Tafarkin sunnah



Yüklə 2,75 Mb.
səhifə27/51
tarix28.10.2017
ölçüsü2,75 Mb.
#17506
1   ...   23   24   25   26   27   28   29   30   ...   51

Martani:

Eh! Gaskiya ne wannan abu ya faru. Amma malamai masana sirrin riwaya sun tabbatar da cewa qarya ce, Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama bai ce: Allah ya la’anci duk wanda wannan runduna ta bari tasha ba. Kuma babu wani isnadi dake tabbatar da cewa ya ce haka. Babu wani littafi na hadisi daya sanda wannan magana asalata. Kuma tarihin musulunci ya tabbatar da cewa imanin Sahabbai ba zai bari su qi fita tare da Usamatu ba, daya fitar. Shi ne da kansa ya ga bai dace su fita a lokacin ba, saboda ganin halin da Annabi Sallallahu Alaihi Wasallama ke ciki na rashin lafiya. Har ya ce masa. Ya Manzon Allah! Ya zan fita in barka cikin wannan hali? In koma ina tambayar fatake yadda ka kwana? Daga nan sai Annabi Sallallahu Alaihi Wasallama ya yi masa izinin lalle sai Usamatun ya tafi, ba abin da zai hana shi zuwa. Da kuwa sauran Sahabban da aka shirya subi shi sun bishi. Don ta tabbata babu wanda ya bari jirgin rundunar ya bar shi tasha, lokacin da ya tashi, bayan rasuwar Annabi Sallallahu Alaihi Wasallama sai fa wanda shi Usaman ya yi wa izinin tsayawa saboda wani jihadin.

Sannan kuma kan malamai ya haxu kan cewa babu sunan Abubakar Raliyallahu Anhu cikin jerin sunayen waxanda ya kamata su fita yaqin tare da Usama. Amma an riwaito cewa na Umar Raliyallahu Anhu na ciki. Kuma tuni Barden ya xaura tamantaka yayi shirin fita, da lokacin ya yi.

Amma sai Abubakar Raliyallahu Anhu ya nemi izinin Usaman a kan ya bar masa Umar Raliyallahu Anhu don ya kama masa wani jihadin. Aka kuma yi sa’a kwamandan ya amince. Amma kuma karka manta zaman Sahabi Abubakar halifa ke da wuya, ya dage a kan lalle wannan runduna ta tafi. Amma sauran Sahabbai suka nuna masa haxarin daka iya faruwa a cikin fita tunda wuri haka. Don magabata sun koxa wuqaqensu da jin rasuwar Annabi. Amma duk da haka halifan ya nace a kan wannan Umurni nasa, yana mai cewa: Wallahi ba zan saukar da tutar da Annabi Sallallahu Alaihi Wasallama ya xaga ba. Sai dai kome ke tafasa ya kone.

Tirqashi ka ji maza. A gaida Uban Aisha saxaukin fama.

Haka kuwa aka yi, sai da rundunar ta tafi.

Wannan shi ne ingantaccen tarihin abin da ya faru. Amma sai gashi sarakunan qaryar duniya na yayata cewa wai Abubakar da Umar Raliyallahu Anhuma anga daga cikin waxanda Annabi Sallallahu Alaihi Wasallama ya shata su tafi yaqin tare da Usama. Kuma wai dasisa ce Manzon ya killa masu, don kada su hana Ali Raliyallahu Anhu kaiwa ga halifanci, idan ya cika suna kusa. Ka kuwa san fa mai kera irin wannan qarya sai mafi jahilcin mutane da tarihin Manzon da Sahabbansa.

Abin da ya tabbata shi ne; tsawon kwanukan jinyar Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama Abubakar Raliyallahu Anhu ne keba mutane sallah, da Umurninsa. Kuma kowa ya san haka. Da Annabi yaga dama, yana iya naxa wanda zai gade shi a lokacin. Kuma Sahabbai ba za su qiya masa ba. Kuma ko shakka babu Muhajiruna da Ansaru na yin layya da duk wanda yaqi bin umurnin Allah da Manzonsa. A matsayinsu na waxanda suka yi gwagwarmayar kafa addinin har ya kai gaci.

Umurnin Manzon Allah ba zai tava faxuwa ba matuqar waxannan na raye. Da Manzon yasa Ali Raliyallahu Anhu ya waqice shi ga limancin sallah, ko aikin hajji, ya kuma sa Abubakar da sauran Sahabbai qarqashin ikonsa. Ko ya ce masu: Ga Aliyu nan shi ne na zava ya zama shugabanku (halifa) idan na qaura. Babu wanda ya isa ya ce masa a’a. Kai ka san haka.

A shirye gaba xayan musulmi da Muhajiruna da Ansaru suke suyi masa xa’a da zai ce haka. Saboda babu wanda Ali Raliyallahu Anhu ya kashe wa xan’uwa daga cikinsu balle yaqi shi.

Ah! Kuma inda Manzon na sone ya korewa Ali Raliyallahu Anhu su, don haka ya tura su yaqi tare da Usama. To da abin ya faskara, sai ya ce wa musulmi: kada wanda ya yi wa xayan su bai’as. Shikenan ba mai yi. Babu wani tsoro da zai ji a cikin faxar haka. Saboda tabbacin samun taimakon Allah da yake da shi. Kuma ga Muhajiruna da Ansaru kewaye dashi. Waxanda da zai hore su da kashe iyayensu da ‘ya’yansu, nan take ne.

Kuma ma me yayi zafi tsakanin Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama da Abubakar da Umar Raliyallahu Anhuma wanda tarihi bai sani ba, balle ya faxa, har da haka zata kasance? Ai surar bara’atu ta sauka daga wurin Allah. Ta tona asirin munafukai, ta fito dasu a fili, musulmi kowa ya sansu. Manzo da gaba xayan al’umma suka yi tir da Allah waddai dasu.

Amma aka ci aka suxe, Abubakar da Umar Raliyallahu Anhuma na nan a kan matsayinsu na mafiya zama kusanci ga manzon. Mafiya girma, soyuwa da cuxanya dashi dare da rana. Kuma waxanda suka fi kowa qaunarsa, da biyar umurninsa, da yarda da ra’ayinsa da xaukaka martabar addinin da yazo da shi.

Ka ga a wannan matsayi nasu, ya savawa hankali a ce kuma, suna daga cikin waxanda mutane da surar Bara’atu ta tonawa asiri. Kuma Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama ya yanke kowace irin hulxa dasu bayan saukar surar. Amma kuma har Allah ya karvi rayuwarsa babu wanda ya keso daga cikin mutane, da girmamawa kamar Abubakar Raliyallahu Anhu .

Bayan wannan kuma sai shaharastanin ya ce: Savani na uku kuma shi ne wanda ya faru a kan rasuwar Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama .

Martani: Eh! Ko shakka babu al’amarin rasuwar Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama yaya shige wa Umar Raliyallahu Anhu duhu a farkon lamari, amma safiya nayi, ya dawo cikin hayyacinsa, ya kuma sakankance cewa dai lalle Manzon Allah ya qaura. Bayan haka kuma ya tabbatarwa sauran musulmi da cewa, matakin da ya hau jiya kuskure ne. Kuma daga nan sai kura ta kwanta komai ya koma daidai. Kuma lafazin hadisin na haqiqa ya savawa yadda shahrastani ya shimfixa al’amarin.

Abin da yazo a cikin Buhari da Muslim, a hadisin da aka riwaito daga xan Abbas, wanda ya ce: Umar na cikin magana, sai ga Abubakar Raliyallahu Anhu ya fito, ya ce: saurara Umar, zauna. Umar yaqi ya zauna. Sai ganin haka, mutane suka mayar da hankali ga Abubakar Raliyallahu Anhu don suji abin da zai faxa. Suka fita batun Umar Raliyallahu Anhu sai Abubakar Raliyallahu Anhu ya ce: Bayan haka, ku sani, duk wanda ke bautawa muhammadu, toya sani Muhammadu ya rasu. Duk kuwa wanda ke bautawa Allah to ya sani Allah baya mutuwa. Kuma Allah Ta’ala ya ce: kuma Muhammadu bai zamo ba face manzo, lalle ne manzani sun shuxe a gabaninsa. Ashe idan ya mutu ko kuwa aka kashe shi, za ku juya akan duga - duganku? (3:144)

Xan Abbas ya ce: Wallahi kai kace mutane basu tava sanin Allah ya saukar da wannan aya ba, sai yau da Abubakar ya karanta masu ita. Nan take kuma sai kowa ya riqe ta yana maimaita a zuci, lavvansa na mui –mui - mui.

Ya ce kuma : xan masayyibi ya bani labarin cewa Umar Raliyallahu Anhu ya ce: wallahi qarewar Abubakar karatun wannan aya keda wuya sai gavvaina suka yi sanyi., har kafafuna suka kasa xauka ta. Nan take na faxi zaune na kuma tabbata lalle dai Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama ya rasu.

Ka ji haqiqanin abin da ya faru.

Sannan kuma savani na huxu, kamar yadda Shahrastanin ya ce, wai shi ne wanda ya faru a kan halifanci. Ya ce kuma shi ne savani mafi muni a tarihin musulunci, daya tarwatsa kan al’umma. Domin babu wata qa’ida ta musulunci da aka zare takubba aka ba hamata iska saboda ita, a tsawon zama, kamar yadda aka yi a kan halifanci.



Martani: Wannan magana babban kuskure ce. Domin kuwa –Alhamdu - Lilahi- babu wani yaqi da aka yi a kan halifancin Abubakar ko Umar ko Usmanu Raliyallahu Anhu kai! Ko cacar baki har hanci ya yi zafi, ba a tava yiba a zamaninsu a kan halifanci, balle a kan wani abu na addini. A sane muke da cewa Ansaru sunyi waxansu ‘yan maganganu. Amma kuma da manyan mutane suka yi masu kashedi, nan take kowa ya nabba a. Ka ga ba wani rikici a nan. Don babu mai musun cewa girman darajar mutane irin su Ubaidu xan Huzairu da Abbadu xan Bushrin da wasunsu tafi ta Sa’ad xan Ubaidata, a tsurar ruwan zatin kansu da girman gida. To sune suka sa baki magana ta kare.

Babu wani mutum xaya daga cikin manyan gidajen Ansaru, waxanda Buhari da Muslimu suka riwaito, ta fuskoki da dama cewa Annabi Sallallahu Alaihi Wasallama ya tabbatar da girmansu da cewa: mafi alheri daga cikin gidajen Ansaru, sune:



  1. Gidan bani Najjar

  2. Gidan bani Abdul-As’hal

  3. Gidan bani Hashi

  4. Gidan bani Sa’idata

Amma kuma akwai alheri a cikin gaba xayan gidajen Ansar inji Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama to babu wani daga cikin gidaje uku masu daraja ta farko (1-3) da aka ji ya yi wata jayayya a kan halifancin. Hasalima manyan mutane daga cikin Bani Najjar, irin su: Abu Ayyuba al-Ansarida Abu Xalhatu, da Ubayyu xan Ka’abu da wasunsu duk Abubakar suka a zava.

Haka kuma Usandu dan Hudhainu, barden da ya jagoranci rundunar Ansaru a ranar da aka ci garin Makka da yaki, yana hagu ga Annabi Sallallahu Alaihi Wasallama Abubakar Raliyallahu Anhu na dama. Wanda kuma daya ne daga cikin Gidan Bani Ashhal, shina daya daga cikin Ansarun da suka hada kan al’umma a kan yi wa Abubakar Raliyallahu Anhu bai’a.

Waxanda kawai suka yi cijiya; suka ki yin wannan bai’a a lokacin da kowa ya yi, s;u ne: Sa’ad dan Ubbadata da Hubbatu dan munzir, da wasu ‘yan tsirarun mutane. Ko su kuma sun gano sun yi kuskure. Daga baya suka dawo suka yi wa Siddiqu mubaya’a, ban da Sa’adu dan Ubbadata shi kam cewa ya yi, atafau.

Amma kuma wannan abu da Sa’ad ya yi, ba abin mamaki ba ne. Domin shi ba ma’asumi bane balle. Amma dai mutum ne salihi. Kuma yana da laifuka, waxanda wasunsu sananni ne ga musulmi. Kuma ana fatar Allah ya gafarta masa su. Musamman tunda ya sami shiga sahun ansaru na farko ga shiga musulunci. Waxanda kuma Allah ya yi wa albishirin aljanna tun duniya. Kari a kan yarda da amincewa da ya yi da su.

Kuma cewar da shahrastani ya yi wai gaba xayan Ansaru sunyi ittifaqi a kan Sa’ad din ya walkice su, ya zama halifa, maganace maras tushe balle makama. Domin abin ada ya tabbata daga bakin ma’abuta ilimin riwaya, da kuma tabbataccin hadisai duk sun tabbatar da kasancewar maganar karya bisa ittifaqi. Duk da yake shahrastani da ma kantansa ba maqaryata ba ne a karan kansu. Amma tabbas suna tsakuro abubuwa daga cikin littafan manyan maqaryata ba tare da sun sani ba.

Haka nan kuma abin da wasu ke yaya tawa, an cewa duk wannan rikici da ake ta yi a kan halifanci, wai Ali Raliyallahu Anhu bai da labari. Don yana can ya shagalta da abin da Annabi Sallallahu Alaihi Wasallama ya umarce shi da yi na yi masa wanka da saka masa likkafani da rufe shi da kuma zaunawa wurin kabarinsa. Wannan magana tabbas qarya ce. Kuma maganar ma ta yi ban hannun smakaho da abin da su kansu suka yi imani da shi. Na cewa a cikin daren ne ankayi jana’izar Annabi Sallallahu Alaihi Wasallama ba da rana ba wasu kuma suka ce a’a, sai da wani dare ya yi sannan aka rufe shi. Kuma bai umurci kowa da zaunawa wurin kabarinsa ba. Kuma tarihi bai fadi cewa Alin Raliyallahu Anhu ya zauna wurin ba, ko a ra’ayin kansa.

Ya ma za a yi haka ta faru, tunda an nufe Manzon ne a cikin dakin Aisha Raliyallahu Anhu kuma ba ajanabace ga alin?

Sannan kuma ai ‘yan Shi’ar sun gaya mana cewa Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama ya riga ya gaya wa Ali shi ne magadin halifarsa. Kuma lalle ne ya yi qoqarin ganin haka ta tabbata. To ya za a yi wanda ke da irin wanna aiki; kuma a ce manzon ya umurce shi da tsare kabariunsa. Ko ya yi me? Oho.

Kuma a haqiqanin gaskiya ba Ali Raliyallahu Anhu ne kawai ya yi hidmar jana’izar Manzon ba. Abin da ya tabbata shi ne, shi da Abbas da ‘ya’yan Abbas din, da barwansa Shakran ne da wasu ansaru suka yi masa wanka da saka masa likkafani. Abubakar da Umar da wasunsu kumas suna bakin kofar dakin har aka ci aka sude. Ka ga da su aka yi kenan. Cewar da ake yi suna Bani Sa’adata a lokacin qarya ce kawai.

Abin da kuma ya hana su shiga a kimtsa gawar ta Ma’aiki tare da su shi ne; kasancewar sunna ta tanadi ta kaita irin wannan hidma ga dangin mamaci. Saboda haka ne Ali Raliyallahu Anhu da makamntansa suka rabauta da wannan alheri. Da kumas aka karkare, sai aka ba musulmi dama suka shiga dakin; daya bayan daya don su yi masa salla da ganin ban kwana. Haka suka yi ta yi, maza da mata. Taron da jama’a musulmi suka yi don wannan ibada, sai ta sa dole aka jin kirta rufe gawar har zuwa ranar alhamis.

To kuma ba halifancin halifofi uku na kafin Ali Raliyallahu Anhu wanda aka yi lami lafiya, ko yakin da aka yi lokacin halifa Ali Raliyallahu Anhu ba yaki ne na neman shugabanci ba. Domin mutanen da ke bayan Sayyida Aisha da Mu’awiyah Raliyallahu Anhu a yakokan Basasar da aka yi na Jamalu da siffain da Nahrawan, ba su saxaukantar da rayukansu ne ba, don nada wani halifa ba, Ali Raliyallahu Anhu kamar yadda Mu’awiyah da Xalhatu da Zubairu babu daya cikinsu da ya ce shi ne shugaba ba Ali Raliyallahu Anhu ba. Kamar yadda kuma ba ba qarqashin jagorancion wanimutum da suke jin shi ne halattaccen shugaba, suka yi yakokin mba, kafin sasantawar da aka so yi bisa girman Allah.

Haka kuma babu daya daga cikinwaxannan yakoka na basasa, da aka yi, a kan wata ka’ida ta shugabanci da ake cece-kuce a kanta don tabbatar da sukar lamiri da rashin goyon bayan halifofi uku magabata, da shelantawa duniyar musulunci cewa ba su ne Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama ya bar wasiya a nassance da cewa su gaji shi ba. Haka kuma su dayan vangaren, ba suna yakin ne don suna jin Ali Raliyallahu Anhu bai cancanci zama halifan ba. Ko alama ba haka al’amurran suka gudana ba.

‘yar ja yayyar da ta shiga tsakanin mutane a kan wannan al’amari, kamar wadda ke tsakaninsu ce da ‘yan Shi’ah da Harijawa da mu’utazilawa da sauransu. Amma babu wani sahaboi da ya shiga ytakin;don kawai jayayyar shugabanci. Babu wanda ya kushe shugabancin Ali Raliyallahu Anhu ko ya kafirta shi, ko ya kafirta duk wanda ya jibince shi, shi da Usman Raliyallahu Anhu.

Ka ga kenan, idan ka fahimci wannan karatu da na shinfida maka, zaka fahimci cewa duk wanda ya ce farkon damtsen da aka ware, aka ba hamata iska a tsakanin musulmi wa-su-wa-su, har anka hada da kaifin takobi, ya faru ne kawai saboda kokuwar shugabanci, makaryaci ne na kinkarawa. Wanda leka kundin tarihin Sahabban kawai, ba tare da an shiga cikinsa ma sosai ba ke tabbatar da haka.

Kuma duk wanda ya kalli waxannan yake-yake da idon basira da tsoron allah, zai tabbatar da cewa yake-yake ne na Basasa, da Allah Sallallahu Alaihi Wasallama ya jarabci Sahabban da su a matsayin “fitina” kuma a kan haka ne mafi yawan malamai masu tsoron allah suka kwana. Kuma idan har ta kama sauran su yi wani sharhi a kai, ba su kan wuce cewa: Yakoka ne da suka faru tsakanin ‘yan santsi da ‘yan tabo a cikin Sahabban ba.

Ka ga a ta kai ce an yi yakokan ne bisa karvabben tawili, na garin dacewar saurara wa wanda bai gama zama shugaba ba. Amma ba don wata ka’ida ta addini ba.

Iyakar fassarar wannan lamari kenan. Kamar yadda da a ce lokacin da aka nada halifa Usmanu Raliyallahu Anhu wasu Sahabbai sun ja daga har haka ta sa ya yake su. To matsayin yakin dazai yi da su din daya da wanda Ali Raliyallahu Anhu ya yi da wadannasn. Eh! Matsayinsu daya mana, tattare kuwa da kasancewar babu wata rashin jituwa tsakaninsu a kan wata ka’ida ta addini.

Ka ji matsayin waxannan yakoka. Amma yaki na farko da aka yi a tarihin musulunci, a kan wata ka’ida ta addini shi ne wanda Harijawa suka tayar tsakaninsu da Sahabbai. Sanadiyar wasu akidu da suka qirqira waxanda suka saba wa akidar musulunci, kuma wannan yaki na daya daga manya-manyan yakoka a tarihin musulunci. Kuma da ma nassosa mutawatirai sun ambace shi kamar cewar da Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama ya yi: wasu ‘yan tawaye za su yi amfani da wata tsaga da za ta faru a garin musulmi, su yi wa musulunci tawaye. Amma vangaren da ya fi gaskiya daga cikin musulmin ne za su kashe su.

Haka kuma shi Ali Raliyallahu Anhu a karan kansa, bai yaki kowa don ya kwaci shugabanci ba. Kuma babu wanda ya yake shi don ya kwace shugabanci daga hannunsa. Kamar yadda babu daya daga cikin: Sayyida Aisha ko Xalhatu ko Zubairu ko Mu’awiyah da Sahabbansa, ko Harijawa, da ke jin shi ya fi cancanta da halifanci a kan Ali Raliyallahu Anhu Hasali ma gaba xayan al’umma na matukar ganin girmansa da zamansa mafificin daraja bayan halifa Usmanu Raliyallahu Anhu ya kaura. Haka kuma suna jin babu wani Sahabi da bai zama wajibi gare shi, ya cire wa Ali Raliyallahu Anhu hula ba,a lokacin Usman Raliyallahu Anhu babu gagarabadau a cilkin Sahabban sai shi. Wanda hakan ta sa babu wanda ya ji wani kaikayi, da aka ce shi ne halifa, balle ya yi wata jayayya, da husuma don qoqarin nuna fifikon cancantar wani a kansa. Ba a sami ko daya daga cikin irin wannan ba, balle dada zancen shaya daga. Kamar dai yadda Akayi halifancin Abubakar da Umar Raliyallahu Anhuma cikin lumana da kwanciyar hankali.

A ta kaice dai, abin da muke son tabbatar wa da wannan jeka-ka-dawo shi ne: duk wanda ke da masaniya da tarihin Sahabbai ingantacce, tabbas ya san cewa babu wani rikici da ya faru tsakaninsu a kan halifancin Abubakar da Umar da Usmnu Raliyallahu Anhu balle yaki .

Haka kuma ba a sami waxanda suka yi wata jayayya ba, don qoqarin jtabbatar da akwai wanda ya fi Ali Raliyallahu Anhu cancanta da halifanci a lokacin sa. Duk da yake akwai wasu mutane da aka tilastawa yi wa dayan halifofin huxu bai’a. Wannan dole na, kuma ba abun mamaki ba ne. Domin ko annabcin Muhammadu Sallallahu Alaihi Wasallama sai da aka tilasta wasu karvar sa, balle halifancin wani Sahabi.

Haka kuma ta tabbata cewa Sahabbai ba su yaki junansu a kan halifancin Abubakar da Umar da Usmanu Raliyallahu Anhu ba. Kai! Ko cacar baki ba su yi ba. Halifancin dai da aka zubar da jini a kasa shi ne na Ali Raliyallahu Anhu ka ga idan har zubar da jini a kan shugabanci abun kunya ne, to ba wanda hakan za ta shafa sai wanda hakan can ta faru tsakanin al’umma kan shugabancinsa.

To kuma wannan ita ce hujjar hawarijawa a kan matsayin da suka xauka na kin yaarda da al’amarin Ali Raliyallahu Anhu kuma wannan hujja tasu, ta fi ta ‘yan Shi’ah qarfi, su kuma a matsayin da suka xauka na kai Sahabi inda Allah bai kai shi ba. Haka kuma takubbansu sun fi sauka madaidaicin wuri bisa ga na ‘yan Shi’ah. Kamar yadda addininsu ya fi nasu inganci. Saboda su Harijawa ba maqaryata ba ne kamar ‘yan Shi’ah. Amma kuma duk da haka ta tabbata daga bakuna da daman gaske, daga Annabi Sallallahu Alaihi Wasallama bisa kuma ittifaqin Sahabbai cewa Harijawa batattu ne, kuma abin da suke kansa bidi’a ne. Dada Balle ‘yan Shi’ah waxanda hauka da jahilci da rashin kishin addinin su, da jaruntakarsua fagen kiren karya da rashin kuzarinsu da rashin tsentseni, kai da suffan tuwarsu da duk wasu miyagun halaye, suka tabbata.

Ko shakka babu Harijawa su ne qungiya mafi yaji, da wasu da takobi a kan wuyan mutane. Amma duk da haka ba su yaki kowa a kan halifancin Abubakar da Umar Raliyallahu Anhuma ba. Hasali ma suna daga cikin duban jama’ar da suka yarda da shugabancinsu, suks kuwa bi su.

Wannan kenan.

Sannan kuma Shaharastani ya ce: Matsala ta biyar wai ita ce ta Fadak da abin da Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama ya bari na kayan gado a duniya.

To, ita wannan mas’ala ba matsala ba ce. Domin kuwa ta tabbata cewa Annabi Sallallahu Alaihi Wasallama ya ce: “Mu Annabawa ba a gadon mu. Duk abin da muka bari duniya sadaka ne”.

To, abin da ya kamata a sani a kan wannan mas’ala shi ne; mas’ala ce ta banbancin fahimta a farfajiyar shari’a. Kuma ba ma wani savani da za a iya cewa akwai a cikinta. Don bai kai wanda ke cikin gadon ‘yan‘uwan juna tare da kaka namiji ba. Ko na kaka mace tare da danta ba. Ko kuma wanda ke cikin shamakance Uwa da ‘yan‘uwa biyu ke yi. Ko xaukar matsayin kaka namiji da Uwa kamar na Uba. Da kuma wasu mas’aloli na gado, masu kama da waxannan, da malamai suka sami banbancin fahimta a kai.

Sannan kuma ita ma mas’alar Fadak, mas’ala ce ga-ta-sarai. Domin kuwa ai Ali Raliyallahu Anhu ya zama halifa bayan haka nan, Fadak da sauran garuruwan musulunci duk suka koma qarqashin ikonsa. Amma bai damqa ta hannun ‘ya’yan Fatima ba, a matsayin wani abu da ‘yan Shi’ah ke iqirarin wai Abubakar Raliyallahu Anhu ya ba mahaifiyarsu. Haka kuma bai karvo wani abu da aka bai wa matan Annabi Sallallahu Alaihi Wasallama da ‘ya’yan Abbas ba, da sunan gado.

Ka ga ke hakan na nuna cewa shi kansa alin Raliyallahu Anhu bai tare da ‘yan Shi’ah a cikin wannan zargi da suke yi wa halifofin. Domin da yana jin cewa abin da suka aikata da abin da Manzon ya bari zalunci ne, lalle da ya walwale shi. Domin kuwa yana da ikon yin haka. Kuma hakan ma shi ne abu mafi sauki gare shi, bisa ga fuskantar Mu’awiyah da rudunarsa da sunan yaki. Ko shakka babu Alin Raliyallahu Anhu ba zai yaki Mu’awiyahn ba, tattare da irin sharrin da hakan za ta haifar. Kuma a lokaci xaya ya kasa qwato wa magadan Annabi wannan xan abin duniya ba. Abin da yake iya yi cikin qyaftawa da bisimillah.

Bayan wannan kuma sai malamin ya ce wai kuma matsala ta shida ita ce: Yaqar waxanda suka hana zakka da halifa abubakar ya yi. Wannan ma ya vata wa al’ummar Muhammadu Sallallahu Alaihi Wasallama suna. Wai ma saboda tsinkayo haka ne da halifa Umar Raliyallahu Anhu ya hau gado ya dage kai da fata ya mayar ma su da waxanda aka kamo daga cikinsu a lokacin yaqin. Ya kuma saki gaba xayan waxanda aka xaure a dalilin haka.

Ka ji abin da Shahrastani ya ce, kuma xan Shi’ar ya riwaito.

To duk wanda ya san tarihin musulunci ya san wannan magana shegiyar qarya ce. Domin kuwa halifa Abubakr Raliyallahu Anhu bai yaki waxannan mutane ba, sai da Umar Raliyallahu Anhu ya yarda da shi, bayan sun kara wa juna ilimi a kan mas’ala. Kamar yadda Buhari da Muslimu suka riwaito daga Abu Hurairata cewa:

Umar ya ce Abubakar Raliyallahu Anhu: ya kai halifan Manzon Allah! Ya zaka yaki waxannan mutane, alhali Annabi Sallallahu Alaihi Wasallama ya ce: An umarce ni da in yaki mutane, matukar ba su yi imani da babu abin bauta wa da gaskiya sai Allah ba, kuma ni Manzon ne. Amma idan suka furta wannan kalima jinai nai da dukiyoyinsu sun haramta gare ni. Sai fa a kan wani hakki na shari’ah. Hisabinsu kuma na wurin Allah?

Sai Abubakar Raliyallahu Anhu ya ce masa: Ah! To ai cewa ya yi: sai fa a kan wani hakki na shari’ah ko? Ti ai zakka hakki ne na shari’ah. Tunda kuwa haka ne. Wallahi da za suki ba ni ko da ragwamar Raqumi da sukan ba Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama zan yake su a kan haka.

Daga nan sai Umar Raliyallahu Anhu ya ce: wallahi, daga nan ne na fahimci Allah ya gama haskaka qirjin Abubakar a kan wannan yaqi. Na kuma sakan - kance da cewa lalle bisa hanya yake.

Ka ga kenan wannan hadisi ya tabbatar mana da cewa Umar Raliyallahu Anhu yayi itifaqi da halifa Abubakar Raliyallahu Anhu a kan wannan yaqi. Haka kuma sauran Sahabbai ma sun yarda da shi a kai. Kuma yaqin yayi amfani matuqa . saboda mutanen sun dawo sun yarda da kasancewar ci gaba da fitar da zakkar wajibi a kansu. Bayan can dauri sun fandare. Sannan kuma a ingantaccen tarihin yadda yaqin ya kasance, ba a kama kowa daga cikinsu aka ribace ba. Ba a kuma xaure kowa daga cikinsu ba. Kai hasalima babu wanda aka tava xaurewa a zamanin Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama kona Abubakar Raliyallahu Anhu a Madina. Balle har a ce halifan ya mutu ya bar ‘yan fursuna. Qarya ne.

Daga nan kuma sai shahashtanin ya ce wai, matsala ta bakwai itace: zaven Umar Raliyallahu Anhu da halifa Abubakar Raliyallahu Anhu yayi a matsayin wanda zai zama halifa bayansa. Wai har wasu mutane suka qorafa cewa: Abubakar ka naxa mana mutum mai kaushi hali da hushi!


Martani:

Harwayau dai, wannan mas’ala ba ta isa a kira ta mas’ala ba domin kuwa ba ga Umar Raliyallahu Anhu aka fara ba. Wasu Sahabbai sunyi irin wannan qorafi a kan Annabi Sallallahu Alaihi Wasallama a kan ya shugabantar da Zaidu xan Harisata da xansa Usamatu a kansu, a wasu lokutta. Kuma wasu mutane da yawa sun yi qorafi da suka a kan wasu da halifa Abubakar da Umar Raliyallahu Anhuma suka ba riqon wasu kasashen musulmi.

To kuma shi wannan qorafi, da waccan magana da malamin ya ce an faxa a kan Umar Raliyallahu Anhu ai ba kowa ne ya yi ba banda Xalhatu. Shi ma daga baya yayi nadama. Har ma aka wayi gari yana cikin sahun mutanen da ke matuqar girmama halifa Umar xin Raliyallahu Anhu kamar yadda masu qorafin can a kan jagorancin Zaidu da Usamata suka yi nadama a kai, kuma suka gyara saboda girman Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama.

Bayan wannan kuma sai malamin ya ce, wai kuma matsala ta takwas ita ce kafa kwamitin da halifa Umar Raliyallahu Anhu yayi, don ya zavi halifa bayansa. Wanda wai kuma a qarshe bayan an yamutsa gashin baki, manbobin suka haxu a kan Usmanu Raliyallahu Anhu a matsayin halifa.


Yüklə 2,75 Mb.

Dostları ilə paylaş:
1   ...   23   24   25   26   27   28   29   30   ...   51




Verilənlər bazası müəlliflik hüququ ilə müdafiə olunur ©muhaz.org 2024
rəhbərliyinə müraciət

gir | qeydiyyatdan keç
    Ana səhifə


yükləyin