Tafarkin sunnah



Yüklə 2,75 Mb.
səhifə6/51
tarix28.10.2017
ölçüsü2,75 Mb.
#17506
1   2   3   4   5   6   7   8   9   ...   51

Fuska Ta Farko: Ai sani ne baku yi ba, imami da xayan waxannan mutane da aka ambata, ba wajibi ne a kan xaya daga cikin Malaman Musulunci, da qungiyoyin Sunnah ba. Duk wanda ko aka samu daga cikinsu yana jin cewa, imanin da mutanen wajibi ne, ko har ma yake wajabta hakan a kan mabiyansa, to, shi da ‘yan Shi’ah uwarsu xaya ubansu xaya. Musamman da zai rataya hakancan da kammaluwar imanin xayan su da Allah.
Fuska Ta Biyu: Duk malaman musulmi da shugabaninsu sun haxa a kan cewa, sanin wajibban addini da mustahabbansa ba su rataya akan gasganta samuwar mutanen da aka ambata ba. Duk kuwa wanda ya zaci haka daga cikin ‘yan xariqa da wasunsu to, tabbas jahili ne kuma vatacce. Ka ga a nan sun banbanta da ‘yan Shi’ah da ke ganin cewa, ba addini ga wanda bai gasgata samuwar Mahadinsu ba.

Sannan kuma lafuzzan da su ‘yan xariqu ke amfani da su irin, Gausi da Quxubi da Autadu da Abdalu da sauransu, ba wanda ya riwaito su daga Annabi Sallallahu Alaihi Wasallama ko Sahabbansa da isnadi tsaftatacce. Gara ma dai kalmar Abdalu da aka samu wasu magabata sun yi amfani da ita, duk da yake hadisin da aka riwaito akan ta mai rauni ne. Mun yi magana mai warkarwa game da wannan a wani littafe ba wannan ba.


1.7 Tsakanin Shi’anci da Sufanci

Fuska Ta Uku: Wannan matsayi na Shi’ah ‘yan-sha-biyu ya yi daidai da na sufaye, waxanda ke da aqidar cewa manyan waliyyansu, wato Gausi ko Quxubi su ke shiryar da mutane a duniya. Haka kuma a cewarsu, babu wani alheri da zai sami wani mutum sai da sani da kuma izininsu. Kai! Hasali ma sun san zahirin mutane da baxininsu, na farko da na qarshe. Irin wannan aqida kuwa, duk musulmin duniya na qwarai sun haxu a kan cewa, vata ce. Domin kuwa ba ta da banbanci da aqidar Kiristoci a wannan babin. Saboda kamar suna cewa ne akwai wani mai tarayya da Allah a cikin ayyukan da ya kevanta da su.

Kamar yadda wasunsu ke cewa game da Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama da wasu shaihunansu, wai ilimin xaya daga cikinsu da ikonsa daidai su ke da na Allah Ta’ala.

Cikinsu akwai wanda ke danganta wa xayan mutanen nan abin da ke iya yiwuwa ga Annabawa da muminai mutanen kirki kamar faruwar wata karama ko kasancewar xayansu idan ya yi addu’a ana karva, da kashefi, wato a sanar da wani bawan Allah wani abin da ya faku ga sauran mutane. Waxanda ke jingina samuwar waxannan karamomi ga mutane rayayyu kuma sanannu ai sun fi kusa da gaskiya bisa ga masu danganta su ga wanda Allah bai halicce shi ba.
1.8 Zancen Khadir Da Ilyasu

Fuska Ta Huxu: Gaskiyar magana ita ce, abin da Malamai masu zurfin bincike suke a kansa, cewa Ilyasu da Khadir sun mutu kamar yadda kowane mahaluki yake mutuwa. Kuma babu wanda Allah ya sanya a tsakanin sa da bayinsa ko ya wakilta shi wajen halittawa ko azurtawa ko shiryarwa ko bada nasara da makamantan su. Ko da Manzanni aikinsu bai wuce na isar da saqo ba.

1.9 Mu Koma Kan Maganar Imamah

Game da maganar Imamah dai, wato shugabancin sha biyun da ‘yan Shi’a suka naxa, ba mu gan shi a Alqur’ani ba. Alhalin kuwa Alqur’anin cike ya ke da bayanin duk abin da musulmi ke da buqatar sanin sa, kamar sanin sunayen Allah da tauhidinsa da siffofinsa, da ayoyinsa da Mala’ikunsa da littaffansa da Manzanninsa da ranar Alqiyama. Ga kuma sauran bayanai da suka haxa da labarai masu qarfafa imani, da umurni da hani. To, duk waxannan abubuwan ‘yan Shi’ah sun ce ba su kai muhimmancin shugabancin sha biyu ba. To, ina yake a Alqur’ani?

Haka kuma Allah Ta’ala ya rataya samun tsira akan abubuwa ga shi ko shugabancin irin na Shi’ah baya cikinsu. Allah Ta’ala na cewa:

ﭽ ﭹ ﭺ ﭻ ﭼ ﭽ ﭾ ﭿ ﮀ ﮁ ﮂ ﮃ ﮄ ﮅ ﮆ ﮇﮈ ﮉ ﮊ ﮋ ﮌ ﭼ النساء: ٦٩



Duk wanda ya yi wa Allah da Manzonsa xa’a to waxannan na tare da Annabawa da Siddiqai da Salihai, to tarayya da waxannan ya kyautatu. Suratun-Nisa: 69

Kuma Allah ya ce:

ﭽ ﯚ ﯛ ﯜ ﯝ ﯞ ﯟ ﯠ ﯡ ﯢ ﯣ ﯤ ﯥﯦ ﯧ ﯨ ﯩ ﯪ ﭼ النساء: ١٣

Kuma duk wanda ya yi wa Allah da Manzonsa xa’a Allah zai shigar da shi aljannar da qoramu ke gudana a qarqashin ta, suna madawwama a ciki. Wancan shi ne babban rabo. Suratun Nisa’i:13.

Kuma Allah na cewa:

ﭽ ﯫ ﯬ ﯭ ﯮ ﯯ ﯰ ﯱ ﯲ ﯳ ﯴ ﯵ ﯶ ﯷ ﯸ ﭼ النساء: ١٤

Kuma duk wanda ya sava wa Allah da Manzonsa, kuma ya qetare iyakokinsa, Allah zai shigar da shi wuta, ya na mai dawwama a cikin ta. Kuma ya na da azaba mai qasqantarwa. Suratun Nisa’i: 14.

In ko wani ya ce: Ai shugabanci irin na Shi’ah shi ma yana cikin xa’a ga Allah da Manzonsa. Sai mu ce masa: Ya za a yi shugabanci ya zarce Sallah da Zakka da Azumi da Hajji da sauran ta fuskar muhimmanci, sannan Allah ya faxe su ya wofintar da shi?

In an ce: Ba shi yiwuwa mu yi xa’a ga Manzo in ba mu yi xa’a ga shugaba ba saboda shi ya san shari’ah. Sai mu ce: wannan ita ce aqidar ‘yan-sha-biyu. Amma ba su da hujja ko ‘yar qarama ce akanta. Domin sannannen abu ne cewa Alqur’ani bai yi nuni da wannan ba kamar yadda ya bayyana sauran assullan addini. Ya gabata cewa, wannan shugaban da su ke rayawa, ba wanda ya amfana da wannan shugabancinsa, kuma dama abubuwan da Manzanni suka zo da su ba a buqatar shugabannin Shi’ah don saninsu.
1.10 Asalin Addini a Wurin ‘yan-sha-biyu

Asullan addini a wajen su huxu ne: Tauhidi, adalci, Annabci da shugabanci. Kuma Shugabanci shi ne na qarshe. A cikin Tauhidi ne sukan shigar da aqidarsu ta kore siffofin Allah da ya sa ma kansa da kuma cewa, Alqur’ani halittar Allah ne, ba maganarsa ba. Haka kuma a nan ne suke cewa, ba a ganin Allah a Lahira.

A cikin rukuninsu na biyu, wato adalci sukan shigar da qaryata qaddara, da kuma cewa Allah ba zai iya shiryar da wanda ya so ba ko ya vatar da wanda ya so. Ba lalle ne kuma abin da ya so ya faru ba, ko abin da bai so ba ya qi faruwa.

Abin da muka sani game da ‘yan Shi’ah shi ne, ba su cewa, Allah na da iko akan komai, ba su kuma cewa abin da Allah ya so ne ke kasancewa. Amma dai Tauhidi da Adalci da Annabci duk suna gaba ga shugabanci. To yaushe ne suka dawo suka sanya shugabanci ya zama mafi xaukaka da muhimmanci akan komai?

Sannan kuma, sun nuna cewa shugabanci wajibi ne don kasancewar sa mai sadarwa zuwa ga wajibbai. To yaya hanyar da ke kai mutum riskuwar maqasudi ke zama mafi xaukaka da muhimmaci a kan abin da ke maqasudin?
1.11 Takin Saqar ‘Yan Shi’ah

Farkon tuqa da warwarar da Shi’ah ‘yan-sha-biyu suka yi a wannan babi, shi ne irin yadda suka xauki mas’alar shugabanci, a matsayin abu mafi xaukaka da girma a addinin musulunci. Qarshe kuma sai suka dawo suka tsira wata wofintattar aqida game da shi. Wato qudurce samuwar wani shugaba a baxini, kuma ma’asumi, wanda kuma luxufi ne gare su a cikin al’amurransu na addini da duniya. Alhali kuwa babu shi ba alamarsa. Haka kuwa na tabbatar da kasancewar su mafi zama nesa daga wannan luxufi tattare da kasancewar sa babban gurinsu.

A maimakon haka, sai suka wayi gari suna xa’a ga kafirai da azzalumai don neman biyan buqatunsu, tunda waccan hanyar ta toshe. A qarshe kuma suka tave; ba su ga tsuntsu ba su ga tarko.

A dunqule Allah Ta’ala ya rataya samun maslahohin lahira da na duniya a kan shugabanni, duk xai ne shin mun ce shugabanci ne abu mafi muhimmanci ko a’a. Su dai Shi’ah ‘yan-sha-biyu sun fi kowa nisa daga samar da wannan maslahar, da kuma alherin da suka ce ana nema, kamar yadda su ke rayuwa.

Abu na biyu kuma shi ne, cewar da suka yi shi wannan ma’asumi a matsayinsa na shugaba, kasancewarsa samamme zata taimaka wa mabiyansa akan aikata abubuwan alheri na wajibi da nisantar munana daidai da yadda yake umurnin su. Ka ga bisa wannan iqirari, kamata ya yi a taras da ‘yan-sha-biyu sun fi kowa riqe addini hannu bi-biyu, tunda Mahadin can nasu na nan raye. Amma sai al’amarin ya kasance ba haka ba; aka wayi gari suka zama kurar baya.

Bayan wannan kuma suka ce, ba kowa ba ne wannan ma’asumi illa Ali. Shi ne kawai ya karva wannan suna daga cikin Sahabbai. Saboda haka shi ya fi kowa cancanta da ya jivinci al’amurran musulmi bayan wucewar Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama kai tsaye. Kuma ma wai, kan malamai ya haxu a kan haka. Suka kuma qara da cewa shi Alin, ya zavi Alhasan ya gade shi, shi kuma ya zavi Alhusaini. Bisa wannan tsari har aka kai ga wannan Mahadi da ake dako.

Ka ga duk wanda ya ji wannan magana sai ya zaci cewa ‘yan-sha-biyu na da cikakkar masaniya da al’amarin Mahadin nasu. Wato ko dai ya kasance sun tava sa shi a ido, ko wani wanda ya sa shi. Ko ko a’a, suna da wani kundi da ke qunshe da maganganunsa na horo da hani, ko wani abu mai kama da haka. Amma abin mamaki da na tambayi wani daga cikinsu a kan haka, sai ya karva man da cewa ba su da ko xaya daga cikin waxannan abubuwa. Ka ga a haka sun tabbata ashararu; waxanda basu jin kunyar yin amai su lashe.

Bayan wannan kuma, duk wanda ya kalli abin da idon basira zai fahimci irin kantar jahilcin da ke damun waxannan mutane. Domin kuwa a zahiri, aqidar dakon bayyanar wasu dokoki da hukunce-hukunce a hannun Mahadin nasu na nuna cewa abin da ke hannunsu na dokoki, waxanda suka samu ga malamansu ba gaskiya ba ne. Idan kuwa har suna jin gaskiya ne, to, tabbas babu wata fa’ida a cikin bayyanar Mahadin, ko da hakan za ta yiwu.

Ka ga a haka ma, har gara masu aqidar cewa Khadir na nan raye da su, domin ko akwai masu raya ganin sa har ma su riwaito wasu nasihohi daga wurin shi duk da yake ingancin hakan abu ne mai wuya. Amma duk da haka gara su da ‘yan-sha-biyu. Kai! Ba waxannan kawai ba, babu wata qungiya ta ‘yan bidi’a da za a ce gara ‘yan-sha-biyu da ita.
1.12 Daga Gani Sai Kai ya Kumbura?!

A bayyane take cewa, a aqidar wannan xan sha biyu, yin zamani xaya da wannan Mahadi nasu da suke jira, ko da kuwa bai bayyana ba ta ishi wanda ya yi imani da shi dalili na samun tsira. Wato a ma daina haqilo akan rashin bayyanarsa.

To, ka ga wannan magana ko kare ba ya ci ba. Domin kuwa, masaniya da Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama, ko yin zamani xaya da shi, ko yarda da an yi shi ba tare da amincewa da abin da ya zo da shi balle ya aikata ba, ba ya sa mutum ya samu rahamar Allah. Ka kuwa san ko waye Annabi, kuma ko waye wannan Mahadi da suke waqa.

Gaba xayan qungiyoyin musulunci sun yarda da cewa, duk wanda ya yi imani da Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama wajibi ne ya yi wa hakan rakiya da tsare dokoki. Idan kuwa ba haka ba, gobe lahira kashinsa ya bushe Annabi na ji na gani.

Akwai daga cikin Shi’ah ‘yan-sha-biyu da ke cewa, da zaran mutum ya so sayyidina Ali Raliyallahu Anhu a zuci to, yana iya aikata duk abin da ya ga dama don ya fi qarfin zunubi. A kan haka kenan, babu wata buqata ta samun wani shugaba ma’asumi a yau, don samun wata falala, domin son da suke ma Ali Raliyallahu Anhu a cewarsu, ya ishe su shinge.

1.13 Shugabanci ba ya Cikin Rukunan Addini

Xan Shi’ar ya ce, duk wanda bai yi imani da kasancewar mas’alar shugabanci rukuni daga cikin rukunan addini ba, to, babu shi babu tabbata cikin aljanna; ko ya shige ta ana koro shi.

Martaninmu a kan wannan magana shi ne, Allah Maxaukakin Sarki ya zayyana siffofin muminai a cikin Alqur’ani, amma bai faxi maganar shugabanci a cikinsu ba. Haka kuma Annabi Sallallahu Alaihi Wasallama bai ambace shi ba a cikin bayanan imani da rukunansa waxanda ya naqalto daga bakin Jibrilu Alaihis Salamu a cikin sanannen hadisin nan da Nawawi ya kawo a cikin Arba’una. Hadisin kuwa hujja ce karvavviya ga dukkan musulmi na qwarai.

Idan kuwa har ‘yan-sha-biyu suka qi yarda da wannan hadisi a matsayin hujjarmu, tattare da su ma suna kafa mana hujja da hadisan da basu kama qafar wannan ba, muna kuma qin karva. To, ga waxancan ayoyi da muka yi masu nuni da su a farko, su nuna mana inda Allah ya umarci muminai da yin imani da wani abu wai shi Imamah balle abu ya zama fitina. Allah Ta’ala na cewa:

ﭽ ﭧ ﭨ ﭩ ﭪ ﭫ ﭬ ﭭ ﭮ ﭯ ﭰ ﭱ ﭲ ﭳ ﭴ ﭵ ﭶ ﭷ ﭸ ﭹ ﭺ ﭻ ﭼ ﭽ ﭾ ﭿ ﮀ ﮁ ﮂ ﮃﮄ ﮅ ﮆ ﮇ ﮈ ﮉ ﮊ ﮋ ﮌ ﭼ الأنفال: ٢ - ٤

Muminai kawai su ne waxanda in a kira sunan Allah zuciyarsu na girgiza in aka karanta masu ayoyin Allah imaninsu na qaruwa kuma suna dogaro akan Allah). Waxanda ke tsaida Sallah kuma suna ciyarwa daga abin da mu ka arzitta su da shi, waxannan su ne muminai na haqiqa, suna da xaukaka qwarai wurin Allah da gafara da arziki mai yawa) Al-anfal 2-4.

Allah ya sheda cewa masu sifofin da ya ambata suna da imani amma bai ambaci shugabanci ba. Kuma Allah Ta’ala yana cewa:

ﭽ ﮬ ﮭ ﮮ ﮯ ﮰ ﮱ ﯓ ﯔ ﯕ ﯖ ﯗ ﯘ ﯙ ﯚ ﯛﯜ ﯝ ﯞ ﯟ ﯠ ﭼ الحجرات: ١٥
Waxanda dai suka yi imani su ne waxanda na yi imani da Allah da Manzonsa sannan ba su yi qwanqwanto ba suka kuma yi jihadi da kuxaxensu da rayukansu a tafarken Allah to waxannan su ne masu gaskiya) Al-hujurat 15.

Sai Allah ya sa (masu waxannan sifofi) cikin masu ingantancen imani ba tare da ambaton shugabanci ba.

Bayan waxannan ayoyi kuma, tarihi ya tabbatar da cewa, babu lokacin da wani ya zo karvar musulunci daga wurin Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama aka samu ya lissafa masa Imamah daga cikin rukunan imani. Ka kuwa san ba ta yuwa Annabi Sallallahu Alaihi Wasallama ya voye wa al’ummarsa wani abu na addini. Tunda kuwa har bai yi haka ba, ka ga ashe qarya ce kawai ‘yan-sha-biyu ke yi.

To, kuma koda ‘yan-sha-biyu za su yarda da rashin makama a nan, su ce, a’a, ai mas’alar Imamah na qunshe ne a cikin nassosa; ba qarara take ba, ta yadda sai an duba sannu a gan ta. Har yau dai basu tsira ba. Domin kuwa ko da haka ne, to, matsayin matsalar bai wuce kasancewa wani reshe na addini amma ba asali ba.

Wata tuqa da warwara kuma, da yin ban hannun makaho da gaskiya, a cikin lamarin ‘yan-sha-biyu shi ne, cewar da wannan wakili nasu ya yi wai, Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama ya ce, duk wanda ya mutu bai san imamin zamaninsa ba, to, ya yi mutuwa irin ta jahiliyyah.

To, kafin mu je ko ina dai, wannan hadisi ba gaskiya ba ne. don ko su ‘yan-sha-biyun ba su iya yin bayanin yadda suka samo shi balle ingancinsa.

Tabbas, akwai ingantaccen hadisi mai kama da wannan, wanda Muslimu ya riwaito daga Nafi’u. sai dai hujja ne a kansu. Bari ka ji yadda abin ya ke:

Nafi’u ya ce, Abdullahi xan Umar ya zo wurin Abdullahi xan Muxi’u lokacin da aka samu taqaddama tsakanin mutanen Madina da sarki mai ci a wancan lokacin, wato, Yazidu xan Mu’awiyah har suka yi niyyar yi masa tawaye da barazanar cire mubaya’arsa daga wuyansa. A nan ne Ibnu Umar ya zo wurin Abdullahi xan Muxi’u wanda shi ne jagoran wannan fitinar, sai xan Muxi’u ya ce, ku ba shi matashi, sai shi kuma Ibnu Umar ya karva da cewa, Ni ban zo da nufin zama ba, na dai zo ne in sheda maka abin da na ji da kunnuwana daga Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama sa’ad da yake cewa: Duk wanda ya cire hannu daga xa’a ran gamon sa da Allah ba shi da hujja. Kuma wanda duk ya mutu ba tare da ya yi wa shugaban musulmi mubaya’a ba, to, ya mutu mutuwa irin ta jahiliyyah.

Wannan ya nuna rashin halalcin fita daga xa’ar shugaba musulmi wanda ya tabbata. Haka kuma wanda ya qi bin shugaba na musulunci shi ne zai yi mutuwar jahiliyyah. Kowa ya sani kuwa cewa, ‘yan-sha-biyu sun fi kowa sava ma shugabannin musulunci.

Da ‘yan-sha-biyu sun san tsiyar da suke yi, da ko wancan gurvataccen hadisin nasu ba su kafa hujja da shi ba. Domin kuwa shi ma turmuza hancinsu yake yi. Saboda xabi’u irin na jahiliyyah sun haxa har da yaqi a kan ‘yan gidanci. Babu ko wanda ya kai su wannan xabi’ar. To, kuma ko a hakan Alqur’ani da Sunnah ba su kafirta mai irin wannan xabi’a ba balle wanda bai kai shi ba. Dubi waxannan hadisai:

Ya zo a ciki Sahihi Muslim ta hanyar Abu Hurairata ya ce Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama ya ce: Duk wanda ya fita daga xa'a, kuma ya bar jama'ar musulmi sannan ya mutu, to, ya mutu mutuwa irin ta jahiliyyah.

Ya kuma zo a cikin Buhari da Muslimu ta hanyar Abdullahi xan Abbas Raliyallahu Anhu. Daga Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama ya ce: Duk wanda ya ga shugabansa na da wani abin da ya ke qi to, ya yi haquri duk da haka. Lalle wanda ya fito yaqi da Sarkin Musulmi kwatankwacin taqa xaya, kuma ya mutu, to, ya mutu ne irin mutuwar jahiliyyah.

Ka ga qarara waxannan xabi’u da suka tabbata ga ‘yan-sha-biyun Shi’ah sun bayyana su xin ne suke mutuwar jahiliyyah ma damar suka gamu da Allah ba su tuba ba.

Haka kuma idan aka yi la’akari da kasancewar babu wanda ya san Mahadin can na ‘yan-sha-biyu daga cikinsu balle wani umurni ko hani nasa tun da ya faku ne tun yana xan shekara biyu ko uku lokacin da ya shiga rijiyar Samarra. Yau kuwa a cewar su shekaru kusan xari huxu kenan.1 Ka ga kenan ashe su ne waxanda basu san imaminsu ba. Wato, da za a qaddara kasancewar wancan hadisi ingantacce, to, su ne waxanda Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama ke yi wa bushara da mutuwa irin ta jahiliyyah.

Amma kuma a kula “Sanin shugaban zamani” ba ya nufin sanin shanu ko alama, ana nufin dai sani irin wanda zai ba mabiyan sa cikakkar damar yi masa xa’a da kasancewa tsintsiya maxaurinki xaya. Wato, irin abin da mutanen jahiliyyah suka rasa kafin aiko manzo.

Harwayau dai a kan maganar shugabanci. Siffofin da suka tabbata ga Mahadin ‘yan-sha-biyu, na rashin bayyana ga jama’a balle a yi masa xa’a, sun tabbatar da cewa shi ba shugaba ba ne a ma’aunin shari’ar musulunci. Dalili kuwa shi ne, Annabi Sallallahu Alaihi Wasallama ya yi umurni ne kawai da yin xa’a ga shugabannin da ke tare da jama’arsu. Ko su ma a kan abin da bai sava wa Allah ba. Bayan haka kuma ya hore su da haxin kai. Ka ga a cikin wannan magana akwai abin da ke tabbatar da cewa, shugaba a musulunci ba ma’asumi ba ne. don haka aka ce kada a yi masa xa’a idan ya kauce hanya.

Kai! Ko tunanin da ‘yan-sha-biyu ke da shi na cewa, wai saboda kasancewar shugabanci abu mafi daraja a addini ne aka ga Sahabbai rana a kansa bayan rasuwar Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama, ba gaskiya ba ne. ba a gan su a rana ba, sun dai qara wa juna sani ne kawai akan mas’alar, kamar yadda suka yi a kan wasu mas’aloli da suka fi ta muhimmanci. Idan dai har ‘yan-sha-biyu na neman lokacin da aka ga Sahabbai rana, to, shi ne lokacin halifancin Ali Raliyallahu Anhu.

Abin da ya faru lokacin naxa Abubakar Raliyallahu Anhu a Saqifa, da halifofi biyu na bayansa, sunansa shawarwari in har ana son gaskiya. Kuma ba a tashi taron ba sai da kowa ya fahimci juna a cikinsu.


1.14 Ina Nassin Yake?

Qare waccan magana kuma ke da wuya sai xan sha biyun ya jeranto sunayen Imaman nan da suke cewa su goma sha biyu. Kuma ya qara da cewa, wai, Annabi Muhammadu Sallallahu Alaihi Wasallama bai bar duniya ba sai da ya bayyana su a matsayin waxanda za su gade shi. Kuma wai har da cewa, duk Ahlus-Sunnah sun yarda da haka. To, ina ma nassin ya ke ballantana wani daga cikin Ahlus-Sunnah ya karvi wannan magana, to, balle kuma a ce duka?!


1.15 Zaven Siddiqu Nassi ne ko Shawara?

A wurin xan sha biyu, halifancin Abubakar naxin mutane ne ba na Allah ba. Tunda wai, Annabi Sallallahu Alaihi Wasallama bai bar wasiccin ya gade shi ba. Kuma wai, wannan shi ne abin da Ahlus-Sunnah suke a kai.

To, abin da za mu ce a nan shi ne, lalle a cikin Ahlus-Sunnah akwai masu ra’ayin cewa, Annabi Sallallahu Alaihi Wasallama bai yi wasicci da wani ya hau kujerarsa ba. Amma kuma tattare da haka, sanannen abu ne cewa, akwai wata jama’a daga cikinsu, da ke da ra’ayin cewa, halifancin Abubakar abu ne da aka yi bisa ga umurnin Allah da Manzonsa, wato nassi. Akwai maganganu masu yawa a kan haka a mazhabar Ahmad da wasu mazhabobi.

Alqali Abu Ya’ala da wasu malamai, sun ambaci riwayoyi biyu daga Imamu Ahmad a kan wannan lamari:

Riwaya ta farko na cewa, halifancin Abubakar ya tabbata ne nassance; ta hanyar wasu hadisai. Kuma a kan wannan fahimta ne wasu malaman hadisi da Mu’utazilawa da Ash’ariyyawa suke. Shi ma Abu Ya’ala ita ce fahimtarsa. A yayin da riwaya ta biyu kuma ke cewa, a’a, halifancin nasa ya dai tabbata ne ta hanyar ijtihadi. Wannan kuwa shi ne abin da Hasanul Basri da wasu malaman hadisi su ke.

Akwai hadisai da dama da ke tabbatar da waxannan riwayoyi kamar hadissan da malam xan Hamidu ya kafa hujja da su, daga cikinsu har da hadisin da Buhari ya riwaito daga Jubairu xan Mux’imu cewa: “Wata macce ta zo wurin Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama sai ya umurce ta da zuwa ta dawo. Sai ita kuma ta tambaye shi da cewa, idan ban taras da kai ba fa? Sai ya karva mata da cewa: “Sai ki nemi Abubakar”. Sai kuma hadisin rubuta wasiyyar da Annabi ya yi quduri a lokacin jinyarsa.

Hadisi na biyu shi ne wanda Huzaifa xan Yamani ya riwaito cewa: Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama ya ce: “Ku yi koyi da biyun nan da ke zuwa bayana; Abubakar da Umar”.

Hadisi na uku daga Abu Hurairata Allah ya qara masa yarda ya ce: Na ji Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama ya ce: “A lokacin da nake barci sai na ga wata guga a kan rijiya, sai na xibi ruwa daga cikin abin da Allah Subhanahu WaTa’ala ya sawwaqe mini. Sannan xan Abu Quhafata (Abubakar) ya xauki gugar ya xebo sau xaya ko biyu. Akwai rauni a cikin xibarsa, Allah ya gafarta masa rauninsa. Sannan guga ta koma hannun Umar xan Haxxabi, ban ga wani gwani mai xiba irin tasa ba. Har sai da mutane suka qoshi da ruwan suka zauna a wurin”. Buhari ya riwaito shi.

Hadisi na uku daga Abdurrahman xan Abu Bakarata daga babansa ya ce: Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama watarana ya ce: “Wane ne daga cikinku ya yi mafarki?” Sai na ce: “Na yi mafarkin na ga kamar sikeli na reto daga sama. Sai aka auna ka da Abubakar sai ka rinjaye shi . Sannan aka auna Abubakar da Umar sai Abubakar ya rinjaye shi. Sannan sai aka auna Umar da Usman sai Umar ya rinjaye shi. Daga nan sai aka xauke sikelin”. Sai Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama ya ce: “Mafarkinka na nuni ga halifanci irin na annabta da za a yi. Bayan sa kuwa Allah zai ba da mulki ga wanda ya so”.

Hadisi na Huxu: Daga Jabir Al-Ansari ya ce: Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama ya ce: “Wani mutumin kirki a yau ya yi mafarkin an rataya Abubakar gare ni. An kuma rataya Umar ga Abubakar. Shi kuma Umar sai aka rataya masa Usman”. Jabir Raliyallahu Anhu ya ce: “Mutumin kirkin nan da ya yi mafarkin ba wani ba ne face Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama. Ratayar kuma abin da take nufi shi ne gadon junansu da za su yi xaya bayan xaya”. Abu Dawuda ya riwaito shi.

Hadisi na Biyar: Daga Nana Aisha Raliyallahu Anha cewa, Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama ya shiga wurin ta ranar da ya fara rashin lafiya. Ya ce: “Ki kira mani babanki da xan’uwanki, in rubuta wa Abubakar saqo”. Sannan kuma dai sai ya ce: “Ai Allah da Musulmi za su qi karvar kowa sai Abubakar”. A wani lafazi na hadisin “Saboda haka, kada kowa ya sa ransa”.

In ka haxa waxannan hadissai da dukkan riwayoyi ingantattu da suka nuna gabatar da Abubakar ya ba da Sallah, zaka aminta cewa, tabbatattar magana dai ita ce, Annabi Sallallahu Alaihi Wasallama ya yi nuni ga mutane cewa, Abubakar ne mai maye gurbinsa. Ya kuma yi musu ishara zuwa ga haka da abubuwa masu yawa da suka haxa da maganganunsa da ayyukansa. Kuma ya so ya rubuta wannan don ya zama wasiccin da za a zartas bayansa amma Allah bai nufa ba saboda wata hikimar da Maxaukakin Sarki yake nufi ta karantar da mu yin shawara a tsakaninmu ga al’amurranmu.

Malam Ibnu Hazam ya kafa hujja a kan ingancin halifancin Abubakar da cewa, muhajirai da Allah ya kira su masu gaskiya su ne suka ba shi wannan suna. Allah Subhanahu WaTa’ala ya ce game da su:

ﭽ ﮱ ﯓ ﯔ ﯕ ﯖ ﯗ ﯘ ﯙ ﯚ ﯛ ﯜ ﯝ ﯞ ﯟ ﯠﯡ ﯢ ﯣ ﯤ ﯥ ﭼ الحشر: ٨



(Arzikin qasa) na matalautan muhajirai ne waxanda aka fitar da su daga gidajensu da kuxaxensu suna neman falalar Allah da Manzonsa. To, waxannan su ne masu gaskiya) Al-Hasr 8.

Ibnu Hazam, daga cikin masu ra’ayin cewa, halifancin Abubakar ya tabbata ne da nassi daga Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama ya kare wannan ra’ayin nasu da hujjoji masu qarfi. Kuma ya ce, ba shi yiwuwa Sahabbai su haxu a kan ce masa Halifa in babu wani nassi a kan haka. Daga cikin hadissan da ya kafa hujja da su har da, hadisin matar da ta ce ma Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama idan ban same ka ba ya zan yi? Sai ya ce, ki je wurin Abubakar. Da kuma hadisin A’ishah Raliyallahu Anha wanda Sallallahu Alaihi Wasallama ya ce mata: “Na so in aika ma babanki da xan’uwanki su zo don in bar masu saqo a rubuce don kada mutane su yi savani, wani ya ce, ni ne na fi cancanta, ko wani mai guri ya yi guri. Amma kuma Allah da Manzonsa da muminai duk Abubakar suka zava”.

Ibnu Hazam harwayau, ya mayar da martani a kan sauran hujjojin da malaman da ke xaya vangaren suka yi amfani da su. Kamar maganar da sayyidina Umar Raliyallahu Anhu ya yi cewa; “In na zavi halifa a bayana to, wanda ya fi ni ma ya yi haka”. Yana nufin Abubakar. “In kuma ban sa wani ba, to, kuma wanda ya fi ni ya tafi bai sa kowa ba”. Yana nufin Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama. Sai kuma hadisin nana Aisha Allah ya qara mata yarda cewa, an tambaye ta, shin da Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama zai sa wani ya maye gurbinsa wane ne zai sa?

Waxannan hadisai duk da yake suna nuna cewa, Annabi Sallallahu Alaihi Wasallama bai ayyana wani tsayayyen shugaba a bayansa ba, amma malam Ibnu Hazam ya ce, ba shi yiwuwa su keta ijma'in da Sahabbai suka yi. Domin ba su yi qarfin da za su iya yin haka ba duk da ingancinsu.

Idan har an qaddara gaskiya ne cewa, Manzo ya faxi wanda zai gade shi, to, ko a haka ma ‘yan-sha-biyu ba su da hujja. Domin Rawandiyawa daga cikinsu na ganin cewa, Abbas ne Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama ya bar nassi a kan zai gaje shi, ba Ali ba. Alqali Abu Ya'ala ya qara haske a kan wannan maganar, inda ya faxi cewa, wasu ‘yan Rawandiyyah na ganin bayan Abbas ‘ya’ya da jikokinsa ne za su ci gaba da halifanci har ranar tashin qiyama. Kuma wai, in ji Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama. Kuma sannan nassin da ya faxi haka wai ba a fayyace yake ba. Waxannan ra’ayoyan biyu sun yi hannun riga da ra’ayoya biyu na ‘yan-sha-biyu da kuma Jarudiyawa daga cikin Shi’ah. Su dai Jarudiyawa, savanin ‘yan-sha-biyu, ganin suke yi Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama ya faxi shugabancin Ali amma ba qarara ba. Ya dai bayyana sifofin da ba a same su ga kowa ba sai Ali.

Abin nufi dai a nan, shi ne cewa, kowane daga cikin waxannan bayin Allah guda uku; Abubakar da Abbas da Ali an samu masu raya cewa, Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama ya bar nassi a kansu. Kuma cewa, ya bar nassi a kan Abubakar shi ne ya xara sauran ra’ayoyan qarfi ta fuskar hujja da kuma karvuwa a wurin malamai, duk da yake a mafi rinjayen zance babu nassin ga ko xaya.

Alamu masu yawa sun nuna cewa, Abubakar ne Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama ya zava, kuma Sahabbai sun fahimci haka. Don haka ne ma Umar Raliyallahu Anhu ya ce, a cikin huxubar da ya yi gaban Muhajiruna da Ansaru: “Babu wanda mutane ke so daga cikinmu kamar Abubakar” Buhari da Muslim. Bisa wannan dalili ne gaba xayansu suka yi wa Abubakar bai’a, in ban da Sa’adu xan Ubadata, a sakamakon sha’awar da yake da ita ga matsayin. Amma kuma daga baya ya yi mubaya’ar.

Muhajiruna sun yi wa Abubakar wannan mubaya’a ne a kan sanin da suka yi na cewa, Allah da Manzonsa shi suka fifita. Ka ga a haka ta tabbata cewa, halifancin nasa ya tabbata ne ta hanyoyi ingantattu.


Yüklə 2,75 Mb.

Dostları ilə paylaş:
1   2   3   4   5   6   7   8   9   ...   51




Verilənlər bazası müəlliflik hüququ ilə müdafiə olunur ©muhaz.org 2024
rəhbərliyinə müraciət

gir | qeydiyyatdan keç
    Ana səhifə


yükləyin