Tafarkin sunnah



Yüklə 2,75 Mb.
səhifə25/51
tarix28.10.2017
ölçüsü2,75 Mb.
#17506
1   ...   21   22   23   24   25   26   27   28   ...   51

2.58 Mu Zuba Zuwa

Wannan Martani da muke yiga wannan xan Shi’ar a kan cin mutuncin halifa Usmanu Raliyallahu Anhu da ya yi bai tsaya nan ba. Mun xan yaxa zango ne mu sha ruwa mu koma daga. Yanzu kuma tunda mun nunfasa, to mu zuba zuwa.

Xazu kaxan mun yi qoqarin bayyana dalilan halifan ne a kan wadancan abubuwa da xan Shi’ar ke qorafi, tare da suka. To yanzu kuma, tattare da waxancan dalilai da muka bayyana, mu qaddara halifan bai dace da sawaba. To ko a hakan bai cancanci cin mutunci da tozartawa ba ga duk mai hankali da ilimi.

Domin kuwa a shari’ance babu wanda yafi qarfin kuskure baya ga Annabi Sallallahu Alaihi Wasallama. Wannan ita ce qa’ida, halifofi da waxanda basu ba, duk na iya faxawa a cikin kuskure. Wannan abune ja’izi a haqqinsu. Amma kuma abune mai sauqi ga Allah (subhanahu wa ta;ala) ya gafarta masu zunuban kurakuransu, ta hanyar la’akari da xinbin kyawawan ayyukansu. Ko kuma ya jarabce su da waxansu musibu irin waxanda ke karkare kantar zunubai da iznin Allah. Ko kuma ta wata hanya da ba wannan ba.

To duk kuwa wani laifi da za’a iya cewa halifa Usmanu Raliyallahu Anhu yayi bai wuce masa yin kuskure ba. Kuma a waje xaya yana da wasu sanadaran gafara da malalonsu ke iya shafe zunuban har gaba. Xauki misalin zamansa da sahun farko a shiga musulunci, da qarfin imaninsa, da irin jihadin da ya yi, da sauran ayyukan xa’arsa zuwa ga Allah, ta kuma tabbata cewa Annabi Sallallahu Alaihi Wasallama ya yi masa kyakkyawar sheda tare da albishirin shiga Aljanna a kan waxansu Bala’o’i da za su faxa masa.

To kuma abune tabbatacce cewa halifan ya tuba ga Allah, tuba irin ta cikon sunna, a kan duk abubuwan da ake zarginsa da aikatawa. Kuma ga jarrabawar da Allah Ta’ala ya yi masa da gwagwarmayar musulunci. Wadda ta zama sanadiyar rasa ransa ba tare da ya yi wani fargaba ko zarewa ba. Wannan kisan gilla da aka yi masa da sauran bala’o’i da ya haxu dasu kafin haka na daga cikin nau’o’in sanadaran da Allah kan karkarwa bawansa zunubai saboda su. Gashi kuma ya mutu shahidi.

Ba halifa Usman Raliyallahu Anhu kawai ba. Ko imamu Ali Raliyallahu Anhu qololuwar abin da Harijawa da sauran magabatansa ke zarginsa dashi, bai wuce zama kuskure ba ko zunubi. Kuma shima a wuri xaya yana da tarin ayyuka na alheri, irin waxanda haskensu yafi qarfin duhun zunubi komai girmansa ya bice. Waxanda suka haxa da kasancewarsa xan gaban goshin musulunci, da qarfin imaninsa, da jihadin daya zuba, da wasu ayyuka na xa’a waxanda ba waxannan ba. Kuma shi ma gashi Annabi Sallallahu Alaihi Wasallama ya yi masa kyakkyawar sheda, tare da busharar shiga Aljanna. Kuma ta tabbata shi ma ya nemi gafarar Allah ta gaba xaya, ya kuma yi nadammar abubuwan da suka faru sanadinsa ga shi kuma shima ya mutu shahidi.

Ka ga wannan qa’ida bakandamiya, ta isa sa mai hankali kame bakinsa daga abubuwan da dai - daikun Sahabban nan suka aikata, balle har ya yanke masu hukuncin zama wajibi ko mustahabbi. Matuqar buqatar hakan bata taso ba.

Ka ga kenan, a kan haka, ko dai cewar da xan Shi’ar ya yi wai halifa Usman Raliyallahu Anhu ya naxa waxanda ba su cancanta. Ko kuma ya kasance basu cancanta xin ba. Wato ijtihadin nasa ya kuskure kenan. To ko a haka bai cancanta sukar lamiri ba. Don yana da lada a wurin Allah a matsayinsa na mai ijtahidi.

Kuma ba halifa Usman ba, ko Annabawa sukan zaci abu, ya kuma kasance ba hakanan ba.

Xauki mi’salin Wahdu xan Ukubatu, wanda ake ta ganin laifin halifan, saboda ya bashi muqami. Ai tafsirai da hadisai da dama, da littafan sura sun tabbatar da cewa, watarana Annabi Sallallahu Alaihi Wasallama ya tura shi karvo zakka daga wajen wasu Larabawa. Isarsa kusa da tungarsu keda wuya, sai suka yo tururuwa don su haxu dashi. Shi kai gogan naka sai ya zaci sun fito ne don su gama dashi. Nan take sai ya aikawa Annabi Sallallahu Alaihi Wasallama da signal cewa gasu nan za su yaqe shi. Nan take sai ya aika wa Annabi Sallallahu Alaihi Wasallama yayi shirin aikawa da runduna don ta kama masa. Sai Allah Ta’ala ya saukar masa da ayar da ke cewa: yaku waxanda suka yi imani! Idan fasiqi yazo muku da wani babban labari, to ku nemi bayani, domin kada ku cuci waxansu mutane a cikin jahilci, saboda haka ku waye gari kuna abin da kuka aikata kuna masu nadama (49:6).

To ka ga, idan har wani abu na iya shigewa Annabi Sallallahu Alaihi Wasallama duhu, to waye Usman Raliyallahu Anhu da hakan ba za ta iya faruwa gare shi ba?

Amma duk da haka na san fitsararrun (‘yan Shi’ah) na iya cewa, ai bayan faruwar haka ne Usmanun ya naxa shi.

To, sai mu karva masu da cewa, ai qofar tuba buxe take kodayaushe. Ai ta tabbata a zamanin Annabi Sallallahu Alaihi Wasallama cewa Abdullahi xan sa’ad xan Abu Sarhu yayi ridda. Amma kuma yazo gaban Manzo ya faxi yana ahi yana tuba. Kuma Manzon ya karvi tubansa bayan ya riga har ya yanke masa hukuncin kisa.

Idan ba a karvar tubar mai laifi, meyasa Annabi Sallallahu Alaihi Wasallama ya karvi ta wannan?

Wannan kenan. Kuma ko da bayan naxa shinne, ta bayyana cewa shi ba mutumin kirki ba ne. Hakan baza tasa a zargi halifan da komai ba. Don ai ko Ali Raliyallahu Anhu daga baya, wasu hakimansa sun bayar daba yada ake zato ba. Kuma haka bai zama abin suka da qorafi a kansa ba. Iyakar abin da ake iya cewa halifa Usmanu yayi shi ne, naxa wasu mutane, alhali kuma yasan akwai waxanda suka fisu cancant. To ko a hakan bai cancanci suka ba, don al’amari na ijtihadi ne.

Ko kuma a ce, son da yake wa danginsa yaba shi karkata gare su, har hakan tasa ya zaci sun fi kowa cancanta da mukaman. Kuma hakan lalle laifi ne. to ko a hakan ba a binda ya gano shi. Domin kuwa mun riga mun yi bayanin yadda Allah ya wanke laifukansu.

Sannan kuma cewar da xan Shi’ar ya yi wai daga baya, sai hakiman na halifa Usmanu suka cika qasa da fasiqanci da varna, maganar banza ce, daba ta isa hujja ba. Domin kuwa faruwar abin bayan naxasu da aka yi, baya nuna cewa ansanda haka kafin naxin. Koma halinsu ne fil’azal. Domin tabbataccen abune cewa, lokacin da halifa Usmanu Raliyallahu Anhu yaji labarin Walidu xan Ukabatu ya sha giya. Bai yi wata - wata ba yasa aka kamo shi ya bulale shi haddi. Haka kuma halifan kan tuve duk wanda ya cancanci tuvewa daga cikin hakiman. Ya kuma tsayar da haddi a kan wanda ya cancanci hakan.

Sannan kuma xan Shi’ar ya zargi halifa Usman Raliyallahu Anhu da arzulta danginsa da dukiyar musulmi. To tafi munji wannan laifi ne, ai halifan gafartacce ne a wurin Allah. Balle ma mas’ala ce ta ijtihadi.

A ta kaice ma dai kai, babu wanda yahau wannan karaga ta halifanci, bayan halifa Umar Raliyallahu Anhu face ya fifita ko kevance danginsa makusanta da wani abu na muqami ko dukiya. Kamar yadda ta tabbata Ali Raliyallahu Anhu ya kama da makusantarsa.

Shi kuwa zancen shan giyar da Walidi yayi bayan naxa shi, kamata yayi ta zama abun yabo ga Usman Raliyallahu Anhu ba suka ba. Domin ya zartar masa da hukuncin Allah. Kamar yadda muka faxa a baya. Kuma Ali Raliyallahu Anhu ne sheda. Don halifan ya umurta da bulala hamsin. Shi kuma ya umurci Hassan a cikin. Da Hassan ya kasa, sai ya umurci Abdulllahi xan Ja’afar. Wanda ya tashi yayi ta zabga wa Walidu bulala baji ba gani. Yana daga kannunsa daga ta azba’in sai Ali Raliyallahu Anhu ya ce masa: ya isa haka nan. Su Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama da Sahabi Abubakar Raliyallahu Anhu suka yi wa mashayin giya. Amma Umar Raliyallahu Anhu har tamanin yayi. Kuma kowanensu sunna ne. Amma dai ni nafi gamsuwa da arba’in.

Muslim da waninsa duk sun riwaito wannan hadisi.

Ka ga a hankalce da shar’arce halifan ne ya zartar da hukuncin, ba Ali Raliyallahu Anhu ba tunda shiya bashi umurni.

Sannan kuma xan Shi’ar ya ce wai mutanen Kufa har sai da suka kori Sa’id xan Asi gwamnan da Usman Raliyallahu Anhu ya tura masu, saboda mugun halinsa.

To ka ga wannan magana, tana tabbatar maka da cewa xan Shi’ar nan xan soke ne a kasuwar karatu.

Eh mana! Xan soke ne. domin kuwa fitinar mutane Kufa sananna ce. Korar da suka yi wa wannan gwamna, bata tabbatar da cewa ya yi wani abu da zai cancantar masa da haka. Halinsu ne duk gwamnan aka tura masu haka suke yi masa, sun yi wa Sa’ad xan Abu Wakkas tawaye. Wanda shi ne yaci garin da yaqi, ya karya lagon rundunonin qasar. Yana kuma daga cikin majalisar shawara. Kuma basu tava samun gwamna irinsa ba. Haka kuma sun yi ta qorafi a kan Amru xan Yasir da shi Sa’ad xin da Mugirata xan Shu’ubata da sauran gwamnonin da aka aika masu. Harma da abin yayi yawa, saida Umar xan Khaxxabi ya yi masu mugunyar addu’a da cewa: ya Ubangiji ka dagula lissafin mutanen Kufa yadda suka dagula mani lissafi.

To kuma, mu qaddara cewa wannan gwamna ya aikata zunubin da zai sa mutanen Kufa su kore shi. To meye laifin halifa Usmanu Raliyallahu Anhu a nan. Ai ko daga cikin waqilan Ali Raliyallahu Anhu har ma dana Annabi Sallallahu Alaihi Wasallama an samu da yawa, waxanda suka aikata ayyuka na zunubi. Abin da zai sa a kalli shugaba a matsayin mai laifi a wannan hauji, shi ne, idan ya kasa gurfanar da irin waxannan mutane a gabansa, balle ya hukun tasu. Ko ya kasa kwatowa wani haqqinsa, ko wani abu mai kama da wannan, daga ma’aikatansa.

In ma har dai akwai wani laifi a nan, daya hau kan halifa Usmanu Raliyallahu Anhu mun riga mun baje shi. Balle ma babu shi.

Haka kuma idan baka manta ba. Xan Shi’ar ya ce wai, gwamnan da Usmanu Raliyallahu Anhu ya tura Masar, wato Abdullahi xan Sa’ad xan Abu Sarhu, ya shakewa mutanen qasar zaiti, har sai da suka kai qarar zaluncin da yake masu ga halifan. Amma maimakon ya kwatar masu haqqinsu, sai ma ya qara xaure mashi gindi. Ta hanyar rubuta masa takarda a asirce a kan Ya ci gaba da aikinsa yadda ya saba. Alhali kuwa yaja kunnensa a rubuce bainar jama’a.

To mu ba duk mai hankalin daya dubi wannan magana ya san qarya ce aka yi wa Usman Raliyallahu Anhu kuma da aka zarge shi da haka, saida ya sha billahil - lazi a kan bai ji bai gani ba. Kuma kasan a qa’ida duk abin da ya faxi gaskiya ne, ko bai rantse ba. Iyakar abin da ya tabbata dai shi ne, magatakardarsa Marwanu xan Hakamu ne ya rubuta wannan takarda ta biyu, bada saninsa ba. Su kuwa Misirawa, suka ce: to in gaskiya ne ya ba su Marwanun su kashe. Shi kuwa ya ce: atafau.

To ka ga kashe Marwanu a matsayinsa na kawai wanda ya yi sojan gona bai halatta baza shari’an ce, bai cancanci kisa ba. Kenan qin bayar dashi da halifan yayi dai – dai ne. Kai! Wajibi mane. idan kuwa akwai wani tawili da zai halatta kashe shi, ba wajabtawa ba… to shima qin bayar dashi xin halas ne. babu kuwa wani dalili da zai wajabta kashe shi, in ba ijtihadi ba.

To tafi ma, mu qaddara cewa halifan ya hana a tabbatar da wani abu daya wajabta. Ai idan baka manta ba kuma shi halifan ga vatacce ne a wurin Allah tabbas.

To sai me kuma?

Wata shahararrar qarya kuma da xan Shi’ar ya tafka a cikin wannan magana, itace cewa da ya yi wai halifa Usmanu Raliyallahu Anhu ya yi umurni da kashe Muhammad xan Abubakar. Ka ji kai.

Wannan magana ko shakka babu qarya ce. Domin kuwa duk wanda ya san Usman da irin dattako da adalcin daya shahara dashiya ba zai yi horo da irin wannan aiko kan wani ma, ba Muhammad ba. Kai ba a tava jin yayi irin wannan aika- aika ba.

To tafi ma halifan ya ce a kashe shi. A matsayin Usman Raliyallahu Anhu na nagartaccen shugaba, yana da damar yin haka. Don wajibi ne a kansa, yakare mutuncin talakawansa. Ta hanyar kashe duk wanda, ba a iya hutawa daga fitinarsa sai ta haka. Kuma wannan ba abin suka bane. kuma shi yafi cancanta da a yi wa xa’a idan yayi horo da hakan ba waxanda suka so kashe mansuranu ba. A matsayinsu na ‘yan tawaye. Kuma mavarnata, waxanda ba suda ikon kashe kowa, ko zartarwa kowa da hukunci. Waxanda kuma iyakar hujjarsu ita ce, an zalunci tane, keda haqqin haninta wanda ya zalunce shi ba. Balle har ya kashe shi daxa.

Ko shakka babu Muhammadun nan da kake ji, ya dace da kisa sosai, savanin maroranu. Don fitina da sharri da matsalolin da koyaurshe a gindinsa babusu a na muh’d. Kuma irin shaharar da Marwanu yayi a fagen ilimi da kishen addini shi bayyi taba. tunda har hadisai da dama ke akwai a cikin shihalu na Marwanun. Kuma ma har fatawa malamia kan yi da wasu maganganunsa. Wasu ma na jin yayi tare da Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama.

Qarya ta farko a wannan magana, itace cewa halifa Usman ne Raliyallahu Anhu ya kai Mu’awiyah sham bayan rasuwar xan’uwansa Yazidu xan Abu Sufyanu. Wanda ke gwamna a qasar. Shi kuwa halifa Usmanu Raliyallahu Anhu da yazo, sai ya barshi a sham xin a matsayinsa na gwamna. Kuma Mu’awiyah yayi abun a zo a gani, a wannan qasa ta sham. Don tarihin rayuwarsa ya tabbatar da cewa yana daga cikin gwamnonin da talakawansu ke matuqar godewa, da tsananin so.

A gaida sarkin sarakuna xan Abu Sufyanu. Baban Yazidu hafizin qur’ani.

Ta tabbata a cikin ingantaccen hadisi cewa, Annabi Sallallahu Alaihi Wasallama ya ce: zavavvu daga cikin shuga banninku, sune waxanda kuke so, suke kuma son ku. Kuma kuna yi masu addu’ar alheri suma suna yi maku. Kuma mafi sharrinsu, sune waxanda kuke qi suna kuma qinku. Kuna la’antar su, su ma suna la’antar ku.

Duk abin da za ka ji ance Mu’awiyah yayi, to ya faru ne bayan kisan gillar da aka yi wa halifa Usmanu Raliyallahu Anhu ita kuwa wannan fitina ruwan dare ce game duniya, ba shi kaxai ta shafa ba. Hasali ma Mu’awiyah shi mafi neman salama da zaman lafiya, fiye da sauran waxanda abun ya shafa. Don baka haxa shi da Ashtar An-nakha’I ko Muhammadu xan Abubakar ko Abdullahi xan Umar xan Khaxxabi ko Abul-a’awar as-sulami, ko Hashim xan Hashim al-Murkali, ko Ash’asu xan kasu al-qiniki, ko Busru xan Abu Azda’ata da wasunsu daga cikin magoya bayansa da magoya bayan Ali Raliyallahu Anhu duk yafi dama sosai.

Haka kuma xan Shi’ar ya ce, halifa Usman ya kai Abdullahi xan Amir Basra, inda gwamnan ya aikata miyagun abubuwa yadda yaso.


Martani:

Duk abin da wannan gwamna ya aikata na zunubi, ai yana kansa. Mi ya gano halifa Usmanu Raliyallahu Anhu? tunda babu wanda ya ce ya yarda da ayyukan Abdullahi. Kuma tattare da hakan rayuwar gwamnan cike take da kyawawan ayyuka, waxanda suka sa mutane na matuqar sonsa iyakar zarafi.

Haka kuma xan Shi’ar ya soki lamirin halifan da naxa Marwanu da ya yi, tare da xauko masa wuqa da nama, a sha’anin mulki. Har ya daka masa hatiminsa. Wanda wai a qarshe hakan ta zama sanadiyar kashe shi halifan. Tare da jefa al’umma cikin fitina.
Martani:

Marwanu, shi kaxai, ba shi ne sanadin kashe halifan ba. Abubuwa ne da dama suka haxu. Waxanda suka haxa da qorafe-qorafen da ake yi kan shi Marwanun, da kuma kasan cewar halifan ya sha ruwa sosai shekaru sun miqa. Wanda hakan taba su gwamnonin damar yin wasu abubuwa ba tare da saninsa ba musamman waxanda ake qorafi a kansu amma sanda yawa yake ba Marwanun umurnin canzawa wasu daga cikinsu wuraren aiki ko tuve ma wasu. Shi kuma wani lokaci ya zartar. Wani lokcin kuma ya doje. Mun riga mun fexe buru’I wannan magana har wutsiya.

Sannan kuma wani abu da zai qara tabbatar maka da cewa cin amanar Usman Raliyallahu Anhu aka yi har aka kashe shi, shi ne, yayin da ‘yan inna da suke qorafi a kansa, saida ya wayar masu da kai a kai. Kai! Har saima da a qarshe, ya yarda da zai tuve duk wanda ba su so . kuma zai danqa mabuxan Baitul’mali hannun wanda suke so. Ya kuma tabbata masu cewa babu kwabo xaya daya tava xauka daga Baitil malin yaba wani, face ya nemi yarda da shawarar sauran Sahabbai. Kai har dai suka yi kwatakyas. Hakan tasa Sayyida Aisha Raliyallahu Anha cewa: basu kashe shi ba saida suka matseshi kamar yadda ake matse tufa, suka raba shi da komai.

Allah ya isa!

Iyakar abin da ake cewa shi ne wai, sun kama wata takarda ne, a kan hanya dasa hannun halifan, inda a ciki wai ya yi umurni da a kashe su. A qarshe kuma halifan ya rantse masu da Allah a kan cewa baida masaniya da wannan takarda. Suka ce to, lalle ko maruranu ne ya rubutata. Saboda haka lalle abasu shi su kashe. Shi kuwa halifan, ya ce, atafau.

Wai a kan haka ne suka kashe shi.

To, mu qaddara cewa wannan labari gaskiya ne, marwanu ya rubuta takardar, kuma halifan yaqi bayar da Shi a kashe. To,ai wannan bai isa halatta jininsa ba, balle a kashe haka kaddan. Don ko shi Marwanun zunubinsa kawai na shirya a kashe sune, in har ta tabbata ya yi hakan, amma ai gurin nasa bai cika ba, balle. Niyar kashe mutum ba tare da wanzarwa ba, bata wajabta kashe mai ita. Ka ga kenan ko Marwanun bai cancanci kisa ba balle halifan.

Amma, eh! Gaskiya ne irin wannan ya kamata a ladabta shi, a kore shi, a kuma yi kaffa - kaffa dashi. Ko wani abu mai kama da haka. Amma a ce a kashe shi, wala.

Haka kuma xan Shi’ar ya soki lamirin halifa Usmanu Raliyallahu Anhu da cewa yana kwasar dukiyar Baitul-mali yana ba danginsa da makusantansa. Wai akwai ma lokacin da yaba wasu Quraishawa dake auren ‘ya’yansa mata dinari dubu.
Martani:

Ina xan Shi’ar ya samo wannan magana? Ba muna musun irin kyautar da halifan ya shahara da ita ne ba. Domin kuwa ko tauraruwar sarfa ta sanda zamansa. Gaskiya ne halifa Usmanu Raliyallahu Anhu na cikawa makusantansa aljifansu. Amma kuma da kowa yake, shi ba indararo bane, kaba daji ruwa gida bai sha ba. A’a shi a duk lokacin daya ba Albasa ruwa sai ya ba yalo. A’a ba musu muke ba. Wannan adadi da xan Shi’ar ya faxa, shi muke son mu ji maqaryacin malamin daya gaya masa shi.

Wannan magana ko shakka babu qarya ce. Ba Usmanu Raliyallahu Anhu ba, babu wani halifa daga cikin shiryayyun halifofin Manzo, daya tava kyautar irin wannan maqodan kuxi. Halifa Mu’awiyah shi ne tarihi ya tabbatar da cewa ya bi sawun halifa Usmanu a fagen kyauta. Toko shi iyakar adadin abin da aka riwaito, daya kan ba waxanda yake lallashi don su bi shi bai tava wuce dirhami dubu xari ko dubu xari uku ba. Kamar yadda ya tava ba Hassan xan Ali Raliyallahu Anhu an kuma riwaito cewa ma Hassan xin kawai ne ya tava dacewa da irin wannan babbar riba. Wasu malama na jinma Mu’awiyah ya sha gaban Usmanu Raliyallahu Anhu a irin wannan kyauta ta lallashi.

Eh! Gaskiya ne halifa Usman Raliyallahu Anhu na irin wannan kyautawa makusantansa, wadda har taja masa fitinu. Amma kuma mun riga mun kawo hojjojunsa a kan haka. Za mu kuma qara warware matsalar nan gaba kaxan.

To kuma duk aje ma wannan. A taqaice dole ne kowane shugaba ya gyara tsakaninsa da wasu mutane, don su ji daxin bashi kariya daga duk wanda ke son cuta masa. Musamman idan bai sami irin yadda Abubakar da Umar Raliyallahu Anhuma suka samu ba, na kasancewar talakawansu tare dasu fai da voye.

Wannan shi ne uzuri na farko daya kamata a yi wa halifa Usmanu Raliyallahu Anhu idan ana yi wa Allah.

Uzuri na biyu kuma da ake iya yi wa halifan shi ne: a matsayinsa na ma’aikacin gwamnatin musulunci, kuma wanda ke hidimar dukiyarta,to yana da haqqi na musamman a ciki. Don cewa Allah Ta’ala yayi: da masu aiki a kansu (9:60) a kan wannan dalili ne gaba xayan musulmi suka yi ittifaqi a kan cewa komi wadatar wanda ke hidimar irin wannan dukiya, to yana da haqqi a cikinta. Kuma ba laifi bane don ya karve shi.

Haka kuma xan Shi’ar ya ce wai: xan Mas’ud na ganin la’anin halifa Usman Raliyallahu Anhu saboda irin waxannan xabi’u nasa, harma yana kafirta shi.

To duk mai hankali da ilimi yasan wannan magana qarya aka yi wa xan Mas’ud babu wani malami daga cikin malamai manaqalta sirrin riwaya daya tava riwaito irin wannan magana. Hasali ma, abin da suka riwaito xan Mas’ud xin na cewa, a lokacin da aka naxa halifa Usmanun Raliyallahu Anhu shi ne: mun naxa mafi girman daraja. Bamu bayar ba.

Wani kuma abin da ke qara tabbatar da kasancewar wannan magana ta xan Shi’ar qarya, shi ne, kasancewar shekarun farko na halifancin Usman Raliyallahu Anhu babu wanda aka ji yana sukar lamuransa a cikinsu. Sai da aka kai ga kashin qarshe na shekarun, sannan aka fara jin qorafe -qorafe a kansa dangane da wasu abubuwa, da masu qorafe -qorafen keda uzuri a cikin wasu daga cikisu. A yayin da kuwa halifan ne keda uzuri a cikin mafi yawansu.

Wannan qorafi da xan Shi’ar ke son mayar wa wani abu, wanda xan Mas’ud keyi a kan halifa Usmanu, na daga cikin waxannan qorafe - qorafe. Abin da ya faru kuwa shi ne xan Mas’ud ya daxe yana hushi da halifan, saboda danqa aikin sake rubuta Alqur’ani da ya yi ga Yazidu, maimakon ya danqa masa. Bayan haka kuma ya umurci Sahabbai da shafe nasu Qur’anan, su bar aiki dasu, su dawo ga wanga da Yazidu ya rubuta daga baya. Kuma sai mafi yawan Sahabbai suka goyi bayan halifan: suka bar xan Mas’ud. Ka ji iyakar abin da ya faru. Amma zancen kafirtawa, bamu da wannan labari: kai, babu shi sam.

To kuma idan dai har ana son gaskiya, zancen halifan shi ne abun xauka. Bana xan Mas’ud ko Amru ko Abu Zarri ba, ko waninsu. Don babu wanda darajarsa daga cikinsu ta kai ta Usman Raliyallahu Anhu kamar yadda dalilai da dama suka tabbatar.

Wannan ta vangaren su kenan. To vangaren kuwa wanda abin bai shafa ba. Amatsayinsa na xan kallo, kamata yayi ya fahimci, halifa ne ya kamata ace yana fushi da xan Mas’ud, ba shi yayi da shi ba. Amma saboda dattakonsa bai yiba, balle a riwaito. Ko kuma idan ya tashi bayar da labarin mas’ala, ya tsetsefeta, tsetstsefewa irin ta masu ilimi da adalci. Idan kuwa matsayinsa bai kai na haka ba, to ya tsaya ga faxar darajojinsu da kishen addininsu, ya fita batun yin alqalanci tsakaninsu. Don yayi kaxan. Sauran abin da ya gudana tsakaninsu na yaya da ja-in-ja, kuma, ya barwa Allah sani.

Kuma bisa wannan dalili nema, malamai su kayi umurci musulmi dasa ido kawai, da kame baki daga duk abin da ya gudana a tsakanin Sahabbai. Domin kuwa Allah ba zai tambaye mu a kan al’amarin ba.

Kuma a qoqarin qarfafa wannan mataki na kame baki ne, Umar xan Abdul’aziz ke cewa: tunda Allah ya sabani da hannu cikin zubar da wadancan jinane na musulmi, toba kuwa zan tsoma halshena cikinsu ba.

Wani magabancin kuma abin da yake cewa shi ne, abin da Allah Ta’ala ya ce: waccan, wata al’umma ce,ta riga ta shige, tana da abin da ta sana’anta, kuma juna da abin da kuka sana’anta. Kuma baza a tambaye kuba daga abin da suka kasance suna aikatawa(2:134).

Amma kuma ka sani, haka ba zata hana, idan wani xan bidi’a ya tsiru yana sukar lamirin wadancan magabata, da abin da basu jiba basu gani ba, a tashi a yaqe shi, ta hanyar amfani da ilimi da adalci, har a karya lagonsa.

Haka nan kuma abin da xan Shi’ar ya ce, wai Amru ya ce: Usmanu Raliyallahu Anhu ya kafirta, kafirci mabayyani. Har kuma Hassan xan Ali Raliyallahu Anhu ya kwave shi. A qarshe kuma wai Alin Raliyallahu Anhu ya cewa Amrun “ sai dai idan kaine ka kafirce wa Ubangijin da Usman Raliyallahu Anhu ya yiimani dashi.

Duk waxannan maganganu, qarairayi ne, da basu tava faruwa ba a tarihin musulunci.

Wannan kenan. Haka kuma cewar da ya yi wai, hawan Usmanu Raliyallahu Anhu keda wuya sai yasa aka yi wa xan Mas’ud dukan tsiya har ransa ya fita. Wannan magana qarya ce bai sa ittifaqin ma’abuta ilimi.

Babu abin da ke tsakanin halifa Usmanu da xan Mas’ud Raliyallahu Anhu sai alheri. Domin haka ne ma a lokacin da Usmanun Raliyallahu Anhu ya zama halifa, bai xauke shi daga Kufa ba, inda yake, har sai da hukuncin Allah ya gudana kansa. Amma ba Usmanu ne Raliyallahu Anhu ya kashe shi da duka ba.

To kuma ko da ta tabbata cewa halifan yasa an yi wa xan Mas’udun dama Amru dukan, wannan ba zai zama abin suka gare suba, har shi halifan. Domin dukansu ‘yan aljanna ne tun duniya. Mun kuma shedi haka. Kuma suna daga cikin manya -manyan waliyan Allah masu taqawa.

Kuma ko bayan haka, mun riga mun yi bayanin cewa abu ne mai sauqi sosai waliyen Allah ya aikata laifin da zai cancantar masa da wata azaba ta shari’a, balle gargaxi (ta’azur).

Tomu dawo ga zancen Ammru. Wanda xan Shi’ar ya ce wai Annabi Sallallahu Alaihi Wasallama ya ce shi wata fata ne daga cikin fatun idonsa Sallallahu Alaihi Wasallama da kuma yake jin wasu la’ananu ‘yan tawaye za su kashe. Waxanda ke fatar Allah ba zai sasu cikin jirgin cetonsa ba a ranar qiyama.

Ina son ka xan kalli wannan magan da kyau.

Iyakar abin da ya inganta daga cikinta shi ne, cewa Annabi ya ce: Ina jin wasu la’anannu ne ’yan tawaye za su kashe shi to kuma ko ita wannan kalma wasu malamai sun raunana ta, a matsayin hadisi. Daga cikin malaman kuwa akwai: al-Husaini al-Karabisi da wasunsu. An kuma riwaito imamu Ahmad shima ya raunana hadisin. Ka ga da sakal kenan.

Sauran abin da kuma ba wannan magana ba, a cikin hadisin, duk qarya ce, karanta aka yi a matsayin toliyar zamba. Babu wani malami daga cikin malamai masana isnadi da ya riwaito ta.

To kuma majata ta tabbata Manzon ya faxi duk tarkacen da xan Shi’ar ya faxa. Hakan ba zata daxa Ammarun da komai ba. Balle ta hana a hukunta shi, idan ya yi wani laifi.

Dubi matsayin da nana Fatima keda shi a wurin mahaifinta Sallallahu Alaihi Wasallama. Wanda harta tabbata a cikin ingantaccen hadisi cewa ya ce: ko shakka babu Fatima jinina ce. Duk abin da ya tava ta ya tava ni.

Amma kuma tattare da ha kan manzon ya tabbatar wa duniya, a cikin wani ingantaccen hadisi, da cewa: da Fatima ‘yar Muhammadu zata yi sata wallahi sai na yanke hannunta.

Haka kuma ta tabbata Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama na matuqar son Usamatu, wanda har ya ce a wani ingantaccen hadisi: ya Ubangiji kasan inason Usamatu. Saboda haka ya Allah kaso shi. Ka kuma so duk wanda ke sonsa.

Amma kuma tattare da haka Manzon yayi matsananci hushi tare da kakkausan kashedi gare shi, a lokacin daya dahe wani mutum bayan ya furta kalmar shahada. Ya ce masa: ya kai Usamatu! Ya zaka kashe shi bayan ya ce: la’ilaha illal-lah?

Usamatu ya ce: haka Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama ya riqa maganar nan yana ta konkoma ta a kaina, har saida naji ina ma dai a ce sai a ranar ne na musulunta!.

To haka abin yake, babu wanda halifa Usmanu Raliyallahu Anhu ya zartar wa wani haddi ko gargadi bisa jahilci ko zalunci. kuma shi yafi cancanta da a yi masa uzuri, a kuma bashi kariya.

a cikin waxannan masallolin bias ga Ali Raliyallahu Anhu

Bayan wannan kuma xan Shi’ar ya soki lamirin halifa Usmanu Raliyallahu Anhu da cewa wai, ya dawo da Hakamu xan Abdul-Abi a wurinsa, da xansa Marwanu a garin Madina. Bayan manzo Allah Sallallahu Alaihi Wasallama ya koresu tsawon rayuwansa. Kuma halifa Abubakar da Umar Raliyallahu Anhuma suka qi maikar dasu, sai shi. Har ma ya naxa Marwanu a matsayin magatakardansa. Alhali kuwa Allah Ta’ala ya ce: Ba zaka sam mutane masu yin imani da Allah da ranar Lahira suna soyaya da wanda ya savawa Allah da Manzonsa (58:22).

Wannan magana ko kaxan babu qanshin gaskiya a cikinta. Domin dai Hakan xin nan xan Abi, na xaya daga cikin mutane dubu da suka Musulunta ne, ranar da aka ci garin da yaqi. Kaji wanan ko? Sannan shi kuma Marwanu, xansa, shekarunsa a lokacin basu wuce bakwai ko aqalla ko akasansa ba da kaxan. Ka ga yazo ne matuqa. Wanda ba wani zunubi kansa da zai sa har Annabi Sallallahu Alaihi Wasallama ya kore shi a kauran kanoli. Kuma a wannan lokaci ba a ba fursunoni yaqin da aka sallama damar zama cikin garin Madina, balle ace an kore Hakim daga cikinta. In har korace, sai dai Annabi Sallallahu Alaihi Wasallama, ya kore shi daga Makka ba Madina ba. Idan kuwa har kaddarata sa aka bashi damar zama Madina. Kuma kora tazo, to sai dai a kora shi zuwa Makka. Amma da mafi yawan ma’abuta ilimi babu yarda da koransa akayi. Abin da suka ce dai ya tafi ne a ra’ain kansa.

Ka ga dawowa da shi bisa wannan lokaci ba lafi bane.

Sannan shi kuma Marwanu mun riga mun gaya muku cewa yaro ne qarami a wannan lokacin ko da Annabi Sallallahu Alaihi Wasallama ya rasu Marwanu bai balaga ba, bisa litaffin ma’abuta cikin qololuwan shekarunsa a wannan lokacin ba sufi goma ba to ya za’ace Annabi Sallallahu Alaihi Wasallama ya kori shi wannan lokaci.

To a kan me?

Kuma tarihi ya tabbatar da cewa qoriya da samartakar Marwanu duk na musulunci ne bai da voye; mutun ne mai yawan karatun al-qurani da neman ilimi fiqihun addini. Haka rayuwarsa ta xore a kan nagarta har lokacin da fitinoni suka kuma kai. To don Allah meye laifin wanda ya haxamu na wannan matsayin magatakardarsa?

Wani abin la’akari kuma shi ne ko da wannan fitina ta faru, ba a kan Marwanu kawai ta tsaya ba; tabi ta kan har waxannda suka fi shi daraja. Kuma baya cikin waxanda suka savawa Allah da Manzonsa. Shi kuma Mahaifinsa yana daga cikin fursunoni da aka saka masa in gantacen imani. Wasu kuwa abin nasu gashi nan dai. Duk kuwa zunubin da ake yi wa mai shita’aziri, ba wajabta kasancenwarsa munafiki a voye.

Haka kuma idan baka manta ba xan Shi’ar ya ce wai halifa Usmanu Raliyallahu Anhu ne ya kori Abu Zarri zuwa Rabzah, bayan ya yi masa dukan tsiya. Alhali kuwa Annabi Sallallahu Alaihi Wasallama ya ce shi ne mafi gaskiyar zance a duniya. Kuma Allah ya yi wa Manzon wahayi da cewa yana son wasu Sahabbansa guda huxu, kuma yana horonsa dashi ma yaso su. Kuma na qarshen waxannan Sahabbai shi ne Abu Zarri.

Allah da iko shike. Kai ka ji wannan tsari.

To mu dai iyakar abin da muka sani, kuma wanda za mu mayarwa ‘yan shi’an nan martani dashi, shi ne: Abu Zarri shi ne a qashin kansa ya bar birnin Madina ya koma Rabza. Saboda rikittan dake faruwa tsakaninsa da mutane. Sakamakon qoqrin da yake yi na tilasta masu zama zahidai. Shi mutum ne salihi mai zuhudu. Wanda kuma ke jin zuhudu wajibi ne. kuma duk abin da mutum ya rage hannunsa bayan buqatarsa ta yini ta biya. Allah zai yi masa azaba dashi gobe qiyama. Harma da Allah ya karvi na Abdulrahamu xan Aufu. Aka samu ya bar dukiya. Sai Abu Zarri ya yanke hukunci cewa Allah zai yi masa lalas da ita gobe qiyama a wuta. To ashe kai ka je.

To kuma da yawa halifa Usmanu Raliyallahu Anhu ke qoqarin ganar da Abu Zarri, ta hanyar ilimi cewa al’amani ta ba haka ba. A haka har watarana ka’abu ya tsoma baki ya kuma goyi bayan lafiya, har Abu Zarri xin ya kai masa duka. Kuma wani abu mai kama da haka ya tava faruwa tsakaninsa da Mu’awiyah a kan haka a sham.

Sannan kuma wannan ra’ayi na Abu Zarri ya savawa abin da gaba xayan halifofi shanyayyu da sauran Sahabbai da tabi’ai suke a kai.

To kuma uwa uba ya savawa abin da ingantattar sunnar Annabi Sallallahu Alaihi Wasallama ta tabbatar. Kamar inda Manzon ke cewa: babu zakka a cikkin abin da ba kai auziqi ko zandi ko awaki biyar ba.

Ka ga a nan Manzon ya tabattar da halarcin aje abin da bai kai xayan biyu ba, ba kuma tare da an fitar masa da zakka ba. Kuma ko da mai shi baya da buqata dashi. ai buqatar ba sharaxi bace a nan.

Bayan wannan kuma jumhuran Sahabbai sai suka fasara waccan kalmar ta “kanzin” dukiyar dake jawo azabar Allah gobe qiyama ga mai ita, da cewa itace. Dukiyar da ba a fitar da haqqin Allah daga cikinta. Komai yawan ta ko qanqancita.

Ka ga kenan Abu Zarri ya jefa kansa a wannan lokaci, a cikin matsalar son wajabta wa mutane abin da Allah bai wajabta masu ba. Ya kuma ga laifin mu a kan abin da Allah bai ga yayi ijtihadinsa ne. kuma Allah zai bashi lada a kai, kamar yadda zai bayar ga takwarorinsa ijtahidai.

To a kan wannan dalili ne Abu Zarri ya ga bari ya batse kansa, ya koma Rabza. Ba don Usmanu Raliyallahu Anhu nada wani mugun nufi a kansa sannan kuma maganar kasancewar Abu Zarri xin alfahari ne ba. Kuma hakan bata nuna cewa darajarsa ta fita kowa. Hasali ma, a ingantacen hadisi, shi mumini ne mai rauni kamar yadda Annabi Sallallahu Alaihi Wasallama ya tabbatar, inda ya ce: ya kai Abu Zarri! Na riga na gane kai mutum ne mai rauni. Duk da yake kuma ina so maka abin da nake sowa kaina. Amma ina ganin bai kamata a shugabantar da kai ko da a kan mutum biyu ba. Ko a baka dukiyar maraya.

Wani hadisin kuma dake qara walwale wannan, tare da fitowa da matsayin Abu Zarri na haqiqa, savanin wancan da xan Shi’ar ke son qaraba mana shi ne, cewar da Annabi Sallallahu Alaihi Wasallama a wani igantacen hadisi: mumini mai kaza da kaza shi ne mafi alheri da soyuwa a wurin Allah, bisa ga mumini raunana. Amma kuma akwai alheri aikin kowanensu.

To ka ga idan haxa hancin waxannan hadisai biyu wuri xaya, sai kace: muminai ‘yan majalisar shura, irinsu Usmanu da Ali da Abdurahama xan Aufu, waxanda suka cancanji zama halifofi da sonransu, shi ne muminai kafata kuma masu kazar - kazar. Shi kuma Abu Zarri da takwarorinsa, masu cikin hali da halittarsa sune raunana. Kenan waxannan sunfi shi falala.

Shi kuwa wannan hadisi, a cikin wannan lafazi da xan Shi’ar ya kawo, hadisi ne mai rauni. Kai! Qagagge ma, don babu wani isnadi da zai iya xaga darajarsa.

Ka ji wannan!

To yanzu kuma mu dawo ga cewar da ya yi wai halifa Usmanu ya keta alfarmar shari’ar Allah, tunda bai kashe Ubaidullahi xan Umar ba, wanda ya kashe Hurmuzanu, bawan Ali Raliyallahu Anhu bayan kuma ya musulunta. Kuma wai saboda haka Alin (Sarkin Musulmi) yayi tsaye a kan shi ko sai ya zartar wa Ubaidullahi da hukuncin Allah. Amma wai a qarshe Mu’awiyah ya bashi mafaka.

Sannan kuma wai, inji xan Shi’ar, halifa Usmanu Raliyallahu Anhu yaso yayi ko oho da hukuncin shan giya. Wanda ya hau kan Walidu xan Uqbata. Sai da Ali Raliyallahu Anhu ya xaukarwa abin matakin soja; ya zartar da hukuncin a kansa, ya kuma rufe caftar da cewa: Ai ba ta yiwuwa a tozartar da hukuncin Allah ina raye.


Yüklə 2,75 Mb.

Dostları ilə paylaş:
1   ...   21   22   23   24   25   26   27   28   ...   51




Verilənlər bazası müəlliflik hüququ ilə müdafiə olunur ©muhaz.org 2024
rəhbərliyinə müraciət

gir | qeydiyyatdan keç
    Ana səhifə


yükləyin