Tafarkin sunnah



Yüklə 2,75 Mb.
səhifə18/51
tarix28.10.2017
ölçüsü2,75 Mb.
#17506
1   ...   14   15   16   17   18   19   20   21   ...   51

Martani: Eh! Gaskiya ne Akhdabu Khawarazumi ya yi wallafa a cikin abin da ya shafi darajojin Ali Raliyallahu Anhu sai dai masana hadisi sun dade da fahimtar cewa mafi yawan hadisan da ya riwaito a wannan babi ka gaggu ne. Wanda hakan ke tabbatar da cewa shi ba malamin hadisi ba ne da dai, balle har a iya riqon shi Hujja ko wata madogara.

Wani kuma abin da ke tabbatar da rashin cancantarsa da taka wanna rawa da yake ta qoqarin takawa a fagen hadisi, shi ne cewar da ya yi babu wani hadisi da zai riwaito face wanda ya inganta a idon waxannan mazaje. Wanda kuma suka riwaito a cikin nagartattun zantuka da littafansu. Sai kuma ga shi hakan ta faskara. Domin kuwa babu wani daga cikin malaman da ya riwaito wani hadisi daga cikin waxannan hadisai, a cikin litafai a cikin dogaro, balle ya inganta shi . hasali ma kansu haxuwa ya yi a kan kasancewar hadisan qarya.

Da haka ne kuma gaba xayan waxancan hadisai tara da muka ambata suka tabbata qarya; har zuwa kar shensu.

Amma hadisi na goma, wanda Mu’awiyah ya umarci da Sa’ad da la’antar Ali Raliyallahu Anhu shi kuwa yaqi. Da muhawarar da ta gudana tsakanin su har ya kafa masa dalilai a kan haka. Hadisi ne .ingantacce. domin imamu Muslimu ya riwaito shi a cikin ingantaccen littafinsa. Sai dai darajojin da aka ambata na Ali Raliyallahu Anhu a cikinsa, ba su kevanta da shi ba.

Xauki misalin daraja ta farko: wato barinsa a birnin Madina da manzo ya yi a matsayin waqili, da abin da ya gudana tsakaninsu qari da busharar da manzon ya yi masa. Ka ga ai ba Ali Raliyallahu Anhu ne kawai wanda ya tava waqiltar birnin na Madina ba.

Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama ya sha barin wasu su waqilce shi a Madina, waqilci kuma irin wanda yafi wanda aka bar Ali Raliyallahu Anhu yi xaukaka; domin shi mata da qananan yara aka barshi tsaro. A kan haka ma ne ya koka wa Annabi, har waccan busharar ta biyo baya.

Ga al’ada babu wani yaki da Annabi Sallallahu Alaihi Wasallama zai fita, face ya bar wasu dakarru muminai daga cikin Muhajiruna da Ansaru a Madina, ya kuma na xawa garin magaji kafin ya dawo. A lokacin da zai tafi yaqin Tabuka ne kawai ya tabbata wa Sahabbai cewa yau kan ba a xauke wa kowa fita ba. Sai masu kunnuwan qashi da mata da qananan yara da masu wasu lalurori. To kaji dalilin da ya sa Ali Raliyallahu Anhu ya kyamaci wannan waqilci, har ya koka wa ma’aiki Sallallahu Alaihi Wasallama A kan haka ne Annabi Sallallahu Alaihi Wasallama ya yi masa bayani da cewa: Bai wakilta shi a wannan karo don ya tozarta shi, ko qasqan tashi ba. A’a ya yi haka ne, saboda gamsuwa da irin amanar da yake da ita. Kamar yadda Musa ya kiltar da Haruna saboda yarda da amanar sa. Duk da yake wanda Musa ya wakilta xin Annabi ne. Amma ni babu wani Annabi da zai zo baya na.

Amma idan ka dubi wannan salon na kamantawa da Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama ya yi amfani da shi tsakanin shi kansa da Musa zuwa ga Haruna da Ali, abu ne da ya ta kaita akan “waqilci” kawai. Amma ba gaba xayan mas’aloli ba.

Eh! Ba gaba xaya ba mana. Tunda ai ka ga gaba xayan Bani Isra’ila ne Haruna ya tsare a matsayin waqilin Musa Alaihis Salamu. A ya yin da shi kuwa Ali Raliyallahu Anhu wasu ‘yan tsiraru ne daga cikin musulmi ya waqilci Annabi Sallallahu Alaihi Wasallama tsarewa. Adai - dain lokacin da ya fita tare da mafi yawansu. Ka gani ko.

Wannan kenan. Wani kuma abin da ke qara tabbatar da rashin kasancewar wannan. kamanta wani abin godoro ko alfahri ga Ali Raliyallahu Anhu da ‘yan Shi’ah, shi ne irin yadda Annabi Sallallahu Alaihi Wasallama ya kamanta Abubakar Raliyallahu Anhu da Annabi Ibrahim da Annabi Isa Alaihis Salamu Umar Raliyallahu Anhu kuma da Annabi Nuhu da Annabi Musa Alaihis Salamu ka kuma san darajar waxannan Annabawa huxu tafi ta Haruna nesa ba kusa ba. Kuma kasancewa ma’aiki ya kamanta Abubakar da Umar Raliyallahu Anhuma da biyu daga cikin Annabawa kowannen su, ta sa salon kamanta war nasu zama mafi xaukakar daraja a kan na Ali Raliyallahu Anhu a matsayinsa na wanda aka kaman ta da mutum (Annabi) xaya kacal. Wannan kuma tattare da kasancewar Alin ba farau ba daga cikin Sahabbai, a cikin wannan aiki da muqami na “magaji Gari” mai taqaitaccen wa’adi, balle ya zama qarau.


2.21 Yamutsa Hazon Hadisin Ranar Shura

Idan baka manta ba. A baya kaxan na gaya maka cewa xan Shi’ar nan yana da hanyoyi biyu, da ya kan bi don tabbatar da fifikon Ali Raliyallahu Anhu a kan Sahabbai, wato hanyar kawo hadissan qarya ko yamutsa hazon wasu ingantattu tare da karkata akalar su.

To anan zan kawo maka wani hadisi da ya inganta a cikin Buhari da Muslimu, a kan yadda Usmanu ya zama halifa, ka ga irin yadda xan Shi’ar ya yamutsa hazon sa. Amma kafin haka sai ka fara da gurbataccen, don a qarshe ka she she baki da nagartacce.

Xan Shi’ar ya ce: An samo daga Amiru xan wasilata, wanda wai ya ce: Na kasance tare da Ali Raliyallahu Anhu ranar shura. Sai na ji yana cewa Sahabbai: zan kafa muku hujja a kan fifikona, da wasu abubuwa da babu wani daga cikin ku; Xan Shi’a ko Bobawa da ke iya karkare shi. Sannan wai ya ci gaba da cewa:

Ya jama’a tsakanin ku da Allah, ko akwai wani daga cikinku, da ya kaxaita Allah Ta’ala kafin na?

Suka wai karva masa da cewa: wallahi babu.

Ya ce: tsakanin ku da Allah ko akwai wani daga cikinku, da ke da xan’uwa irin Ja’afaru, wanda ke shawagi a cikin Aljanna kamar tsuntsu, tare da Mala’iku in ba ni ba?

Suka ce: wallahi babu.

Ya ce: Tsakanin ku da Allah ko akwai wani daga cikinku da ke da Ammi kamar Ammi na Hamza; zakin Allah da manzonsa kuma limamin shahidai.

Suka ce: Wallahi babu.

Ya ce: Tsakaninku da Allah ko akwai wani daga cikin ku da ke da mata kamar matata Fatimatu; ‘yar Muhammadu Sallallahu Alaihi Wasallama shugaban matan aljanna?

Suka ce: Wallahi babu.

Ya ce: Tsakanin ku da Allah ko akwai wani daga cikinku, da ke da ‘ya’ya biyu kamar nawa; Hassan da Husaini, shugabannin samarin aljanna?

Suka ce: Wallahi babu.

Ya ce: Tsakanin ku da Allah ko akwai wani daga cikinku daya tava ganawa da Manzon Allah sallahu alaihi wa sallam sau goma, kowace da manzon sadaka kafinta kamar yadda nayi?

Suka ce: Wallahi babu.

Ya ce: Tsakanin ku da Allah, ko akwai wani daga cikinku, da Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama ya ce wa irin yadda ya ce mani: Duk wanda ya yarda dani abin jibinta to ya riqi Ali abin jivinta. Ya Allah ka jivinci al’amarin duk wanda ya jivinci Ali. Ka kuma qi duk wanda ya qishi. Wanda ya ji ya sanar da wanda bai ji ba?

Suka ce: Wallahi babu.

Ya ce: Tsakanin ku da Allah ko akwai wanda addu’ar Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama wadda ya ce: Ya Ubangiji ka koxo mani mafi soyuwar halitta a wurin ka, mu yi kalaci da wannan tsuntsu tare da shi. Ta faxa kansa; ya faxo suka ci tare in ba ni ba?

Suka ce: Wallahi babu.

Ya ce: Tsakanin ku da Allah ko akwai wani daga cikinku, wanda Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama ya shelartawa duniyar Sahabbai cewa: yau zan danqa tutarmu ta yaqi a hannun wani mutum da ke son Allah da manzonsa suke kuma sonsa. Wanda ba zai dawo ba sai da guxar nasara. Ashe ni yake nufi. Hakan kuma ta tabbata. Bayan wasu sun kutsa fagen famar suka dawo suna tavavvi. Ko akwai shi?

Suka ce: Wallahi babu.

Ya ce: Tsakaninku da Allah ko akwai wani daga cikinku, da Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama ya ce wa bani waki’ata: ku bari. Ko wallahi in aiko muku da aradu; wani dakare daga cikin dakarruna. Wanda ni da shi ba banbanci; yi masa biyayya kamar yi mani ne. Kuma sava masa kamar sava mani ne; wanda zai shiga tsakanin ku da kaifin takobi. qarshe ya aika ni?

Suka ce: Wallahi babu.

Ya ce: Tsakanin ku da Allah, ko akwai wani daga cikinku, da Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama ya ce a kansa: Duk wanda ya ce yana so na ba ya son wannan (Ali) makaryaci ne. In ba ni ba?

Suka ce: Wallahi babu.

Ya ce: Tsakanin ku da Allah, ko akwai wani daga cikinku, da mala’iku dubu uku suka yi wa sallama a lokaci xaya, wato; Jibrilu da Mika’ilu da Israfilu. A lokacin da suka kawowa Manzon Allah ruwa daga wata rijiya. In ba ni ba?

Suka ce: Wallahi babu.

Ya ce: Tsakanin ku da Allah, ko akwai wani daga cikinku, da aka gwarzanta daga sama’u da cewa: Yau duk wani takobi in ba “zul-kifaru” ba labari ne. [hadari mai kashe qarfi rana, goga mai kashe qarfi molo] In ba niba?

Suka ce: Wallahi babu.

Ya ce: Tsakanin ku da Allah, waye daga cikinku, Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama ya ce zai yaqi Baqaqe da jajaye da kore-koren musulmi a kan umarnin sa, in ba ni ba?

Suka ce: Wallahi babu.

Ya ce: Tsakani ku da Allah ko waye daga cikinku, Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama ya ce zai yi yaqi don tabbatar da ingantattar fassarar Alqur’ani. Bayan shi ya yi yaqi don samar masa gindin zama, in ba ni ba?

Suka ce: Wallahi babu.

Ya ce: Tsakanin ku da Allah, waye daga cikin ku Allah Subhanahu WaTa’ala ya dawo wa da rana bayan ta faxi don ya sallaci sallar la’asar cikin lokacinta, kamar yada aka yi mani?

Suka ce: Wallahi babu.

Ya ce: Tsakanin ku da Allah ko akwai wani daga cikinku, da Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama ya umarta da karvar sakon surara bara’atu daga hannun Abubakar. Har da Abubakar xin ya tambaye shi cewa: ko an saukar da wani abu ne a kaina? Manzon ya tabbatar masa da cewa: ko alama. Na dai ga babu wanda ya kamata ya isar da irin wannan saqon sai Ali kawai, kamar yadda ya umarce ni?

Suka ce: Wallahi babu.

Ya ce: Tsakanin ku da Allah, waye daga cikin ku, Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama ya ce wa: Babu mai son ka sai mumini, babu kuma mai qinka sai munafuki. In ba ni ba?

Suka ce: Wallahi babu.

Ya ce: Tsakanin ku da Allah, ashe ba kune Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama yayi umarni da’a rufe qofofinku, a buxe tawa ba. Har kuka yi qorafi a kan haka. Ya tabbata maku cewa; ba shi ne yake da sha’awa a kan haka ba. umurnin Allah ne? Ko kun manta?

Suka ce: Wallahi bamu manta ba.

Ya ce: Tsakanin ku da Allah, Ashe ba kune kuka kalubalanci Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama ba, a kan ya xauki lokaci yana ganawa da ni, ranar yaqin Xa’ifa; savanin irin yadda yake ganawa da mutaane. A qarshe ya tabbatar maku da cewa, Allah ne ke ganawa da ni a lokacin ba ni ba. Ko kun manta?

Suka ce: Wallahi bamu manta ba.

Ya ce: Tsakanin ku da Allah, kun manta da cewar da Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama yayi: Ali na tare da gaskiya; gaskiya kuma na tare da shi, duk in da ya yi tana biye da shi?

Suka ce: Wallahi bamu manta ba.

Ya ce: Tsakanin ku da Allah kun manta da cewar da Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama yayi: Haqiqa na bar muku waxansu abubuwa guda biyu masu nauyi; Littafen Allah da mutanen gidana. Ba za ku vata ba matukar kuna rike dasu. Kuma su, ba za su saki hannun juna ba. Ko sun isa gabar kogina?

Suka ce: Wallahi bamu manta ba.

Ya ce: Tsakanin ku da Allah waye daga cikinku, ya saxaukar da rayuwarsa, saboda kariya ga Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama daga mushrikai. Ta hanyar kwanciya a kan shimfixarsa Sallallahu Alaihi Wasallama kamar yadda na yi?

Suka ce: Wallahi babu.

Ya ce: Tsakanin ku da Allah, waye daga cikinku, ya yi gum da Umar xan Abdul-Widdi a lokacin da yakewa musulmi kuce. Ashe bani ne nace masa cas ba?

Suka ce: Wallahi kai ne.

Ya ce: Tsakanin ku da Allah, ko akwai wani da cikinku wanda Allah Subhanahu WaTa’ala ya saukarwa ayar tsarkakewa a kansa, wadda ke cewa: kuma Allah na nufin ya tafiyar da qazanta kawai daga gare ku, ya kuma tsarkake ku tsarkakewa (33:33) kamar yadda ya saukar a kai na?

Suka ce: Wallahi babu.

Ya ce: Tsakanin ku da Allah ko akwai wani daga cikinku, wanda Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama ya ce wa: Kai ne shugaban sahun muminai, kamar yadda ya ce mani?

Suka ce: Wallahi babu.

Ya ce: tsakanin ku da Allah ko akwai wani daga cikinku, da Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama ya tava cewa: Ban tava roqon Allah wani abu ba face na roqa maka kwatankwacin sa; kamar yadda ya ce mani?

Suka ce: Wallahi babu.

Akwai kuma daga cikin irin waxannan hadisai na qarya da xan Shi’ar ke dogaro dasu, hadisin da wai aka samo daga Abu Amru Azzahidu, daga kuma xan Abbas, wanda wai ya ce: Ali Raliyallahu Anhu nada wasu darajoji guda huxu da babu wanda ke dasu daga cikin mutane; Shi ne mutum na farko daga cikin Larabawa da Bobayi, wanda ya yi sallah tare da Annabi Sallallahu Alaihi Wasallama shi ne kuwa wanda tutarsa bata tava faxuwa a kowane yaqi. Shi ne kuma gagarraren damon yaqin hunainu. Shi ne kuma wanda ya yi wa Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama wanka, ya kuma saka shi cikin kabarinsa.

Ka ji kai! Allah da iko shi ke.

Haka kuma xan Shi’ar ya ce wai, Annabi Sallallahu Alaihi Wasallama ya ce: Ni da Jibrilu mun taras da wasu mutane, a daren da akayi mi’iraji dani, ana shatar naman jikinsu. Sai na tambayi Jibrilu ko suwaye? Ya ce sune waxanda ke cin naman mutane ta hanyar giba. Can kuma muka taras da wasu an shashshavesu kamar daudawa. Na tambayi Jibrilu kosu waye? Ya ce kafirai ne. Daga nan sai muka sake hanya.

Isarmu sama ta huxu keda wuya sai ga Ali na sallah. Sai na cewa Jibrilu: Ah! Kai ji Ali har ya riga mu isowa. Sai ya ce mani: wannan ba Ali ne ba. Na ce: To waye? Sai ya ce: wani mala’ika ne Allah Subhanahu WaTa’ala ya halitta a cikinsurar Alin. Wai dalili kuwa mala’ikun da ke hidma faxar Allah ne, da shugabannin su, suka sami kansu cikin matsanancin shauqi da begen Ali, a sakamakon yawan jin darajojinsa da suke ji. Musamman cewar da wai Annabi AllahSallallahu Alaihi Wasallama yayi: Matsayin Ali a wurina kamar matsayin Haruna ne a wurin Musa. Duk da yake babu wani Annabi bayana.

Saboda haka a duk lokacin da shauqin Ali ya motsowa mala’kun sai suzo su kewayi wannan mala’ika mai siffar Ali; an huta dasu kenan.

Kai ka ji magana kamar irinta mata da qananan yara.

Kuma wai xan Abbas ya ce: watarana Almusxafa Sallallahu Alaihi Wasallama na jin nishaxi. Sai kawai muka ji ya ce: Ni bajini ne, xan bajina kuma xan’uwar bajini.

Xan Abbas xin wai sai ya ce: Annabi na nufin: Shi bajinin Larabawa xan bajinin Annabawa Ibrahim. Saboda cewar da Allah Ta’ala yayi: Munji wani saurayi (bajini) yana ambatar su. Anace masa Ibrahim (21:60) kuma shi ne xan’uwan bajinin sahabbi Ali.

Kuma wai wannan magana da kirari da koxa da manzo yayi, ita ce fassarar guxar da Jibrilu ya tashi sama’u yana yi a ranar yaqin Badar yana cewa: Duk takobi yau idan ba “zul-qifari” neba labari ne, kuma duk dakare (bajini) in ba Aliyu ne ba labari ne.

Wai kuma an samo daga xan Abbas xin dai, wanda ya ce: Na ga Abu Zarrin, watarana riqe da labulayyen Ka’aba yana cewa: Wanda ya sanni cikinku ya sanni. Wanda kuma bai sanni ba, to ni ne Abu Zarri. Kuma ku ji ta daga bakina: Da za kuyi azumi ku rame kamar tsarkiya, kuyi ta sallah har ku yi doro kamar baka. Hakan ba zata amfane ku da komai ba. Matuqar baku son Ali.

Tammat! Magana ta qare. Kai ka ji. Wasu dai Allah ya hore masu iya qarya. Kai kasan wannan ko Musailamatul-kazzabu albarka ko?!

To, martanin mu kan zaqaqarun malamai a fagen ilimin hadisi ya haxu a kan cewa gaba xayan abin da xan Shi’ar ya ce an riwaito daga Amru xan wasilatu dan gane da wannan rana ta shura da abin da ya faru a cikinta qarya ne; babu wani abu da Ali Raliyallahu Anhu ya fada mai ko kama da wannan a wannan rana.

Iyakar abin da ya tabbata a wannan rana shi ne, Abdurrahman xan Aufi ya ce wa Ali Raliyallahu Anhu : ina fatar da Allah zaisa in zaveka a matsayin halifa da zaka yi adalci? Ali ya ce: ko shakka babu, da yardar Allah zan yi iyakar qoqarina. Abdurrahman ya kuma sake ce masa: To da Allah zai nufi inyi mubaya’a ga Usmanu a matsayin shugaba fa, za ka yi masa xa’a? Ali Raliyallahu Anhu ya sake karvawa da cewa: Tabbas zan yi.

Kuma irin wannan muhawara ce ta gudana tsakanin Abdur-Rahman xin da Usmanu a kan Ali Raliyallahu Anhu.

A qarshe sai Abdur-Rahman ya fahimci cewa matsayin su duka xaya ne; wato babu wanda keda nufin qin yin adalci da zai zama halifa. Ko yaqi yarda da hukuncin Allah, da xan‘uwansa zai zama. Saboda haka, ba abin da ya rage wa shi illa shawara. Sai ya kwashe kwana uku ya na gudanarda tattaunawa da dai-dakin musulmi a kan wannan mas’ala.

Bari ka ji yadda Buhari da Muslim suka kawo wannan waqi’a a cikin ingantattun littafansu.

Buhari ya ce: An samo daga Amiru da Maimun, a kan abin da ya faru na kashe Umar xan Khaxxabi. Ya ce: qare hidimar kawar da Umar keda wuya sai waxannan manyan Sahabbai suka haxu. Sai Abdur-Rahman ya ce: To, ku zavi mutum uku daga cikinku ku fice masu nauyin jagorancin nan. Nan take zubairu ya ce: Ni na jaye na zavi Ali. Xalhatu kuma ya ce: Ni kuma na jaye na zavi Usmanu. Shi kuwa Sa’ad ya ce: Ni kuma na jaye na zaveka kai Abdur-Rahman.

Sai kuma Abdur-Rahman ya sake cewa: To, waye daga cikinmu zai ba wannan al’amari baya. Mu kuma mu yarda da shi, ya zavi wanda ya ga ya fi dacewa daga cikin biyun, bisa sharaxin kiyaye alfarmar Allah da addinin musulunci. Sai Usmanu da Ali suka yi tsit. Sai Abdur-Rahaman ya ce: ko za ku yarda dani a kan haka? Ni kuma ina tabbatar maku ba zan kasa zabar mafi cancanta daga cikinku ba, da yar dar Allah. Nan take suka karva masa da cewa: mun amince.

Daddale wannan magana a kan haka keda wuya, sai Abdur-Rahman ya kama hannun xaya daga cikinsu (Ali) ya ce: kai dai xan’uwan Manzon Allah ne na kusa. Kuma kana daga cikin na farko-farko na shiga musulunci. Ka kuma san haka. Kuma ka riga ka tabbatar mini, tsakanin ka da Allah cewa, da Allah zai baka halifancin nan, za ka yi adalci. Kuma da zai ba wanin ka zaka yi xa’a. Ko ba haka ba?( Ali ya ce tabbas haka ne) Sai kuma ya kevace da xayan (Usmanu) shima ya tuna masa irin wannan yarjejeniya da suka yi. Shi kuma ya qara tabbatar masa da haka.

Qare wannan shiga da fita keda wuya sai Abdur-Rahaman ya xaga hannun Usman, a matsayin wanda Allah ya zava.

Wannan kenan. Shi kuma wancan hadisi da wannan xan Shi’ar ya yamutsa hazon wannan da shi, cike yake fal da qarya ce qarya ce, irin waxanda Allah ya tsarkake Ali daga furtawa. Kamar hujjar da ya ce Alin ya kafa da matsayin xan’uwansa dana Amminsa da na matarsa. alhali kuwa duk ya fisu girman daraja. Ka ga gaba ta koma baya kenan, inji xan tanoma.

Ko alama Aliyu ba zai yi haka ba, don ya daxe da sanin cewa mafificin mutane a wurin Allah shi ne wanda ya fi kowa jin tsoronsa.

Yan da Abbas zai kafa hujja da cewa: babu wanda ya kai darajata daga cikinku, don ni keda ‘ya’yan ‘yan‘uwa da suka haxa da: Muhammadu Sallallahu Alaihi Wasallama da Ali da Ja’afar Raliyallahu Anhu , ka ga babu abin da ya banbanta wannan hujja ta sa da wacan ta Ali.

kuma da abi zai tsaya nan ma da sauqi. Don alfahari da ‘ya’yan ‘yan’uwa yafi zama xaukaka, bisa yinsa da ‘ya’yan ammi.

Abin kamar dai Usmanu Raliyallahu Anhu ne ya tashi ya bugi qirji ya ce: Akwai wanda ya auri ‘ya’yan Annabi mata biyu kamar yadda na yi? Ka ga babu wani abin alfahari da dogaro a nan. Kuma da shi da wanda ya ce: ko akwai mai mata irin tawa a cikinku, duk jirgi guda ya xauko su. Domin kuwa da Fatima da waxancan ‘ya’ya na manzo mata biyu da Usmanu ya aura duk ba wanda ke raye a daidai wannan lokaci na “shura”. Musanman ma Fatimatu da Allah ya karva bayan kamar wata shidda da rasuwar Annabi Sallallahu Alaihi Wasallama.

Haka kuma cewar da xan Shi’ar yayi, wai alin Raliyallahu Anhu ya ce: ko akwai daga cikinku mai ‘ya ‘ya irin nawa? Da cewar da ya yi wai, Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama ya ce: Ban tava roqon Allah wani abu ba face na rokar wa Ali irin sa. Da kuma wai cewar da ya yi: Ba wanda ya isa ya isar da wannan saqo daga gare ni sai Ali.

Duk waxannan magangannu qaryayyaki ne da ba su da tushe balle makama.

Ita wannan magana kuma ta qarshe, ta cewa babu wanda ya kamata ya isar da wannan saqo daga Annabi Sallallahu Alaihi Wasallama sai xan cikin gidansa, Alkhixabi ya ce a cikin littafinsa: ‘Shi’arud-dini’: magana ce mutanen Kufa suka yayata daga bakin Zaidu xan Yazidu. Wanda yake kuma ana tuhumar sa da shi’anci, da rashin gaskiyar zance. Kuma ta tabbata duk waxanda sukayo riwaya daga gare shi, ba su san komai ba a kansa.

Sannan kuma wannan malami, wato Al-khixabi ya kalli waccan ‘sako’ da ake qoqarin kore cancantar isar da shi ga kowa in ba ahlu Baitin na biyu ba, a matsayin sakon musulunci. Ta wannan mahanga ne ma, ya kafawa ‘yan Shi’ah hujja da cewa: Suna ina Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama ya aika As’ad xan Zurarata zuwa Madina don ya isar wa jama’ar can da saqon musulunci, tare da koyawa Ansaru karatun Alqur’ani da sanin makamar addini. Ya kuma aika al-Ala’u xan Al- Hadharami zuwa baharaini da irin wancan saqo. Abu Musa da Mu’azu kuma zuwa Yaman. Utba xan Asidu kuma zuwa Makkah?

Ka ga da haka malamin ya tabbatar masu da cewa, zancen rashin cancantar wani wanda ba Ahlul baiti ba, ga isar da saqon musulunci ya tashi.

Wani abu kuma wanda ke tabbatar da kasancewar wannan xan Shi’a limamin maqaryata shi ne: hadisin daya ce an samo daga xan Abbas. Wannan hadisi ko shakka babu qarya ce lafiyayya. Xauki misalin cewar da ya yi wai mai riwayar ya ce: Babu lokacin da tutar musulunci ta faxi daga hannun Ali Raliyallahu Anhu a dukkan yaqoqan da Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama yayi. Alhali kuwa babu wanda baisan cewa Mu’ab xan Umari ne, ke riqe da wannan tuta ta Annabi Sallallahu Alaihi Wasallama a lokacin yaqin Uhudu ba. A ranar yaqin Falhu Zubairu ne xan Auwamu ne ke riqe da ita. Wanda har Manzon Allah ya umarce shi da ya kafata a wani wuri da ake kira Al-ityan. Har Abbas yake tambayar sa da cewa: Anya kuwa nan ne Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama ya umarceka da kafa wannan tutar?

Buhari da muslimu duk sun riwaito wannan hadisin.

Haka nan kuma cewar da xan Shi’ar ya yi wai xan Abbas ya ce: Aliyu Raliyallahu Anhu ne ya ari tutar haquri da juriya a ranar yaqin Hunainu, a inda ya tsaya tare da Manzon Allah .

Itama wannan magana qarya ce kamar sauran. Domin kuwa tarihi ya tabbatar da cewa Abbas xan Abdul-mudallib ne da Abu Sufyanu xan Harisu xan Abdul-mudallibi ne suka kasance gidin Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama a wannan rana. Abbas na riqe da ragwamar jakar ma’aiki, a yayin da Abu sufyanu ke riqe da shimfixar da yake kanta, a matsayinsu na hurrasu. Wanda a wannan lokaci ne ma Annabi Sallallahu Alaihi Wasallama ya umarci Abbas xin da ya xaga murya ya kira masa “masu faren kaya da bakar karraba”.

Xan Abbas ya ce: Nan take nayi kururuwa na kiransu. Kuma wallahi irin yadda suka danno zuwa wurina, kai kace saniya ce taji kukan lavovon xanta; suna isowa suna faxar: Ga mu ya Manzon Allah, ga mu. Shi kuwa Annabi Sallallahu Alaihi Wasallama a lokacin ya xau kyarma, ya na kirari yana cewa: Ni Annabi ne haqiqa kuma xan Abdul-mudallibi ne ubana.

Yana qare faxar haka sai ya sauko daga kan jakarsa, ya xibi tsakwankwani da hannun sa, ya watsawa abokan gaba, yana cewa: Allah ka karya su don girman Ka’aba. Abbas ya ci gaba da cewa: Wallahi wannan aiki na Manzon Allah keda wuya sai naga bangonsu yana darewa suna juyawa da baya, har Allah ya kunyata su.

Buhari da Muslim duk sun riwaito wannan hadisin. Amma Buhari cewa yayi Abu Sufyanu xan Harisu ne ke riqe da ragwamar jakar ta Ma’aiki ba Abbas ba. Kuma a wannan martani nasa, cewa Buhari yayi: Abbas ya ce: Ni da Abu Sufyanu mun kafe gindin Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama ranar yaqin Hunainu, har akaci aka suxe.

Ka ji wannan. Shi kuwa zancen cewa, Ali Raliyallahu Anhu ne ya yi wa Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama wanka ya kuma saka shi cikin kabarinsa, magana ce dake da bukatar ‘yar kwarye - kwaryar garan fuska. Domin kuwa babu wani daga cikin: Abbas da ‘ya’yansa da barorin sa shakran. Da wasu Ansaru, wanda bai sa hannunsa a cikin wannan al’amari ba. Illa dai Ali Raliyallahu Anhu shi ne wanda ke wanka jikin ma’aiki kai tsaye, Abbas na bashi umarni a matsayin sa na kan gida, da kuma kasancewar Aliyu mafi cancanta daga cikinsu da xaukar wannan nauyi kai tsaye.


Yüklə 2,75 Mb.

Dostları ilə paylaş:
1   ...   14   15   16   17   18   19   20   21   ...   51




Verilənlər bazası müəlliflik hüququ ilə müdafiə olunur ©muhaz.org 2024
rəhbərliyinə müraciət

gir | qeydiyyatdan keç
    Ana səhifə


yükləyin