Tafarkin sunnah


Wai ‘Yan Shi’ah ne Kawai za su Shiga Aljanna!



Yüklə 2,75 Mb.
səhifə9/51
tarix28.10.2017
ölçüsü2,75 Mb.
#17506
1   ...   5   6   7   8   9   10   11   12   ...   51

2.6 Wai ‘Yan Shi’ah ne Kawai za su Shiga Aljanna!

Xan Shi’ar ya ce: Dalili na biyu mai nuna wajabcin bin mazhabar Imamiyyah, shi ne: Abin da shehunmu jagora mafi girma, Khawwajah, mai taimakon addini da gaskiya, muhammadu xan Al-Hassan ax-Xusi Allah ya tsarkake ruhinsa ya ce, bayan na tambaye shi game da mazhabobi sai ya ce: Mun yi bincike game da su kuma da cewar Manzo Sallallahu Alaihi Wasallama: “Al’ummata za ta rarrabu zuwa qungiyoyi saba’in da uku, daga cikinsu akwai qungiya guda mai tsira sauran kuma suna wata”. ga shi kuma ya bayyana a cikin wani hadisi ingantacce qungiyar da ke tsira da kuma qungiyoyin da za su halaka shi ne cewarsa: Iyalaina kamar jirgin Annabi Nuhu Alaihis Salamu ne, wanda ya shige shi zai tsira, wanda bai shiga ba kuma ya halaka. Sai muka tarar da cewa qungiyar da za ta tsira ita ce ta Imamiyyah, don sun sava wa dukan mazhabobi, dukan mazhabobi kuma sun haxu a cikin asullan aqidojinsu.


Martani:

Da farko shi wannan xan Shi’ar ai ya kafirta wannan malamin nasa da yake fankamawa bai sani ba. Don malamin nasa na cikin masu cewa, duniya ba ta da farko. Shi kuma ya kafirta duk wanda ya ce haka a cikin littafinnan nasa da muke tattaunawa da shi.

Wannan malamin nasa kuma yana da kyau a sani shi ne wannan da ya yi qaurin suna wajen taimakon arna ‘yan Shi’ah Baxiniyah Al-Isma’iliyyah a Alamauta. Sannan lokacin da Turkawa mushrikai su ka zo qasar musulmi, har suka iso bagadaza cibiyar halifanci, wannan mutum ne ya kasance malamin duban da ya ba mushrikai su Hulaku sa’a don su kashe halifan musulmi, da malamai da masu riqo da addini. Kuma ya ce kada a kashe masu sana’o’in hannu da ‘yan kasuwan da xan Shi’ar ke samun amfani na duniya daga wurinsu. Kuma ya yi rubda ciki da dukiyoyin waqafi na musulmi, yana bayarwa daga cikinta ga mushrikai, malamai da shehunnansa na qungiyar Bakhshiyyah masu siddabaru da makamantansu. Sannan kuma lokacin da ya yi wani gini a wurin da ake kira Maragah ya gina shi kamar ginin mabiyan addinin Sabi’awa mushrikai, ya fi quntata wa mutanen da addininsu ya fi kusa da addinin Allah, waxanda suka fi rabo wurinsa kuwa sune waxanda suka fi nisa daga addinin Allah kamar su Sabi’awa da masu kore sifofin Allah Ta’ala da sauran mushrikai, kodayake sana’arsu ta kasance duban taurari da tsibbu da makamantan wannan.

Abu ne da yake sananne game da wannan da ya kira shehinsa – shi da mabiyansa, shi ne suna wulaqanta abubuwan da musulunci ya farlanta, suna qin barin abin da musulunci ya yi hani da shi, kuma ba su kiyaye salloli, ba su barin aikata savo kamar Zina da shan giya da miyagun abubuwa kamar waxannan, har ya kai ga cewa an san abin da suka aikatawa na munkari cikin watan azumi na dangin ashsha da shan giya, wannan malamin nasa bai kasance yana da wani tasiri ba sai tare da ‘yan’uwansa mushrikai waxanda addininsu ya fi na Yahudawa da Narasa zama qumsa cuta.

Don hakan ne duk lokacin da musulunci ya qarfafa cikin turkawan Mugul, sai lamarin waxannan ‘yan Shi’ar ya yi rauni don tsananin qiyayyar da suke yi wa musulunci da musulmi. Don haka Sarki Nuruz mujahidi kuma Shahid ya nisantar da su. Shi ne kuma wanda ya kira Sarkin Mugul Gazan zuwa ga musulunci, ya yi masa alqawarin zai taimake shi in ya musulunta. Shi ne kuma ya kashe mushrikan da ba su musulunta ba cikin Bakhshiyyah mushrikai masu sihiri, ya rusa wuraren bautar gumakansu, ya karya gumakan, ya kuma halaka masu kula da su, sannan ya lizimta ma Yahudawa da Nasara biyan jiziya soboda bayyanar musulunci a cikin turkawa Magul da mabiyansu.

A taqaice dai lamarin Tusi da mabiyansa mashahuri ne wurin musulmi, kuma ya fi qarfin a sifanta shi. Duk da haka an ce a qarshen rayuwarsa ya kasance yana tsare salloli biyar, kuma yana yawan karanta tafsirin Al-bagawi da fiqihu da makamantan haka. In dai har ya tuba ne daga ilhadi, to, Allah na karvar tuban bayinsa kuma yana gafarta zunubai. Allah Ta’ala na cewa:

ﭽ ﮣ ﮤ ﮥ ﮦ ﮧ ﮨ ﮩ ﮪ ﮫ ﮬ ﮭ ﮮﮯ ﮰ ﮱ ﯓ ﯔ ﯕﯖ ﯗ ﯘ ﯙ ﯚ ﯛ ﭼ الزمر: ٥٣

Ka gaya wa bayina waxanda suka wuce wuri cikin zaluntar kawunansu cewa, kada su yanke qauna daga rahamar Allah. Haqiqa Allah na gafarta dukan zunubbai. Haqiqa shi, mai gafar ne, mai jinqai. Az-Zumar: 53.

Amma dai abin da xan Shia’ar ya riwaito daga shi Tusi in ya kasance kafin tuba ne, to, ba a karvar maganarsa. In kuma bayan tuba ne, to, bai tuba daga bin mazhabar Shi’ah ‘yan-sha-biyu ba kenan. Ya dai tuba ne daga ilhadi kawai. To, bisa qaddarawa ta biyun ma ba za a karvi maganarsa ba. Abin da ya fi bayyana shi ne cewa xan Shi’ar nan ya kasance yana huxuwa da shi da makamatan sa lokacin da yake yi ma mushrikan Al-magul duba, a wannan lokacin an san ilhadi ne halinsa.

To, wanda ya kasance yana sukar mutane kamar Abubakar da Umar da Usmanu da Muhajirai da Ansarai na farko, kuma yake sukar irin su Maliki da Shafi’i da Abu Hanifa da Ahmad xan Hambali da mabiyansu, yana aibata su saboda kurakuran da ba nasu ba kamar cewa wasu na ganin halaccin wani nau’i na dara, ko waqe. Wanda yake haka, ya zai kafa hujja maganar irin waxansu da ba su ko yi imani da Allah da ranar qarshe ba, balle su haramta abin da Allah ya haramta da wanda Manzo ya haramta, kuma ba su bin addinin gaskiya. Waxanda kuma suke halatta haramtattun abubuwan da duk musulmi sun haxu a kan haramcinsu, kamar zina da shan giya da rana a cikin watan azumi. Waxanda suka tozarta sallah, suke bin son rayukansu, suka keta hurumin shariah, suka wofinta abubuwan da addini ya haramta, suka bi hanyar kafirai.

Wannan dai shi ne halin da Shi’ah ‘yan-sha-biyu suke a kai. Kodayaushe suna qiyayya da waliyyan Allah salihai magabata na farko daga cikin Muhajiruna da Ansaru, da waxanda suka yi masu kyakyawan bi, suna jivintar kafirai da munafukai.

Abin mamaki shi ne wannan makirarren xan Shi’ar maqaryaci da yake ambaton Abubakar da Umar da Usmanu da sauran magabatan farko da Tabi’una da kuma sauran shugabannin musulmi da malamai da masu riqo da addini, yake ambaton su da munanan siffofi na qarya ba su ji ba, ba su gani ba, sannan ya zo wurin wanda ya shahara wurin musulmi da kasancewa mai sava wa Allah da Manzonsa, yana cewa wai: “Malaminmu mafi xaukaka” har da cewa: “Allah ya tsarkake ruhinsa”. Tare da cewa shi kansa ya sheda da kafircinsa da masu kama da shi, tare da la’anar da ya ke yi ma mafifitan muminai na farko da na qarshe.

Waxannan ‘yan Shi’ar na shiga cikin ma’anar cewar da Allah Ta’ala ya yi:

ﭽ ﯵ ﯶ ﯷ ﯸ ﯹ ﯺ ﯻ ﯼ ﯽ ﯾ ﯿ ﰀ ﰁ ﰂ ﰃ ﰄ ﰅ ﰆ ﰇ ﰈ ﰉ ﭑ ﭒ ﭓ ﭔﭕ ﭖ ﭗ ﭘ ﭙ ﭚ ﭛ ﭜ ﭝ ﭼ النساء: ٥١ - ٥٢

Shin ba ka ga waxannan da aka ba su wani rabo na (ilmin) littafi ba, amma suna gasgata gunki da Xagutu, kuma suna ce ma waxanda suka kafirta: “Waxancan (mushrikai) sun fi muminai kasancewa bisa hanyar shiriya. Waxannan su ne Allah ya la’anta. Wanda duk Allah ya la’anta kuwa ba za ka sami mai taimakon sa ba. An-Nisa: 51-52.

Su ma ‘yan-sha-biyu an ba su wani sashe na littafe, don sun yarda da wani sashe na littafin da Allah ya saukar, kuma suna da wani yanki na imani da sihiri da Xagutu wanda shi ne duk abin da ake bauta ba Allah ba. Saboda suna imani da falsafa da ta qunshi wannan, suna ganin cewa addu’a da ibada ana yi wa matattu, suna yin masallatai akan qaburbura, suna xaukar cewa, tafiya zuwa wurinsu kamar hajji ne.

Wannan hadisi da xan-sha-biyun ke godogo da shi, fassararsa ta zo ta fuskoki biyu: Fuska ta farko, an tambayi Manzo Sallallahu Alaihi Wasallama game da qungiyar da zata tsira, sai ya ce “wanda suke akan irin abin da nake yau a kansa; ni da Sahabbaina”. A wata riwayar ya ce: “Su ne jama’a”. Dukan waxannan maganganu biyu sun ci karo da ra’ayin ‘yan-sha-biyu, kuma suna nuna cewa, ba su ne qungiyar da za ta tsira ba, don sun fita daga cikin jama’ar musulmi, suna kafirta shugabannin musulunci suna kiransu Fasiqai, irin su Abubakar da Umar da Usmanu. Ba zancen su Mu’aawiyah da sauran Bani Umayyah ake yi ba. Suna kuma kafirtar da malaman Sunnah da masu ibada daga cikinsu kamar su Maliki da Sauri da Auza’i da Laisu xan Sa’adu da Abu Hanifa da Shafi’i da Ahmad xan Hanbali da Ishaqa, da Abu Ubaidi da Ibrahimu xan Adhama da Fudailu xan Iyal da Abu Sulaimanad-Darani da Ma’aruf Al-Karkhi da makamantansu.

‘Yan-sha-biyu kuma sun fi kowa jahiltar tarihin Sahabbai balle koyi da su, sawa’un lokacin rayuwar Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama ko bayansa. Ga su kuma da qin hadisi da malamansa. To, in har siffar qungiyar da za ta tsira ita ce bin abin da Sahabbai suke a kai lokacin Manzo Sallallahu Alaihi Wasallama to, wannan taken Ahlus-Sunnati wal jama’a ne. Su ne qungiyar da za ta tsira. Don Sunnah ita ce abin da Manzo Sallallahu Alaihi Wasallama ya kasance a kansa shi da Sahabbansa, da abin da ya umurce su da shi, ko ya tabbatar da su a kanshi, ko ya aikata shi da kansa. Jama’a kuma su ne waxanda suka haxu, ba su rarrabe addininsu ba zuwa qungiyoyi. To, waxanda suka rarraba addininsu suka koma qungiyoyi ba su cikin Jama’a, Allah ya barrantad da Annabinsa dagare su. Wannan ya sa aka san cewa, Ahlus-Sunnati wal Jama’ah ne ke da wannan siffar ta masu tsira, ba siffar ‘yan-sha-biyu ba ce.

Suna iya cewa, tunda hadisin ya ce: “Abin da nake a kansa ni da Sahabbaina a yau” to, duk wanda ya fita daga wannan hanyar ba ya a kan hanyar qungiyar da za ta tsira. Kuma Sahabbai sun yi ridda bayansa, don haka ba su cikin qungiyar da ke tsira.

Sai a ce masu, haka yake. Mutanen da suka fi kowa shahara a ridda su ne masu jayayya da Abubakar da mabiyansa kamar Musailamu sarkin qarya da mabiyansa da ire-irensu. To, ‘yan-sha-biyu na son su, suna kariyarsu, suna ganin laifi Abubakar ya yaqe su wai, ba a kan gaskiya ba. Sannan waxanda suka fi kowa ridda bayansu su ne waxanda Ali Raliyallahu Anhu ya qona su a lokacin da suke cewa shi Allah ne abin bauta. Su ne sabi’awa mabiyan Abdullahi xan Saba’i waxanda suka fara bayyana zagin Abubakar da Umar Raliyallahu Anhuma.

Haka kuma farkon wanda ya fara da’awar annabta a cikin musulunci shi ne Mukhtar xan Baban Ubaidu, xan Shi’ah ne. Daga nan ake sanin cewa waxanda suka fi kowa ridda suna cikin ‘yan Shi’ah. Don haka ba a san wata ridda da ta wuce wuri kamar ta qungiyar ‘yar Shi’ah Nusairiyyah, da ta ‘yan Shi’ah Isma’iliyya Baxiniyyah da makamantansu ba. Wanda ya fi kowa shahara wurin yaqar waxanda suka yi ridda dai shi ne Abubakar Raliyallahu Anhu. Kuma masu ridda daxai sun fi yawa cikin qungiyoyin da ke husuma da Abubakar. Ka ga dai ridda na nan biye da ‘yan-sha-biyu kenan.

Wannan bayyane yake ga duk wanda ya bar musulunci da musulmi. Ba mai shakkar cewa jinsin masu ridda sun fi yawa cikin waxanda ke da dangantaka da ‘yan Shi’ah kuma riddarsu tafi kowace muni da tsanani a kafirci.

Sai cewarsa wai: ‘Yan Shi’ah sun banbanta da kowace mazhaba, sannan duk sauran mazhabobi sun haxu a kan wasu asulla na aqida. Idan yana nufin cewa ‘yan Shi’ah sun savawa duk mazhabobi ga abin da suka kevanta da shi, wannan haka yake, ba ga ‘yan Shi’ah kaxai ba, ga duk sauran qungiyoyi. Ba ka ganin Harijawa sun banbanta da kowa ga abin da suka kevanta da shi kamar kafirta mai savo, da kafirta Ali Raliyallahu Anhu, da cewa ba a yi wa Manzo xa’a ga abin da Manzo bai ce Allah Ta’ala ne ya yi umurni da shi ba, da cewa yana yiwuwa Manzon Allah ya yi zalunci wurin rabon abubuwa da kuma cikin hukuncinsa, da kuma qin bin hadisi mutawatiri in ya sava wa zahirin Alqur’ani, kamar cewa hannu varawo ana yanke shi ne daga kafaxa.. da dai ire-iren waxannan.

Amma in sun ce su ‘yan Shi’ah sun kevantu da dukan maganganansu, to, ba haka ba ne, don aqidunsu xaya ce da ta Mu’utazilawa. Kuma manyan ‘yan Shi’ah na farko masu sifaita Allah da jiki ne. Sannan sun yi muwafaqa da Mu’utazilawa a sha’anin yarda da qaddara. Manyansu na farko sun kasance suna tabbatar da qudura ga bawa, kuma na farkonsu masu tsananin inkari ne ga qudurar Allah fiye da inkarin da suke yi ma siffofin Allah, da cewar da suke yi masu zumubi ba su fita daga wuta.

A taqaice dai ‘yan Shi’ah na da maganganun da suka kevanta da su, kuma akwai waxanda suke tare da wasu a cikinsu, kamar yadda Mu’utazilawa da Harijawa da makamantansu su ke.

Amma Ahlul-hadith kuma Ahlus-Sunnah wal Jama’a sun kevantu da bin Alqur’ani da Sunnar da ta tabbata daga Manzonsu Sallallahu Alaihi Wasallama ga asuli da reshe, da kuma abin da Sahabban Manzo suka kasance a kansa. Wannan Savanin Mu’utazilawa da Harijawa da Shi’ah ‘yan-sha-biyu da waxanda suka yi muwafaqa da su a cikin wasu maganganunsu. Basu bin hadissan da amintattun malamai suka riwaito daga Annabi Sallallahu Alaihi Wasallama waxanda malaman hadisi sun san ingancin su.

Kuma ai sava wa mazhabobin da suka yi ya fi nuna vacin maganganunsu fiye da nuna cewa maganganun qwarai ne. Kasancewar kuwa maganganun qungiya sun banbanta da na sauran qungiyoyi ba shi ke nuna cewa maganganun daidai suke ba, kamar yadda haxuwarsu ga wata magana ba shi ke nuna cewa kuskure ce ba.

To in an ce: Annabi ya ce al’ummarsa za ta rarrabu zuwa kashi saba’in da uku, kuma xaya ce kawai ke tsira. Saboda haka dole ne xayar ta banbanta da saba’in da biyun da suka rage. Sai mu ce haka ne. Haka ma hadisin ke nuna cewa saba’in da biyun na banbanta da junansu kamar yadda suka banbanta da xayar mai tsira. Hadisin bai nuna cewa sauran qungiyoyin za su haxu a kan asullan aqidodi ba. Kai zahirin hadissin na nuna cewa saba’in da ukun dukansu sun banbanta da juna. A nan za a san cewa, gefen banbanci shi ne abin zargi ba gefen da suka haxu a kansa ba, don Allah Ta’ala ya yi umurni da jama’a da kuma jituwa tsakanin musulmi, ya kuma zargi rarrabuwa da savani. Allah Ta’ala ya ce:

ﭽ ﭱ ﭲ ﭳ ﭴ ﭵ ﭶﭷ ﭼ آل عمران: ١٠٣

Ku yi riqo da igiyar Allah gaba xaya, kuma kada ku rarraba. Ali-Imran: 103.

Ya kuma ce:

ﭽ ﮦ ﮧ ﮨ ﮩ ﮪ ﮫ ﮬ ﮭ ﮮ ﮯﮰ ﮱ ﯓ ﯔ ﯕ ﯖ ﯗ ﯘ ﯙ ﯚ ﯛﯜ ﯝ ﯞ ﯟ ﯠ ﯡ ﯢ ﯣ ﯤ ﯥ ﯦ ﯧ ﯨ ﯩ ﯪ ﯫ ﯬ ﯭ ﯮ ﯯ ﯰ ﯱ ﯲ ﯳ ﯴ ﯵ ﯶ ﯷ ﯸ ﯹ ﯺﯻ ﯼ ﯽ ﯾ ﯿ ﰀ ﰁ ﭼ آل عمران: ١٠٥ - ١٠٨

Kada ku kasance kamar waxanda suka rarrabu suka yi savani bayan bayani ya zo masu, to, waxannan suna da babbar azaba. Ranar da wasu fuskoki za su yi fari, wasu kuma su yi baqi. Amma waxanda fuskokinsu suka yi fari sai a ce masu: “Shin kun kafirta ne bayan imanininku? To, ku xanxana azaba saboda abin da ku ka kasance kuna aikatawa. Ali-Imran: 105-106.

Xan Abbas da waninsa sun ce, fuskokin Ahlus-Sunnah za su yi fari, fuskokin ‘yan bidi’a da masu savani su yi baqi. Allah Ta’ala ya ce

ﭽ ﭹ ﭺ ﭻ ﭼ ﭽ ﭾ ﭿ ﮀ ﮁ ﮂﮃ ﮄ ﮅ ﮆ ﮇ ﮈ ﮉ ﮊ ﮋ ﮌ ﮍ ﭼ الأنعام: ١٥٩

Lalle waxanda suka rarraba addininsu; suka zama qungiyoyi ba ka cikinsu ga komai. Al-Anam: 109.

Ya kuma ce:

ﭽ ﮒ ﮓ ﮔ ﮕ ﮖ ﮗ ﮘ ﮙ ﮚ ﮛ ﮜ ﮝ ﮞﮟ ﭼ البقرة: ٢١٣

Ba waxanda suka yi savani a cikinsa face waxanda aka ba su shi bayan bayani ya zo masu, (suka yi haka) don zalunci tsakaninsu. [Al-baqara 213]

Ya kuma ce:

ﭽ ﮌ ﮍ ﮎ ﮏ ﮐ ﮑ ﮒ ﮓ ﮔ ﮕ ﮖ ﮗ ﭼ البينة: ٤

Waxanda aka ba su littafi ba su rarraba ba sai bayan bayani ya zo masu. Al-Bayyinah: 4.

Idan lamarin ya kasance haka, to, qungiyar da tafi kowaci savawa jama’a da kuma savani tsakanin ita kanta, tafi sauran qungiyoyi cancantar zargi, wadda ta fi qarancin rarrabuwa da kusantar jama’a ta fi cancantar kasancewa a kan gaskiya. In dai Imamiyyah sun fi cancantar sava wa sauran qungiyoyin al’umma to, sun fi kowa nisa daga gaskiya, musamman ma kasancewar sun fi duk qungiyoyin al’umma savani tsakanin kansu, har aka ce qungiyarsu ta kasu zuwa saba’in da biyu. Wannan abin da muka faxa shi ne wanda aka riwaito daga Tusi da mabiyansa. Al-Hasan xan Musa An-Nubakhti ya rubuta littafi game da qididdigar qungiyoyin Shi’ah, ga shi kuma shi ma xan Shi’ar ne.

Amma Ahlus-Sunnah sun fi kowa qarancin savani a cikin asullan addininsu, sun fi kowace qungiya kusantar juna kasancewa tsakiya a wuraren savani, don ba su faifayewa ba su kuma kasawa. Ka ga ko ai Annabi Sallallahu Alaihi Wasallama ya ce: “Mafi alherin lamurra shi ne matsakaicinsu”. Don haka Ahlus-Sunnah su ne mafifitan dukan qungiyoyi. Don su ne matsakaita a kowane fanni.Ko a mas’alar Sahabbai, Ahlus-Sunnah ba su wuce wurin da masu guluwi ke yi, ba su kuma cin zarafi. Xauki misali Ali Raliyallahu Anhu ‘yan-sha-biyu sun faifaye game da shi, a yayin da Harijawa suka ci zalunsa; suna kafirta shi, suna ce masa azzalumi, mai yunwar jinin musulmi, can ga bakinsu. Ahlus-Sunnah suka shiga tsakani, suka faxi gaskiya.

Ni a iya sanina, ‘yan-sha-biyu ba su tava haxuwa a kan wata mas’ala ba koda qwaya xaya. Ita kanta wannan maganar da xan Shi’ar ya ambata xaya ce daga cikin maganganun ‘yan Shi’ar sha biyu ba duka ba. Daga cikinsu akwai masu sava ma wannan a tauhidi. Kuma mafi yawan ‘yan Shi’ah sun sava ma Imamiyyah (‘yan-sha-biyu) game da lamarin Imamai goma sha biyu. Zaidiyyah da Isma’iliyyah suna tsananin gaba da wannan aqidar ta imamai goma sha biyu.


2.7 Maganar Wofi: Wai su Kaxai ke da

Tabbacin Suna Kan Gaskiya!

Xan Shi’ar ya ce: Fuska ta uku, ita ce: Imamiyyah sun tabbatar cewa su da imamansu za su tsira, kuma cewa wanda ba su ba zai halaka. Ahlus-Sunnah ko ba su da tabbacin tsira ga kansu balle ga waninsu. Don haka bin ‘yan Shi’ah shi yafi cancanta ga mai hankali. Ka ga in da mutane biyu sun fita daga cikin Bagadaza suna son tafiya Kufa sai suka ga hanyoyi biyu kowanensu ya zavi xaya, sai wani mutum na uku ya zo shi ma zai je Kufa. Da ya tambayi na farkon, ka san hanyar da ka zava na kai ka Kufa? Kuma ita amintacciya ce ko a’a? Sai ya ce: Ni ban san komai ba game da wannan. Da ya tambayi na biyun sai ya ce masa, ni na tabbata tana kai ni Kufa, kuma amintacciya ce, kuma na san cewa hanyar da wannan ya bi ba zata kai shi Kufa ba, kuma ba amintacciya ba ce. To, in wannan mutum na uku ya bi hanyar mutumin farko lalle ya tabbata wawa a wurin masu hankali. Amma in ya bi na biyu to, ya nuna sanin-ya-kamata.


Martani:

In dai har wajibi ne a yi wa shagabannin da Shi’ah ke rayawa xa’a don a tsira, to, bin shugabannin Bani Umayyah da yi masu xa’a shi ma wajibi ne. Kuma in haka ne, masu bin su ido-rufe suna bisa gaskiya duk da zagin da suke yi wa Ali Raliyallahu Anhu da yaqan ‘yan Shi’ar da suke tare da shi da suka yi. Kar ka manta su ma suna ganin cewa, yi wa shugabanni xa’a wajibi ne a komai, kuma wai, Allah Ta’ala ba zai kama shugaba da kowane irin zunubi ba, kuma wai mabiya ba su da laifi ga duk abin da suka yi wa shugaba xa’a a cikinsa. Kai, waxannan sun fi cancantar ace suna da hujja fiye da ‘yan Shi’ah, don su suna xa’a ne ga shugabannin da Allah ya tsayar, ya kuma qarfafa mulkinsu.

Sanannen abu ne cewa maslaha da luxufin da aka samar wa bayin Allah ta hanyar sarakunan Bani Umayyah sun fi waxanda aka samu saboda shugaban ‘yan Shi’ar da babu shi, babu alamarsa, kasasshe; wanda bai iya bayyana don tsoro. Don haka ne maslahar duniya da ta lahirar da mabiya Bani Umayyah suka samu ta fi wadda mabiyan Na-Voye suka samu. Don duk tsawon jiran da suke ma sa ba ya umurnin su da kyakkyawa balle ya hane su daga aikata mumuna, bai taimakon su don samun wata maslaha ta addininsu ko ta duniyarsu. Savanin mabiyan Bani Umayyah da suka amfana qwarai ga lamurran addininsu da na duniyarsu ta hanyar shugabannin nasu da suke yi ma xa’a.

Daga wannan ya bayyana cewa, idan hujjar da masu biyar Ali Raliyallahu Anhu ke kafawa daidai ta ke, to, mabiyan Usmanu su xin ma hujjarsu tana a kan hanya. Tasu ma ta fi cancantar kasancewa gaskiya. In ko hijjarsu vatatta ce, to ta ‘yan Shi’ah ta fi vaci. Don da su da saura Ahlus-Sunnah duk sun haxu a kan cewa, xa’ar imaman Shi’ah kuskure ne kawai da vata.

Maganar ‘yan-sha-biyu dai an gina ta a kan turaku biyu waxanda gara da gumxa suka zaizaye. Na farko, cewa suna da imami ma’asumi. Na biyu, cewa yana umurni da wani abu. To, ka ga ai imaman da suke raya cewa ma’asumai ne; ba sa kuskure sun mutu tun tuni, shi ko wanda suke jira ya vace tun fiye da shakaru xari huxu da hamsin. Wasu malaman tarihi ma sun ce ba a tava samun sa ba. To, wa suke yi wa xa’a? Sai fa malaman Shi’ah ko litaffan da suka rubuta waxanda suke cewa sun karvo daga imamai da ba su kuskure. To, kuma ai suna kuskure, sannan ba su da tabbacin cewa za su tsira.

Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama dai shi ne ke isar da saqo daga Allah Ta’ala game da abin ya yi umurni da shi kuma da wanda ya yi hani daga gare shi, ba wata halittar da ake yi wa xa’a kai tsaye sai Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama. To, in an mayar da imami ko shaihi bayan fakuwarsa ko mutuwarsa abin kira, kuma ana neman ya biya wasu buqatu, kenan mamacin ya yi kama da Allah Ta’ala, wanda kuwa yin haka fita ne daga tushen musulunci shi ne Tauhidi.

Duba mafi yawan ‘yan xariqu, suna dogaro ne a kan wasu hikayoyin da aka riwaito daga shehinsu, waxanda da yawa daga cikinsu qarya ce aka yi masa, wasu kuma kuskure ne shehin ya yi, sai su bar riwaya ta gaskiya daga Annabi ma’asumi zuwa ga riwayar da ba a gasgatawa kuma daga wanda ba ma’asumi ba. To, idan waxannan ‘yan xariqun sun yi kuskure ne anan, to, ‘yan-sha-biyu sun fi su kuskure don sun fi zura qarya a cikin abubuwan da suke riwaitowa daga imamansu, kuma sun fi tsananin wuce iyaka ga raya cewa imamansu ma’asumai ne.

Misalin da ya bayar na masu tafiya Kufa shirme ne kawai. Wa ya sani ko wanda ya ce ya sani qarya yake yi? Wataqila ma dibara ce yake yi don ya samu abokin tafiya in sun yi nisa ya yi masa fashi! Shi dai na farkon ya bar ka da nazarinka, bai yi ma ka qarya ba don ka so shi. Ashe aikin hankali ba shi ne ka bi wannan kawai don ya cika baki ba, sai dai ka yi naka nazari har ka gano lafiyayyar hanya.

Kuma wai, yana nufin duk wanda ke bisa aqidarsu ya sakankance zai shiga aljanna koda kuwa ya bar farillai, ya aikata haramun? To, wannan kam ko ‘yan-sha-biyun ba su ce haka ba. Kuma duk wani mai hankali ma ba zai faxi haka ba.

Wai, a ganinsu sun samu tabbacin tsira ne saboda son Ali Raliyallahu Anhu a matsayinsa na aikin lada da suka ce, savo ba ya cutar da mai shi. Saboda haka kenan barin salloli da aikata alfasha koda zuriyar Ali ne Raliyallahu Anhu ba zasu cutar ba, kai, koda mutum ya zubar da jinin Bani Hashim, dangin Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama matuqar dai yana son Ali Raliyallahu Anhu. Wa zai gasgata wannan wofintattar magana? In kuma sun dawo sun ce, so na gaskiya na sa mutum ya bi masoyinsa, sai lamari ya koma ga cewa dole ne kenan a aikata wajibbai kuma a bar abubuwan da Allah Ta’ala ya haramta.

In kuma suna nufin cewa, duk wanda ke da aqida ingantacciya ya kuma aikata wajibai ya nisanci abubuwan da aka haramta zai shiga aljanna, to, wannan ita ce aqidar Ahlus-Sunnah, don su suna yanke cewa wanda ya ji tsoron Allah Ta’ala zai shiga aljanna kamar yadda Al-Alqur’ani ya ba da tabbaci. Amma Ahlus-Sunnah ba su yanke hukuncin shiga aljanna akan wani mutum na musamman don ba su da tabbacin cewa yana cikin masu tsoron Allah Ta’ala. Amma in an san cewa, ya mutu akan taqawa to, ana sanin cewa ya na cikin ‘yan aljanna. Don haka ne suke cewa, waxanda Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama ya ce ‘yan aljanna ne to, batu ya qare. Amma wanda mutane da yawa suka yaba da cewa mai rikon addini ne to, ba dukan Ahlus-Sunnah ke yarda da yin yanke a kan zamansa xan aljanna ba, sai dai kyautata zato.

Daga nan ne ya bayyana cewa, ‘yan-sha-biyu ba su da wani yaqinin da ake yabawa wanda suka kevanta da shi koma bayan Ahlus-Sunnah.

In sun ce suna da yaqini a kan wanda suka ga yana lizimtar aikata wajibai sannan yana nisantar muharramai cewa shi xan aljanna ne, ba tare da imami ma’asumi ya faxa masu abin da ke cikin zuciyarsa ba. Sai a ce masu wannan matsalar ba ta rataya da shugabanci ba. In ma an qaddara cewa akwai ingantacciyar hanya mai kai ga wannan to, ta Ahlus-Sunnah ce, kuma sun qwarewa shiga hanyar. In ko babu wata ingantacciyar hanya zuwa ga wannan, to, wannan magana da ba a gina a kan ilimi ba, babu wata falala a cikinta, haka ma cikin rashinta. A taqaice dai babu wani ingantaccen ilimin da za su raya face Ahlus-Sunnah sun fi su cancantarsa, amma abin da suka raya na jahilci to, wannan naqasu ne, kuma Ahlus-Sunnah sun fi kowa nisa daga gare shi.

Kuma ma a qashin gaskiya yaqinin da Ahlus-Sunnah ke da shi na samun tsirar shugabanninsu ya fi na Shi’ah ‘yan-sha-biyu. Don shugabanninsu bayan Manzo Sallallahu Alaihi Wasallama sune magabata na farko daga cikin Muhajiruna da Ansaru, sun kuwa sani yanke cewa, za su sami tsira. Suna sheda cewa Sahabban nan goma za su shiga aljanna, kuma Allah ya ce wa Sahabban Badar: “Ku yi abin da kuke so, lalle na gafarta maku”. Kai har ma suna cewa: “Babu wanda zai shiga wuta cikin waxanda suka yi wa Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama mubaya’a a qarqashin itaciyar nan”. Kamar yadda ya tabbata a cikin ingantaccen hadisi daga Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama. Waxannan sun fi mutum dubu da xari huxu, kuma shugabanni ne na Ahlus-Sunnah. Suna sheda cewa babu wanda zai shiga wuta cikinsu, kuma shahada ce da aka gina ta a kan ilimi, kamar yadda Alqur’ani da Sunna suka nuna.

Ahlus-Sunnah na yin sheda ko dai gamammiya ko kuma ga wasu sanannu, amma duk suna gina wannan akan ilimi. Amma ‘yan-sha-biyu su suna sheda a kan abin da ba su sani ba, ko su yi Shedar-Zur wadda sun san qarya ce, kamar yadda imamus-Shafi’i ya ce: “Ban ga mutanen da ke shedar qarya kamar Shi’ah ‘yan-sha-biyu ba”.

Kuma duk imamin da aka shaida cewa zai tsira ko dai ya kasance wanda ake yi wa gamammiyar xa’a ne, ko kuma wanda ake yi wa xa’a in ya yi umurni da abin da yake xa’a ne ga Allah Ta’ala da Manzonsa, da kuma abin da yake faxa daga ijtihadinsa in ya san babu abin da ya fi wannan. In imami shi ne na farkon to, Ahlus-Sunnah ba su da wani shugaban da ke haka bayan Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama. Su suna faxa ne kamar yadda Mujahid da Hakim da Malik da sauransu suka faxa cewa: “Duk mutum ana karva kuma ana barin maganarsa face Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama”. Su suna sheda cewa shugabansu shi ne mafificin halitta. Kuma suna sheda cewa duk wanda ya yi koyi da shi, ya bi umurninsa, ya hanu daga haninsa zai shiga aljanna. Kuma shaidar su Ahlus-Sunnah ta fi ta Shi’ah ‘yan-sha-biyu kamala har bisa wadda su ke yi wa shugabanninsu Askari i da ii da makamantansu cewa wanda ya yi masu xa’a zai shiga aljanna.

Allah Ta’ala dai ya yi alqawarin ni’ima ga wanda ya yi masa xa’a kuma ya yi wa Manzonsa xa’a, kuma ya yi alqawarin tavarwa ga wanda bai aikata haka ba. To, an rataya ni’ima a kan xa’a ga Allah Ta’ala da Manzonsa. Kamar yadda Allah ya ce:

ﭽ ﭹ ﭺ ﭻ ﭼ ﭽ ﭾ ﭿ ﮀ ﮁ ﮂ ﮃ ﮄ ﮅ ﮆ ﮇﮈ ﮉ ﮊ ﮋ ﮌ ﭼ النساء: ٦٩



Kuma wanda duk ya yi wa Allah da Manzonsa biyayya to, waxannan suna tare da waxanda Allah ya yi wa ni’ima daga cikin Annabawa da siddiqai da shahidai da salihai kuma maqwabtaka da waxannan ta kyautata An-Nisa: 69.

Da makamantansa.

Idan ya kasance haka, to, Allah Ta’ala na cewa:

ﭽ ﮧ ﮨ ﮩ ﮪ ﭼ التغابن: ١٦



ku ji tsoron Allah gwargwadon ikonku At-Tagabun: 16.

Duk wanda ya yi iyakar qoqarinsa wurin yin xa’a ga Allah da Manzonsa to, zai kasance cikin ‘yan aljanna.

Saboda haka cewar ‘yan-sha-biyu wai, ba mai shiga aljanna sai in shi xan-sha-biyu ne ba ya da banbanci da maganar Yahudawa da Nasara:

ﭽ ﯧ ﯨ ﯩ ﯪ ﯫ ﯬ ﯭ ﯮ ﯯ ﯰﯱ ﯲ ﯳﯴ ﯵ ﯶ ﯷ ﯸ ﯹ ﯺ ﯻ ﯼ ﯽ ﯾ ﯿ ﰀ ﰁ ﰂ ﰃ ﰄ ﰅ ﰆ ﰇ ﰈ ﰉ ﰊ ﰋ ﰌ ﰍ ﭼ البقرة: ١١١ - ١١٢



Kuma sun ce ba wanda zai shiga aljanna face in ya kasance Bayahude ne ko Banasare. Wannan gurinsu ne. Ka ce, su kawo hujjarsu in sun kasance masu gaskiya. Ba haka ba ne, duk dai wanda ya miqa wuyansa ga Allah (ya musulunta) kuma ya kasance mai kyautatawa, to, yana da ladarsa wurin ubangijinsa. Kuma ba tsoro gare shi, ba baqin ciki. Al-Baqarah: 111-112.

Sanannen abu ne cewa, wanda ‘yan-sha-biyu ke jira ba shi wajaba a kan kuwa ya yi masa xa’a, don ba a san wata maganar da aka naqalta daga wurinsa ba. Don haka, wanda ya yi wa Manzo xa’a zai shiga aljanna ko da bai yi imani da wannan imamin ba. Wanda ya yi imani da wannan imamin kuma ba zai shiga aljanna ba in bai yi wa Manzo Sallallahu Alaihi Wasallama xa’a ba. Don haka xa’ar Manzo ita ce abin dogara akai wurin samun tsira ba zama xan-sha-biyu ba. Ko a nan ta bayyana cewa, Ahlus-Sunnah sun tabbatar da cewa za su samu tsira da kuma tsira ga duk wanda yake bisa tafarkin na Sunnah.


Yüklə 2,75 Mb.

Dostları ilə paylaş:
1   ...   5   6   7   8   9   10   11   12   ...   51




Verilənlər bazası müəlliflik hüququ ilə müdafiə olunur ©muhaz.org 2024
rəhbərliyinə müraciət

gir | qeydiyyatdan keç
    Ana səhifə


yükləyin