubi hadisin da ya zo cikin Sahihu Muslim riwayar Jabir Allah ya yarda da shi, cewa watarana wani hadimin Haxibu xan Abu Balta’ata ya ce; “Ya Manzon Allah! na rantse da Allah sai Haxibu ya shiga wuta”. Sai Annabi Sallallahu Alaihi Wasallama ya ce masa, ka sha qarya. Saboda Haxibu ya halarci yaqin Badar da Hudaibiyya.1

To, me ya yi zafi wanda ya sa mabiya Shi’ah suke adawa da waxannan manyan bayin Allah, in ba kaxan daga cikinsu ba? Yanzu Mu ma jingine zancen Sahabbai a gefe, bari mu ba da wani misali, mu qaddara cewa yanzu haka akwai wasu gogaggun qafirai guda goma a duniyarmu ta yau, me zai zama dalilin camfa adadin yawansu har a ce ana qyamar amfani da shi idan ba tsagwaron jahilci ba? Ai Allah ya ambaci cewa:

ﭽ ﭽ ﭾ ﭿ ﮀ ﮁ ﮂ ﮃ ﮄ ﮅ ﮆ ﮇ ﭼ النمل: ٤٨



Kuma waxansu jam’a (Su) tara sun kasance a cikin birnin, suna yin varna kuma ba su kyautatawa.2

Shi kenan sai ya zama dole a camfa lamba tara (9), a qaurace ma yin amfani da duk wani abu da ke da dangantaka da ita, hujja da cewa tarihi ya labarta samuwar wasu ‘yan daba guda tara masu varna a cikin birni a wani lokaci da ya gabata? Idan kuwa har wannan ba aikin hankali ne ba, to ya za a yi qaurace wa lamba goma (10) ya zama aikin hankali? Ai ita lamba goma xin ma, Allah ya faxe ta a wurare da yawa a cikin Alqur’ani Mai girma kuma ta fuska kyakkyawa. Kamar in da Allah ya ce;

ﭽ ﰃ ﰄ ﰅ ﰆ ﰇ ﰈ ﰉ ﰊ ﰋ ﰌ ﰍﰎ ﰏ ﰐ ﰑ ﭼ

البقرة: ١٩٦



Sa’an nan wanda bai samu ba, sai azumin yini uku a cikin hajji da bakwai idan kun koma, sun zama goma kenan cikakku1.

Wannan game da hukunce-hukuncen hajji kenan. Game da lamarin Annabi Musa Alaihis Salamu kuwa, sai Allah ya ce;

ﭽ ﮕ ﮖ ﮗ ﮘ ﮙ ﮚ ﮛ ﮜ ﮝ ﮞ ﮟ ﮠﮡ ﭼ الأعراف: ١٤٢

Kuma muka yi wa’adi ga Musa da darare talatin, kuma muka cika su da wasu goma, sai miqatin Ubangijinsa ya cika dare arba’in.2

Kai! Ba ma fa sai an tafi da nisa ba, duba farkon Walfajri ka ga abin da Allah ya ce:

ﭽ ﭑ ﭒ ﭓ ﭔ ﭕ ﭼ الفجر: ١ - ٢

Ina rantsuwa da alfijir da darare goma (na farkon watan Muharram).

A cikin Sahihul Buhari, Hadisi ya tabbatar da cewa: “Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama ya kasance yana I’itikafi cikin kwanaki goma na qarshen Ramalana har ranar da ya bar duniya”.3

Game da daren Lailatul qadari kuwa, ga abin da Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama ya ce: “Ku Lalube ta cikin ranaku goma na qarshen Ramalana”.4

Ga kuma wani hadisin da ya ce: “Babu kwanakin da aikin alheri ya fi soyuwa a wurin Allah cikinsu fiye da kwanaki goma (yana nufin na farkon watan Muharram)”.5

Waxannan bayanai da Makamantansu suna da yawan da sun fi qarfin qididdiga.

Wani halin kwan-gaba-kwan-baya da bankaurar mabiya Shi’ah shi ne, lale marhabin da suke yi da lamba tara (9) saboda ximauta da makanta har sun mance da cewa cikin waxancan Sahabbai goma da ba su son a ce an yi wa bushara da aljanna, guda tara ne suke qyama. Ga shi kuma lamba tara (9) ta zo ne a matsayin zargi, da bayanin adadin ‘yan daba kamar yadda ya gabata. To, ya kenan?

Kada a manta cewa, sun qaurace ma sunan Abubakar da Umar da Usmanu kuma ba su qaunar duk wani mai sha’awar su, saboda tsananin qiyayya da masu su na asali. Alhali kuwa ko da a ce waxannan mutane sun zama ‘yan gaba-gaba ga ayyukan kafirci a duniya, ba wai gaba-gaba a wajen taimakon Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama ba, wannan ba ya zama dalilin qaurace ma sunayensu. Ai a cikin Sahabbai akwai mai suna Walidu wanda Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama ya yi ma addu’a cewa: “Ya Allah ka kuvutar da Walidu”.1 Ko ka manta da Walidu xan Mugirata na daga cikin manya manyan masu adawa da Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama, wanda har shaguve Alqur’ani ya yi game da shi a Suratul Muddassir?

Akwai mai suna Amiru a cikin Sahabbai kamar yadda akwai mai irin wannan suna cikin mushrikai. Haka ma Khalidu da Hishamu da Uqbatu, kai! Har da sunan Aliyu akwai masu irin sa a cikin kafirai, kamar Aliyu xan Umayyata xan Khalafu, kafiri, gamji sai sara.

Tambaya a nan ita ce, wa ya tava cewa, Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama ya umurci Sahabbai da su qaurace ma waxannan sunaye, wai saboda dangantakarsu da wani kafiri? Idan kuwa babu ita ce amsar, to, ina dalilin qyama da qaurace ma sunayen manyan Sahabban Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama?

A cewarsu wai, Sahabban munafukai ne. Shi ne dalilin da ya sa suke qyamar su. Assha! Magana ta yi muni. Amma kada ku manta da matsayin Aliyu Allah ya yarda da shi a wajenku. Ba kun ce shi ma’asumi ba ne wanda ba ya kure gaba xaya? To, ai ba a ga ya nuna qyamarsa ga xaya daga cikin waxannan manyan waliyai ba. Hasali ma, ya girmama su. Kai! Har ma shi da kansa ya sanya wa wasu daga cikin ‘ya’yansa sunayensu.

Gaskiyar lamari dai, musulunci bai hana amfani da sunan duk da bai sava ma Shari’a ba, ko da ko an ambaci wani kafiri da shi. Kuma kangare ma wannan tafarki ba komi ba ne face fito na fito da shari’ar Musulunci. Sunayen Aliyu da Ja’afaru da Hasan da Husaini da suke yawan sa wa, ai ba tabbaci ne cewa duk masu waxannan suna masoya ne ga waxanda ke da sunayen na asali ba.

A wata Sabuwa kuma suna da wata xabi’ar ta wauta, inda suke sammako da maraici a gindin wani dutse mai kogo da ke garin Samarrah. Su kan yi tamatela suna jiran bayyanar Mahadinsu wanda suke da aqidar yana cikin dutsen. Kuma sun tanadar masa ingarman doki taka-hau don da ya bayyana ya garzaya da su zuwa aljannar duniya. Sun girke wani mutum a daidai wurin mai qatuwar murya yana qwalla kira a kai-a kai yana cewa fito maza fito maza Ya Maulana! Sannan wani babban abin da ke xaure kai shi ne yadda suke zagaye wannan bagire xauke da makamai tsoron wai kada a hargage su. Sannan sai su ayyana mutum guda wanda jiddadun za a same shi a tsaye a wannan wuri riqe da makami duk da Sallah babu ruwansa da ita don kada hankalinsa ya xauku har Mahadi ya vullo ba da saninsa ba.

A lokacin da duk suka yi ma wannan wuri nisa kuwa, sai su rinqa fuskantar dabra da wajen suna qwala ihu da kiraye-kiraye cikin gaugawa, wanda babu buqatar yin hakan da a ce gaskiya ne wannan mahadin yana raye. Kuma har Allah ya umurce shi da fitowa. To, ka ga daman ai Allah Subhanahu WaTa’ala ya ce:

ﭽ ﮀ ﮁ ﮂ ﮃ ﮄﮅ ﮆ ﮇ ﮈ ﮉ ﮊ ﮋ ﮌ ﮍ ﮎﭼ فاطر: ١٣



Wannan Shi ne Allah, Ubangijinku gare shi Mulki yake, kuma waxannan da kuke kira waninsa ba su mallakar ko fatar gurtsun dabino. Idan kun kira su ba za su ji kiranku ba, kuma ko sun jiya, ba za su karva muku. Kuma a Ranar qiyama za su kafirce wa shirkinku, kuma babu Mai ba ka labari kamar wanda ya sani.1

Wannan ya nuna gara ma ‘yan bautar gumaka, waxanda duk da rashin ji da ganinsa amma ga shi gabansu suna kallo, savanin masu zaman jiran gawon shanu.

Idan wani xan Shi’ah ya bugi qirjin cewa shi, babu mai xauke shi daga ra’ayinsa na yarda da samuwar Mahadin nasu, to, ai maganarsa ba ta da banbanci da ta ‘yan bautar gumaka da suke cewa, babu mai raba su da ra’ayinsu na cewa tabbas gumukansu za su cece su wurin Allah. Kuma ha kanshi ne dalilin da ya sa suka dage kai da fata suna bauta masu. Da waxannan da waxancan duk ja buge man, saboda jirgin halaka guda ya xauko su, zai kuma sauka da su tashar wahala.

Abin la’akari a nan shi ne, duk da wanda ya riqi mala’iku da Annabawa matsayin ababen bauta bai fita daga zargi da fushin Allah ba, balle wanda ya ciccivi wani mahalukin da ba ma ko xuriyarsa. Duba min gaba ka gani wai makaho ya so tsegumi.

Bugu da qari, har karvar umurni da hani suke yi daga wurin wannan hadarin kaka da Allah bai halitta ba ta hannun malumansu. Alhalin ko Allah Maxaukakin Sarki yana cewa:

ﭽ ﯘ ﯙ ﯚ ﯛ ﯜ ﯝ ﯞ ﯟ ﯠ ﯡ ﯢ ﯣ ﯤ ﯥ ﯦ ﯧﯨ ﯩ ﯪ ﯫ ﯬﯭ ﯮ ﯯ ﯰ ﯱﭼ التوبة: ٣١



Sun riqi Malamansu (Yahudawa) da Ruhubanawansu (Nasara) ababen bauta, baicin Allah, Kuma sun riqi Masihu xan Maryama (haka). Alhalin ba a umurce su ba face su bauta Ubangiji guda. Babu abin bauta wa face shi. Tsarkinsa ya tabbata daga abin da suke yin Shirka da shi.2

Kuma hadisi ya zo a cikin Tirmizi da waninsa, daga Adiyyu xan Hatimu Allah ya yarda da shi ya ce: “Ya Manzon Allah! Ba fa bauta musu su ke yi ba”. Sai Annabi Sallallahu Alaihi Wasallama ya ce: “Ba suna halalta musu haram ba, kuma suna haramta masu halal, su yi xa’a gare su? To, bautar da suke yi masu kenan”.

A nan idan ka dubi lamarin ‘yan Shi’ah za ka taras da su suna jingina hukunce-hukuncen halattawa da haramtawa ga Imaminsu da suka kira Mahadi, wanda bayani ya gabata cewa, sam babu samuwarsa kuma ko da abin da suka jingina ma Imamin ya ci karo da Alqur’ani da sunna da ijma’in malamai su ba ruwansu. Wautarsu ba ta tsaya a nan ba, ta kai su ga liqa ta ga Imamin nasu duk wata matsala da suka qirqira maras tushe. Qarshe kuma su ce, tafi maganar kowa.

Za a same su suna hanzari wajen misalta waxanda suke qiyayya da su da dabbobi. Wani lokacin ma sukan xauki matakin gana wa dabbar azaba, wai don xebe ta kaicin maqiyansu. Misali, sukan kamo akuya sai su xaure ta, su rinqa tsigar gashinta qarfi da yaji, wai sun ci zarafin Aisha. Kaico!

Wani lokaci kuma sukan samo salka su tsatstsageta da kakide (dasqararren mai). Daga nan sai su zaro wuqa su tsaga cikin salkar, sai kakiden ya bultso sai su rinqa riganganto wajen shan man, suna yi suna Santi, suna cewa, wai jinin Umar Raliyallahu Anhu ne suke sha. Ba wannan kaxai ba, sukan bushi iska a wani karon, su kamo jakuna biyu, su raxa wa xaya sunan Abubakar, xayan kuma sunan Umar, su ce, me za su yi in ba lallasa musu azabar duniya ba?

Wannan ya sa watarana da wani sarki ya lura da irin wannan xanyen aiki nasu ya sa aka ciyo kwalarsu, aka tungume su aka xaure ya rinqa gwada masu nau’ukan azaba, a cikin izgili, yana cewa Abubakar da Umar ne ya ke son sai ya ga baya gare su.

Wasu ‘yan Shi’ah kuwa karnuka suke kamowa su basu sunayen halifofin can guda biyu da muka ambata. Suna kiran su suna zagi da tsinuwa suna xebe musu albarka. Wani daga cikinsu kuwa ko karensa ba ya son a jingina ma sunayen waxannan bayin Allah. Wanda ko duk ya kuskura ya yi haka, to, faxa ya gama qulluwa a tsakankinsu, ya rinqa kururuwa da kumfar baki kenan, wai don mi ake ambatar karensa da sunan ‘yan wuta?!.

Akwai wani gogaggen kafiri wanda ya kashe Sarkin Musulmi Umaru xan Haxxabi har lahira, ana ce masa, Abu Lu’uluata, Bamajuse. Su kuwa wasu ‘yan Shi’ah shi suke matuqar girmamawa saboda a ganinsu ya yi namijin qwazo da ya kamata a so shi, a kuma jinjina masa saboda shi.

Harwayau, daga cikinsu akwai masu zuwa maqarbarta su zavi wasu qaburburan da ko kakanninsu ba su san waxanda ke kwance a cikinsu ba. Amma duk da haka, sai su zagaye su, su gina dogayen hasumiyoyi a kansu, kuma su rinqa kai musu ziyara lokaci-lokaci. Kai! Wani lokaci ma har da shirya bukukuwa a wurin, da sunan wai qaburburan Ahlul-baiti ne suke girmamawa. Wataqila ma qaburburan wasu manyan maqiya musulunci ne, amma da yake sun ximauce, sun makance gane ha kan zai wuyata gare su.

Bari a ba da wani gajeren bayani domin masu hankali. Idan aka yi la’akari da waccan aika-aikar mabiya Shi’ah ta azabtar da wasu dabbobi da sunan waxannan Sahabbai sai a ga iyakar wauta sun yi ta. Xauki misalin abin da yake qunshe a cikin kundin tarihin duniya, in da aka zayyana sunayen wasu qeqasassun kafirai irin su Fir’auna da Abu Lahabi da Abu jahali wawa, yanzu yana yiwuwa saboda son musuluncinmu da qyamar matsayinsu, sai mu kamo wasu dabbobi bayin Allah mu ayyana ma kowace dabba sunan xaya daga cikinsu, sannan mu rinqa koxa masu azaba?

A tsarin Shari’ar musulunci, duk da gawar kafiri ba a yarda da tozarta ta ba bayan an kashe shi. Saboda muradin musulunci shi ne ya dakatar da cutar kafirin, kuma ta hanyar kashe shi wannan buqatar ta biya. A kan yi masa haka ne kawai in ya kasance shi ya fara yi wa wani musulmi haka.

An samu ingantaccen hadisi cikin Sahihu Muslim daga Buraidah Allah ya yarda da shi ya ce: “A duk lokacin da Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama zai tura rundunar yaqi yakan umurci shugaban rundunar da cewa, ya ji tsoron Allah a karan kansa da kuma jama’arsa. Daga nan kuma ya qara da cewa, ku yi yaqi saboda Allah, ku yaqi wanda duk ya kafirce ma Allah, kada ku ci gululi, kuma kada kuyi yaudara. Sannan ku kuma nisanci Musla, wato, wulaqanta gawa. Kada kuma ku kashe qananan yara.1

A Wani bayani mai kama da wannan, yazo a cikin littafan Sunan cewa, Manzon Allah sallahu alaihi wasallam ya kasance yana horon mutane da yin sadaqa, kuma yana tsawatar su game da yin Musula.

A nan, ya bayyana a fili cewa yin Musula ga kafirai bayan mutuwarsu, wulaqanci ne ga halittar Allah. Kuma Shari’a ba ta goyi bayan aiwatar da haka ba, tattare da kasancewarsa kafiri. Kenan su waxancan manyan Sahabbai Allah ya yarda da su, waxanda ‘yan-sha-biyu ke aibatawa tare da nuna qiyayya gare su, ko da a ce tun farko su ba musulmi ba ne, to, wannan ba zai zama lasisin wulaqantar da gawarsu ba ta hanyar duka ko tsage sashen jiki ko tsigar gashin gawar, balle maganar azabtar da wata dabba da sunansu. Wannan bai ko taso ba tattare da cewa azabtarwar ba za ta kai ga jikin Sahabban ba.

Daga cikin shiriritarsu, suna shirya bukukuwan baqin ciki da koke- koken tuna rasuwar malamansu, da wasu mutane. Tabbas wannan na nuna cewa sun jahilci haramcin kukan mutuwa da bukukuwan makokin a addinin musulunci. Kamar yadda Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama ya ce: “Wanda ya mari fuska, ya keci wuyan riga, ya yi hargowar jahiliyya, to ba shi tare da mu”. 2A wani hadisin kuwa cewa ya yi “Na barrantar da kaina daga mace mai aske kanta da mai hargowa a lokacin faruwar wata musiba, da kuma mace mai kece tufafinta” 3. A wani wurin kuma ya ce: "Ana azabtar da mamaci saboda kukan da ake fasa masa.” 4

Za ka ga ‘yan Shi’ah sun fi kowa aikata ayyukan jahiliyyah, kamar marin fuska, da keta tufafi, da iface-iface. Duka wai don tuna wata tsohuwar musiba. Kuma baka tava jin sun yi wa wani daga cikin bayin Allah da aka yi wa kisan zalunci daga cikin Annabawa da Waliyyai ko qyasham ba. Abin da yake nuna maka cewa, ko Husainin ma dai a lava ga sabara ne a harbi barewa. In ba haka ba, me ya sa ko mahaifin nasa ba sa yi masa kuka? Ashe ba kisan sharri ne shi ma aka yi masa ba? Ba sai mun tambaye su ba game da Usmanu xan Affana wanda aka yi wa kisan gila yana a matsayin halifan Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama a kuma cikin birnin Manzo yana rungume da Alqur’ani ba. Ba za mu tambaye su don me ba su yi masa kuka ba, domin mun riga mun san matsayinsu a kansa. Amma dai duk mai hankali ya gani a tarihi irin musibar da ta cimma musulmi a sakamakon kisan Usman, ba a tava ganin aukuwar irin ta ba ko a lokacin da aka kashe Husaini. Amma waxannan musibun sun wuce. To, mine ne na tashintashina?

Abin da ‘yan Shi’ah ke yi xin nan kuwa babban dalili ne a kan wautarsu. Domin babu wani mai kiran kansa musulmi da ke yin irin wannan xabi’a in ba su ba. Wautarsu ba a nan ta tsaya ba. Yanzu haka dai wasu daga cikinsu ba su qona wata itaciya da ake kiya Xarfa’u wai don sun ji an ce jinin Husaini ya zuba ga reta! To, in banda wauta wa ya ce ba a qona itace idan wani jini ya zuba a kansa? Kuma ma shin wannan iccen shi ne yake har yanzu a cikin dazuzzuka? Irin waxannan abubuwa na wauta a cikinsu suna da yawa. Kuma tun farkon vullar Shi’ah a zamanin Tabi’ai ake hikaito irin waxannan labaran game da su, ga su ko har yau ba su bari ba.

Don mu yi masu adalci, dole ne a nan mu faxi cewa, ba dukkan ayyukan wauta da ‘yan Shi’ah ke yi suka kevanta da ‘yan-sha-biyu ba. A’a, wasunsu an fi sanin su ne a wajen sauran qungiyoyin Shi’ah, musamman dai Gulatu. Haka kuma wasu abubuwan da jahilan ‘yan Shi’ah ke qudurtawa, malamansu ba su fatawa da su, kamar haramta cin naman raqumi, da kuma cewa sharaxi ne sai mace ta yarda da saki kafin ya tabbata.


Yüklə 2,75 Mb.

Dostları ilə paylaş:
1   2   3   4   5   6   7   8   9   ...   51




Verilənlər bazası müəlliflik hüququ ilə müdafiə olunur ©muhaz.org 2024
rəhbərliyinə müraciət

gir | qeydiyyatdan keç
    Ana səhifə


yükləyin