Tafarkin sunnah



Yüklə 2,75 Mb.
səhifə28/51
tarix28.10.2017
ölçüsü2,75 Mb.
#17506
1   ...   24   25   26   27   28   29   30   31   ...   51

Martani:

Wannan magana na xaya daga cikin maganganun da malamai masana sirrin riwaya, suka haxu a kan kasancewarsu qarya tuburan. Domin kuwa babu wanda ya nemi tayar da hankali a kan halifancin Usmanu Raliyallahu Anhu saboda wai bai yarda ba. Illa dai Abdurrahamanu xan Aufu ya xauki tsawon kwana ukku yana tattaunawa da mutane. Inda yabi har matan Sahabbai a gidajensu, yana neman shawarar su. A qarshe aka tabbatar masa da cewa an gamu da Usman ya zama halifa Raliyallahu Anhu. To kuma ko da akwai wanda ke qyamar halifan a zuciyarsa, ba a samu wanda ya riwaito hakan ba. Kai! Hasali ma dai babu abin da aka faxa a kan wannan al’amari, da ya kawo kunnenmu.

Amma kuma duk da haka, ba mu cewa wani bai yi wani qorafi ba, koda a zuci. Tunda irin wannan al’amari na neman shawara wurin jama’a ya gadi haka.

Sannan kuma malamin ya ce wai ko bayan waxannan matsaloli. Wasu matsalolin sun faru da dama. Waxanda suka haxa da: Mayar da Hakamu xan Umayyata da halifa Usmanu Raliyallahu Anhu ya yi a Madina, bayan Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama ya kore shi. Wanda har mutane ke yi masa laqabi da “Zakkar Manzo”. Kuma wai halifan ya yi haka ne, tattare da neman halifa Abubakar da Umar Raliyallahu Anhuma da ya yi, a lokacin halifacin da su yi wa Hakamu xin afuwa. Amma abun ya faskara. Kuma ma wai halifa Umar Raliyallahu Anhu bai tusaya ga qin yi masa Afuwa ba. Har qarawa yayi da shi gaba, daga inda yake zaune a Yamen, da tsawon zango arba’in.

To abin da za mu ce a nan shi ne: Wannan mas’ala ba ta isa a kira ta savani ba. Abin da har za’a xauka a kai shi da nisa. Balle a ambace ta matsala. Idan kuwa har aka yi haka. To kenan, duk wani hukunci da wani halifa ya yanke, wasu Sahabbai suka saba da shi a fahimtar abun ya zama “matsala” kenan ko?

To dama irin wannan, har gwamma a ambaci banbance-banbancen fahimtar da aka samu tsakanin Sahabban, a kan wasu mas’alolin gado da saki da wasu mas’aloli irinsu. Waxanda suka fi inganci a riwaya, da amfani ga mutane. Eh! Waxannan mas’aloli da ire - irensu su ne mafi inganci mana, da tabbata. Saboda ma’abuta ilimi sun riwaito su. Wanda kuma har yau mutane na bitar su, tare da amfanuwa da taskokin da ke cikinsu na ilimi, a matsayinsu na duwatsun murhun shari’a, da ake iya qara wa juna ilimi a cikinsu.

Savanin irin waxannan qananan abubuwa, daba su isa a kalli banbance - banbancen fahimta a cikinsu, a matsayin wani abu daya cancanci tautaunawa don qara wa juna ilimi ba.

Amma fa duk wannan sharhi da muke yi muna yin sa ne, tattare da yaqinin da muke da shi a kan cewa duk waxannan abubuwa da ya faxa game da Hakam, qorarsa, laqabinsa, nemar masa afuwa, qiyawa da qarawa dashi gaba, duk qarya ce.

Idan kuwa xan Shi’ar ko shi shahrastanin naji zancen gaskiya ne, to su gaya mana asalin wanda ya riwaito shi, da isnadinsa, da lokacin da ya tafi yeman xin, da dalilin da ya sa aka iza qeyarsa can. Alhali Annabi Sallallahu Alaihi Wasallama ya yi masa mazauni a Xa’ifa, kamar yadda suke cewa. Gashi kuma ya tafi Yemen xin zama kusa ga Makka da Madina.

Eh mana! A gaya mana dalilin da zai sa a matsa dashi can bayan Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama ya aje shi kusa dashi. A gaya mana.

To kuma duk aje wannan. Ma’abuta ilimi sun tabbatar cewa, wannan magana da ‘yan Shi’ah ke yayatawa, ta cewa Annabi Sallallahu Alaihi Wasallama ne ya kore Hakamu zuwa Xa’ifa ba gaskiya ba ne, shi ne ya tafi a son ransa. Sannan kuma wani abu da zai tabbatar ma ka da cewa maganar tatsuniya ce. Shi ne kasawar waxanda suka ce Manzon ya yi masa korar, daga ambaton wani isnadi ingantacce, a kan yadda al’amarin ya faru dalla-dalla.

Sannan kuma malamin ya ce, wai daga cikin matsalolin, akwai korar da halifa Usmanu Raliyallahu Anhu ya yi wa Abu Zarri zuwa Rabaza. Da aurar wa Marwanu xan Hakamu ‘yarsa da ya yi. Tare da dunqule wasu ganimomi biyar da aka samo daga Afrika, ya danqa masa. Waxanda qimarsu ta kai dinari dubu xari biyu.


Martani:

Ita maganar Abu Zarri da barin garin Madina da ya yi, mun riga mun yi bayani a kanta dalla-dalla a baya kaxan.

Wannan kenan. Sannan kuma me ya haxa aurarwa Marwanu da ‘yarsa da al’amarin musulmi, balle ace hakan ta haifar da wata matsala a tsakaninsu? Sannan zancen ganima biyar ta Afrika da yaba shi, daga ina aka samo ta? Abin da suke faxa can farko shi ne halifan yaba shi dinari dubu biyu. Ka ga an sami savani nan take. To kuma ko a haka, ai kowa ya san waccan ganima ba ta kai wannan qima ba.

Bayan wannan kuma sai ya ce: Kuma daga cikin matsalolin akwai bayar da mafaka da halifa ya yi ga Abdullahi xan Sa’adu bayan Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama ya halarta zubar da jininsa. Wai ma kuma halifan ya naxa shi gwamnan Masar bayan haka.


Martani:

Idan xan Shi’ar na nufin har zuwa lokacin da halifa Usmanu Raliyallahu Anhu ya tura Abdullahi xan Sa’ad xin Masar a matsayin gwamnansa, jinin nasa na nan halattace. Kamar yadda maganar tasa ke nunawa, to qarya yake yi. Kuma hakan ta qara tabbatar da kasancewarsa jahilin tarihin Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama. Domin kuwa gaba xayan mutane; soja da farar hula a fagen sani sun yi ittifaqi, a kan cewa, an karvi tubar Abdullahi xan Sa’ad. Suka ce bayan da Annabi Sallallahu Alaihi Wasallama ya shelanta halartar zubar da jinin waxansu mutane da dama, a ranar da aka ci garin Makka da yaqi. Kuma a cikin mutanen nan har da Abdullahin nan. Bayan xan lokaci sai Usman Raliyallahu Anhu ya taho dashi wurin Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama ya roqar masa afuwa. Shi kuma yayi mubaya’a. A qarshe kuma ya kulle amana da musulmi; ta a faxi a tashi tare. Daga nan sai jininsa ya koma haramtacce.

Sannan kuma malamin ya ci gaba da cewa: Kuma halifa Usmanu ya naxa kwamandan Askarawansa, Mu’awiyah xan Abu Sufyanu gwamnan Sham. Ya kuma kai Sa’ad xan Abu waqqasi Kufa. Ya kuma maye gurbinsa da Abdullahi xan Amru daga baya. Ya kuma tura Walidu xan Uqubata Busrah.

To abin da za mu tabbata wa xan Shi’ar a nan shi ne, halifa Umar xan Khaxxabi ne farkon wanda ya naxa Mu’awiyah gwamnan Sham bayan rasuwar xan’uwansa Yazidu xan Abu Sufyanu, wanda ke gwamna a can. Iyakar abin da halifa Usmanu Raliyallahu Anhu ya yi shi ne tabbatar ma sa da ci gaba da riqon Sham xin tare da haxe masa baki xayan sassanta. Kuma Mu’awiyah ya zauna da mutanen wurin zama na madalla; tarihin zamansa dasu cike yake da abubuwa masu faranta rai. Wanda hakan ta sa talakawan nasa ke matuqar girmama shi, da qaunar shi.

Ka ga ashe Mu’awiyah ya sami babban rabo musamman idan aka yi la’akari da abin da ya tabbata a cikin Buhari, a ingantaccen hadisin da aka samo daga Annabi Sallallahu Alaihi Wasallama wanda ya ce: Zavavvu daga cikin shugabaninku sune waxanda kuke so, suke kuma son ku. Kuke kuma yi masu fatar alheri, suma suke yi maku.

Kuma tabbas tarihi ya tabbatar da cewa talakawan Mu’awiyah Raliyallahu Anhu suna matuqar sonsa tare da yi masa addu’a da fatar alheri. Haka shima, son da yake masu ne yasa ya riqa su da aminci, har ma yake masu fatar dauwama cikinsa ko bayansa.

Shi kuma zancen abin da ya faru tsakanin Sa’id xan Asi, wanda halifa Usman Raliyallahu Anhu ya naxa gwamnan Kufa, da talakawan nasa, abu ne sababbe. Mun riga mun faxa maku cewa su miyagun mutane ne asalatan. Babu gwamnnan daya tsira daga qorafe - qorafensu. Sa’ad xan Abu Wakkas, da Abu Musa al-Ash’ari da Ammaru xan yasir da Mugirata xan Shu’ubata duk sun zauna da mutanen Kufa, a matsayin gwamnoninsu. Amma babu wanda ya kwashe lafiya dasu. Sun shahara da irin wannan matsala. Illa dai abin nasu yafi qamari a lokacin halifa Usmanu Raliyallahu Anhu amma kuma ko Ali Raliyallahu Anhu bai tsira daga sharrin suba. A matsayinsa na wanda shima yaba makusantansa muqamai kamar yadda Usman Raliyallahu Anhu yayi.

Xan Shi’ar ya ci gaba da cewa: kuma shahrastani ya ce: matsala ta tara kuma ita ce wadda ta faru a zamanin Sarkin Musulmi Ali Raliyallahu Anhu wadda ta haxa da: Tashin da Xalhatu da Zubairu suka yi zuwa Makka, bayan an zaxi Ali Raliyallahu Anhu a matsayin halifa har kuma an yimasa bai’a, da kuma xaukar sayyida Aisha Raliyallahu Anhu da suka yi kan Raqumi zuwa Busra. Da kuma dagar da suka shiga da halifan. Wadda aka sani da suna “Yaqin Basasar Raqumi”. Da kuma savanin da ya shiga tsakaninsa da Mu’awiyah Raliyallahu Anhu wanda a qarshe ya haifar da “Yaqin basasar Siffin”. Da kuma warewar da Amiru xan Asi ya yi wa Abu Musa al-Ash’ari.

Sai kuma savani daya faru tsakanin halifan da la’anannin Marikawan nan a Nahrawan.

Amma dai a taqaice, duk waxannan abubuwa da suka faru, Ali Raliyallahu Anhu shi ne mai gaskiya. Sai gashi kuma mutane irin su: Ash’as xan Kaisa da Mus’ir da Fadqi at-Tamini da Zaidu xan Huswain ad-da’i da wasunsu dake tare dashi, sun yi masa tawaye da sunan Harijawa. Bayansu kuma, duk a zamanin nasa aka sami “Gulatu” irin su Abdullahi xan Saba’i. Waxannan qungiyoyi biyu sune mafarkacin kowace irin fitina da varna. Kuma a haka sa maganar da Annabi Sallallahu Alaihi Wasallama yayi a kansa ta tabbata. Inda ya ce: mutum biyu za su halaka a kanka; wanda ya wuce wuri a cikin sonka da wanda ya zurfafa a cikin qinka.

Xan Shi’ar ya kammala wannan magana da cewa: don Allah ka dubi maganar wannan mutum (Shaharastani) da idon basira. Za ka fahimci cewa waxannan tsoffin bariki (halifofi uku kafin Ali Raliyallahu Anhum) su ne ummul-haba’asin duk wata fitina da ta faru a tarihin musulunci. Kar ka daxa kar ka qara.
Martani:

Eh; to. Wannan ra’ayinka ne. Amma a qashin gaskiya, duk wanda ya dubi wannan magana ta Shahrastani da idon adalci. Zai fahimci cewa marubucin ya shirya littafin ne kawai don ya tallata Shi’ah. Kamar yadda muka riga muka vulguta maku tun farko. Ah! To idan ba haka ba. Ai ya ambaci Abubakar da Umar da Usmanu Raliyallahu Anhu fiye da sau shurin masaki. Amma baice “suke da gaskiya ba”. Amma nan take, daya kawo kan Ali Raliyallahu Anhu sai ya yanke hukuncin cewa shi ne mai gaskiya. Kamar dai an naxa shi Alqalin alqalai.

Ka kuwa san ga al’ada, idan ba wata manufa kega marubuci ba, a matsayinsa kuma na mai bayar da labari, to baya wuce faxin abin da kowa yayi, da abin da aka yi masa. Amma duk wanda kaji ya kutsa wannan duhun daji, daga cikin musulmi. A qarshe kuma ya buye ga cewa: Gaskiya na tare da Ali, yana kuma tare da ita Raliyallahu Anhu su kuwa Abubakar da Umar da Usmanu Raliyallahu Anhu to!---. Ka tabbata xan Shi’ah ne.

Kuma wani abin da ke tabbatar maka da cewa wannan magana qarya ce shi ne, cewar da Shahrastanin ya yi wai: Sai da aka daddale magana a kan zaven Ali Raliyallahu Anhu har aka yi masa bai’a. Sannan qura ta muske. Alhali kuma a haqiqanin gaskiya mafi yawan musulmi, har daga cikin mutanen Makka, ba su yi masa mubaya’a ba. Fita batun waxanda ke nesa. Irin mutanen Sham da Masar da Magrib da Iraqi da Khuransa.

Irin wannan magana ta haxuwar kan jama’a gaba xaya, bata faxuwa a kan Ali Raliyallahu Anhu kamar yadda take faxuwa a kan halifa Usmanu Raliyallahu Anhu wanda ba a sami mutum xaya daya qi goyon bayansa ba.

Wani abun kuma dake tabbatar da rashin gaskiyar Shahrastani a cikin wannan magana shi ne, sukar lamirin daya yi wa xalhatu da Zubairu da Aisha Raliyallahu Anhu ta hanyar wanka da kamar jirwaye. Ba tare da ya fito da al’amarin fili yadda ya faru ba. Alhali kuwa ma’abuta ilimi na qwarai, sun kwana da sanin cewa Xalhatu da Zubairu basu fita da nufin su yaqi Ali ba Raliyallahu Anhu Abin ya zamar masu dole ne, a matsayin kariyar kai. Haka suma mutanen Sham basu fita da niyar yaqar saba. Allah kawai ya qaddara haka ta faru. Shi Alin Raliyallahu Anhu ba nufinsa ne ya yi yaqi da waxancan ko waxannan ba. Qaddara ce kawai ta riga fata.

Malaman da suka naqalci zahiri da baxinin tarihin musulunci, sun bayyana cewa yaqin Raqumi ba yaqi ne ba. Rikici ne kawai na cikin gida. Koka ce masa “Yaqin Basasa” kamar yadda muka ambace shi a farko.

Dalili kuwa inji malaman shi ne; gaba xayan vangaroran biyu sun haxu ne, domin daddale yarjejeniyar da suka yi. Da shata yadda za a yi a kama makasa halifa Usmanu a hukunta su. Don a sami zaman lafiya; kowa yabar jin qaiqayi a ransa. A cikin wannan dufulomasiyya, sai makasan nasa, dake cakuxe cikin musulmi, suka tabbata cewa, idan suka yarda aka zartar da wannan yarjejeniya, lalle kashin su ya bushe. Saboda haka bari su sake tayar da wata fitina kamar yadda suka tayar da ita farko.

Sai nan take, suka kai farmaki kan Xalhatu da Zubairu da mutanensu. Su kuma suka yo kukan kura don su kare kansu. Sai makasan suka yi tururuwa, daga cikin jama’ar Ali Raliyallahu Anhu da cewa ga su Xalhatu nan za su far ma su. Nan take sai kuma Ali Raliyallahu Anhu ya sa qaimi, mutanensa, har da su makasan, suka rufa masa baya, a matsayin su ma masu kariyar kai, aka yi karon battar qarfe.

Subhanallahi. Allah ka kiyashe mu da halin munafukai.

Iyakar guri da niyyar kowane vangare kenan; kariyar kai. Amma ba yaqi ba.

To tunda ko har haka ne. Ka ga al’amarin sai hamdala da hauqala. Kuma kame baki daga gareshi shi yafi. Tunda Alqur’ani da Sunnah sun bayyana cewa, su zavavvu ne a wurin Allah, na kirki ne, ‘yan aljanna.


2.60 ‘Yan Shi’ah na Taimakon Kafirai a Kan Musulmi

Bari mu fara da inda xan Shi’ar ke cewa: “Ka dubi maganar wannan mutum da idon basira da adalci. Za ka tabbatar cewa waxannan tsoffin bariki, yana nufin halifofi uku na farko, su ne ummul haba’isin wannan fitina”.



Martani:

Zancen fitina a cikin musulunci, ko na-goye ya kwana da sanin cewa, ‘yan Shi’ah ne mafarinta. Babu wata fitina ko wani sharri da ya faru ga wannan al’umma, face ka taras da cewa su ne kanwa uwar gami a ciki. Domin kuwa ai wutar fitinar farko da ta kama a tarihin musulunci, su ne suka hasa ta, don su ne suka kashe halifa Usmanu Raliyallahu Anhu.

Imamu Ahmad ya riwaito daga Annabi Sallallahu Alaihi Wasallama cewa: “Fitinu uku, duk wanda ya tsira daga cikinsu to, shi ne tserarre. Mutuwata, da kisan wani halifa a kan zalunci, da kuma Dujjal”.

Wannan kenan. Wani abu kuma dake tabbatar da kasancewar maganar wannan xan Shi’ah qarya shi ne, duk wanda ya bibiyi diddigin tarihin qungiyoyi a duniya, zai tabbatar cewa, Sahabban Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama mutane ne da Allah Subhanahu WaTa’ala ya shaida a cikin Alqur’ani da kasancewa mafiya alheri daga cikin halitta, kamar inda yake cewa:

ﭽ ﭞ ﭟ ﭠ ﭡ ﭢ ﭣ ﭤ ﭥ ﭦ ﭧ ﭨ ﭩﭪ ﭫ ﭬ ﭭ ﭮ ﭯ ﭰ ﭱﭲ ﭳ ﭴ ﭵ ﭶ ﭷ ﭼ آل عمران: ١١٠

Kun kasance mafi alherin al’umma, wadda aka fitar ma mutane; Kuna umurni da Alheri, kuma kuna hani daga abin da ake qi, kuma kuna imani da Allah (3:10).

Su ne mutanen da suka fi kowa son zaman lafiya. Domin kuwa ba a tava samun jama’a wadda kanta ya haxu a kan shiriya, da faxaka da nisantar fitina da savani da rarrabuwar kai, a tarihin duniya kamar su ba.

Haka kuma kundin tarihin ya tabbatar da cewa ‘yan Shi’ah sun fi kowa nisa daga shiryayyar qungiya wadda Allah ke taimako.1 Hakan kuwa ta faru ne a sakamakon kasancewarsu mafiya jahilci da zalunci daga cikin qungiyoyin shexan, waxanda ke iqirarin kasancewa cikin musulmi masu mayar da gaba gabas su yi sallah.

Haka kuma ya tabbata cewa, zavavvun wannan al’umma su ne waxancan Sahabbai. Sun kuwa samu wannan sheda da matsayi a sakamakon kasancenwarsu shafe zane a fagen zama tsintsiya maxaurinki daya, a cikin shiriya da addinin gaskiya. Tare da yin matukar nesa-nesa daga xai-xaicewa da zaman 'yan marina. Duk kuwa wani abu na tasgaro da kasawa, da wani zai ce ya faru daga waxannan mutane, ba zai wuce ajizanci irin na xan Adamu ba. Kuma da za a kwatanta shi da wanda ya faru daga wasunsu, za a taras da bai taka kara ya karya ba.

Fita batun duk wani abu da mutum zai qaddara a cikin zuciyarsa, ya kuma nace a kan kasancewarsa, alhali Allah Subhanahu WaTa’ala bai halicci mai irin wannan abu a cikin qanana da matsa kaita da manyan bayinsa ba. Kamar abin da waxansu ke cewa, wai lallai ne shugaba ya kasance ma'asumi. Wasu kuma su ce, a’a, ko dai bai kai ma'asumi ba, ya kasance xan qwarya-qwarya. Kai wasu ma za ka taras suna jin cewa, ya kamata duk yadda malami ko shehi ko shugaba ko sarki ya qasura, tattare da yawan iliminsa da kishin addininsa da yawan ayyukansa. Duk da haka su a wurinsu lalle ne ya kasance ya san komai, ta yadda ba ya kure a cikin kowace irin mas’ala. Ya kuma fita daga layin mutane, ta yadda babu abin da zai vata masa rai balle ya yi fushi. Kai da yawa daga cikin irin waxannan mutane ma ke gurin shugaba ya siffanta da wata sifa da ko Annabawa albarka.

Ka ga wannan ya sava wa hankali. Domin kuwa ai Allah Subhanahu WaTa’ala umurtar Annabi Nuhu da Muhammadu Alaihimus Salamu Ya yi da su ce:

ﭽ ﭶ ﭷ ﭸ ﭹ ﭺ ﭻ ﭼ ﭽ ﭾ ﭿ ﮀ ﮁ ﮂ ﭼ هود: ٣١

Kuma ba ni ce muku a wurina taskokin Allah suke, kuma ba ina sanin gaibi ba ne. Kuma ba ina cewa ni mala’ika ne ba. (11:31).

Amma kuma tattare da wannan magana, sai ka taras da jahilai daga cikin mabiya na gurin shugabansu ya kasance masanin duk abin da za’a tambaye shi, mai iko a kan duk abin da za’a nemi ya yi. Ya kuma wadatu daga duk wasu buqatu irin na ‘yan Adamu; wato ya dai zama kamar mala’ika. Irin wannan guri da fata da wasu mabiya ke yi wa shugabanninsu, daidai yake da fatar da Harijawa ke yi wa al’umma baki xaya, wato kada wani ya aikata wani zunubi daga cikinsu. Wanda kuwa duk ya aikata, to a wurinsu ya kafirta kuma xan wuta ne har abada.

Da wannan matsayi na Harijawa da wancan na ‘yan Shi’ah da wasunsu daga cikin qungiyon bidi'a, duk vata ne. Allah Subhanahu WaTa’ala bai halacci irin waxannan mutane ba, balle ya shari’anta irin waxannan siffofi.

Harwayau kuma dai, muna qara nanatawa. ‘Yan Shi’ah su ne matattarar vata da danbarwa, fiye da kowace qungiya daga cikin qungiyoyin da ke jingina kansu ga wannan al’umma. Kamar yadda su kuma ma'abuta hadisi da tantagaryar Sunnah, su ne matattarar shiriya da sawaba da rahama fiye da kowace qungiya daga cikin qungiyoyin wannan al'umma. Wanda hakan ta sa duk motsin da za su yi, lalle ne ya kasance taimako ga sunnar Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama don ba su da kowa sai shi. Shi ne shugaba a garesu na qarshe. Ba su sauraren maganar kowa, sai idan ta yi muwafaqa da tashi. Kuma fatarsu kodayaushe ita ce taimakon addinin Allah da sunnar Manzo.

To, ka ga a hankalce, idan Sahabbai da ma’abuta hadisi da tantagaryar sunnah, sun kevanta da kasancewa ma’abuta shiriya da addinin gaskiya, mafiya nisantar qungiyoyi daga shiriya su ne masu zagin su.

A haka kenan, ta bayyana ga dukkan mai hankali cewa, maganar wannan xan Shi’ah shirme ne kawai irin wadda babu mai kafa hujja da shi sai jahili. Haka kuma ta bayyana cewa marubucin, son rai ne yake bi, illa iyaka. Ga shi kuma bai san kome ba a cikin fannin riwaya. Matsayinsa bai wuce na masu bada qissoshi a cikin masallaci ba.

Su dai ‘yan Shi’ah an sani cewa, munafukai ne da suka shigo musulunci da nufin gurvata shi. Saboda haka suka qirqira qarairayi, suka haifar da miyagun ra’ayoyi don cimma wannan manufa tasu, ta qasqanta duk wanda ke kan tafarki madaidaici. Saboda haka suka fara da kashe halifa Usmanu, wanda shi ne xaya mafarin qirgar fitina. Bayan haka sai suka koma suka kewaye Ali Raliyallahu Anhu da sunan so da qauna gare shi da 'yan gidan Manzon Allah, alhali kuwa manufarsu ita ce girka sanwar fitina a tsakanin musulmi.

Wannan dalili ya sa za ka taras da 'yan Shi’ah kodayaushe suna goyon bayan kafirai da waxanda suka yi ridda. Kamar yadda suka goyi bayan Banu Hanifata mabiyan Musailamatul-Kazzabi, suka ce wai musulmi sun zalunce su, a qarqashin shugabancin Abubakar Raliyallahu Anhu kamar yadda marubucin ya ce. Haka kuma za ka same su suna goyon baya da jin-jina wa kasurgumin kafirin nan Abu lu’uluatal Majusi wanda ya kashe sayyidina Umar.

Bari kaji yadda abin ya kasance: An riwaito cewa, Abu lu’uluata ya nemi halifa Umar ne da ya sa baki tsakaninsa da masu karvar haraji, don a sassafta ma shi. Halifa Umar ya yi niyyar sa bakin, amma kafin haka sai qiyayyar da ke kimshe cikin zuciyar Bamajushen zuwa ga musulunci da musulmi ta yunquro masa. Sai kawai ya kashe halifa Umar, saboda ya xaukar wa kafirai fansar fatattakar da Umar xin ya yi masu lokacin da ya ci qasashensu, inda ya karkashe shugabanninsu ya kuma rarrabe dukiyoyinsu a tsakanin musulmi.

Ka ji aika-aikar da Abu Lu’ulu’ata ya yi. To, don Allah kai kana ganin akwai wanda zai kalli irin wannan bawa da gashi a ka, balle har ya koxa shi, in ba mafi girman kafirce wa Allah da Manzo daga cikin mutane, da qiyayya da musulunci, da kai matuqa ga jahiltar al’amurransa ba?.

To, mu fita batun ma wannan, da duk wani abu da a ke ji ko ake karantawa wanda ya faru tsawon shekaru, duk mai hankali da ya dubi abin da ke faruwa yau a zamaninsa, da wanda ya faru jiya kaxan na fitinu da sharri da varnace-varnace a cikin musulunci, zai taras da cewa ‘yan Shi’ah ne suka haddasa mafi yawansa. Zai kuma tarar da cewa aikinsu kenan: duk abin da zai jefa wannan al’umma cikin wutar fitina da sharri da varna, to suna lale marhabin da shi.

Mu mun sheda, mun kuma ji ta lafiyayyun hanyoyi, abin da ya faru a wannan zamani namu. Mun ga irin yadda Jankizkhan sarkin kafiran Turkawa ya danno, da irin mugun abin da ya faru ga musulunci, na mamayewar da kafirai mushrikai suka yi wa qasashen musulmi. Suka taka dangin Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama Hashimawa da Banul Abbas yadda suke so. Suka kashe na kashewa, suka raunata na raunatawa. Suna da ribaci mata muminai suka halatta farjojansu. Qananan yara kuwa suka shigar da su cikin addininsu, tare bautar da su.

Wannan duk ban da karkashe malamai da suka yi da fitattun makarantan Alqur’ani da wargaza masallatai. Daga sai suka samu damar xaukaka darajar gidajen gumaka waxanda suke yi wa laqabi da Al-Bazkhanat, da wuraren ibadar Yahudawa da ‘yan mishan. Kai da waxansu abubuwan da dama, waxanda ba su da daxin faxi.

Kuma duk mai hankali ba ya shakkun cewa da Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama zai dawo duniya, ya ga wannan illa da ta faru ga al’ummarsa lalle zai yi baqin ciki fiye da wanda zai yi, a kan musulmi biyu da suka shaya daga tsakaninsu saboda tabbatar da mulki na gari. Dalili kuwa shi ne su waxannan yaqe-yaqe na basasa, babu wani vangare daga ciki da aka ribace matansa, ko aka keta alfarmarsa. Kuma ba su qari wani kafiri da komai ba. Kamar kuma yadda ba su rosa wasu shari’o’i mutawatirai, bayyanannu na musulunci ba.

Ka dubi girman wannan al’amari. Ya kuma faru bisa ga gayyata da tallafi na musamman daga ‘yan Shi’ah. Haka kuma mutane sun sheda a lokacin da Holaku Sarkin kafiran Turkawa ya shiga qasar Sham a shekara ta 658H. ‘Yan Shi’ah da ke cikin Sham a birane da qauyuka, waxanda suka haxa da mutanen Halab da maqwabtanta da na Dimashqu da kewayenta, su ne suka zama manya-manyan dakarun da waxannan kafirai suka yi amfani da su ga tabbatar da mulkinsu, bayan sun roshe na musulmi.

Haka abin ya kasance a lokacin da Holakon ya isa qasar Iraqi, ya kashe halifa da musulmin da Allah ne kaxai ya san adadinsu. Babba da yaro, kowa ya san cewa a wannan lokaci, wazirin halifan ne, wato Ibnul-Al-qami xan Shi’ah da mutanensa suka mara wa wannan kafiri baya, suka taimake shi ta hanyoyi daban-daban, na voye da na bayyane. Waxanda faxarsu ba za ta yiwu ba, ko wani sarki ya ci ya fita.

Haka kuma an tabbatar mana da cewa, ‘yan Shi’an sun ci gaba da kasancewa tare da Jankizkhan, don musulmi na ganin su tare kodayaushe, a cikin sasannin Sham da sauran garuruwa.

Kai! Babu wani lokaci da musulmi za su shaya daga da Nasara, face ‘yan Shi’ah sun yi qawance da Nasaran, tare da ba su kowace irin gudunmuwa gwargwadon ikonsu. Suna baqin ciki da qyamar su ji an ci wani gari na Nasara da yaqi. Kamar yadda suka qyamaci cin garin Akka da ire-irensa. Kai kama hannun Nasaran ma suke yi suna nuna masu inda musulmi suke. Akwai ma wani lokaci da aka yi qanfar rudunar musulmi a Sham, a shekara ta 599H. Ganin haka sai ‘yan Shi’ah suka bazu a cikin garuruwa suna ta varna da masha'a ta hanyar kashe Ahlus-Sunnah da qwace dukiyarsu. Tare da kaxa tutar da ke xauke da hoton kuros a sama, da kururuta fifikon Nasara a kan musulmi. Qarshe ma har ribace musulmi da dukiyoyinsu da makamansu suka xora yi suna kai wa Nasara abokan gaba, a Qubrus da wasu garuruwa.

Mutane da yawa sun shedi waxannan abubuwan da makamantansu. Wanda kuwa bai ganar wa idonsa ba, ya ji ta hanyoyi mutawatirai. Wallahi da zan ambaci gaba xayan abin da na gani da wanda na ji a kan wannan lamari da wannan littafi ya gagari kundila. Na kuma tabbata mutane da yawa sun san wasu abubuwa filla-filla na wannan labari, waxanda ban sani ba.

Taimakon da ‘yan Shi’ah ke yi wa kafirai a kan masulmi da irin yadda suka fi qaunar ganin kafirci da kafirai sun bice hasken musulunci da musulmi abu ne da ya fi rana bayyana idan ta fito.

Mu qaddara cewa musulmin da ‘yan Shi’ah ke wannan matsananciyar gaba da su, azzalumai ne kuma fasiqai, waxanda kuma ke bayyanar da nau’o’an bidi’o’i waxanda suka fi zagin Ali da Usmanu Raliyallahu Anhuma nauyi. Duk da haka, da a ce ‘yan Shi’ah mutane ne masu hankali, kamata ya yi su auna irin sharrin da wannan aiki nasu zai haifar, da alherin da ke cikin rashin yin sa.

Ai ka ga su Ahlus-Sunnah, da yake mutane ne masu cikar hankali, tattare da abin da suke faxa na kasancewar Harijawa da ‘yan Shi’ah da wasunsu daga cikin mutanen bidi'a karkatattu, ba su tava taimakon kafirai a kan xaya daga cikinsu ba, balle su guraci rinjayen kafirci da kafirai fiye da yadda wata ‘yar qaramar bidi'a za ta bayyana. Don sun san haka rosa kai ne.

Su kuwa ‘yan Shi’ah da xai haka suke. Idan suka sami sa’a ba su iya ba. Dubi abin da suka haifar na varna a zamanin daular sarki Khudabandah, wanda aka rubuta wa wannan littafi, da muke martani a kansa. Sharrin da waxannan mutane suka qulla a wannan lokaci, da ya tabbata ya kama qasa sosai, da gaba xayan shari’o’in musulunci sun kwanta dama! Sai dai da yake ta Allah ba tasu ba; kullum suna qoqarin bice hasken Allah ta hanyar amfani da kaifin halsunansu, amma Allah na daxa tabbatar da haskensa, ko da kafirai sun qi.

Su kuwa halifofi da sauran Sahabbai su ne tushen duk wani alheri da musulmi ke ciki a yau har Allah Ya naxe qasa. Su ne suka yi jihadi fi sabillillahi, har hasken imani da musulunci da Alqur’ani da sauran fannonin ilimi, da ibadodi suka kammala, dashensu ya haxu ya yi kyau ya barbaje. Musulmi suka yi galaba a kan kafirai, kalmar Allah ta xaukaka, aljanna ta tabbata ga musulmi wuta ta nisanta daga gare su. Gaba xaya aikin da Sahabban can suka yi na yaxa addini, shi ne ya tabbatar da wannan.

A kan haka babu wani mutum da ya yi imani da Allah face Sahabbai nada kamisho da falala a cikin haka har rana ta qarshe. Kai su kansu ‘yan Shi’ah, duk wani abu na alheri da suke cikinsa, sun same shi ne albarkacin waxannan Sahabbai. Su kuma halifofin Annabi Sallallahu Alaihi Wasallama shiryayyu, su ne kan gaba a sahun wannan alheri da aka samu ta hanyar Sahabbai. Domin kuma a duniya da lahira babu wani Sahabi da ya kamo qafarsu a fagen aikata alheri da dasa shi. To, ta yaya za a wayi gari yau a ce mana su ne mavuvvugar sharri, su kuma ‘yan Shi’ah wai su ne mavuvvugar alheri?

Alhali kuwa sanannen abu ne cewa, shi wannan xan Shi’ah yana bisa turbar waxancan ‘yan Shi’ah ne, ta qin jinin Sahabbai. Ashe wannan ba yana nuna kasancewarsu mafi sharrin waxanda Allah Ya toshe wa basira ba?:

ﭽ ﯲ ﯳ ﯴ ﯵ ﯶ ﯷ ﯸ ﯹ ﯺ ﯻ ﯼ ﭼ الحج: ٤٦

Domin haqiqa makanta ba ta idanu ba ce, amma makanta (ta gaskiya) ita ce makantar zukata waxanda ke cikin qiraza (22:46).


Yüklə 2,75 Mb.

Dostları ilə paylaş:
1   ...   24   25   26   27   28   29   30   31   ...   51




Verilənlər bazası müəlliflik hüququ ilə müdafiə olunur ©muhaz.org 2024
rəhbərliyinə müraciət

gir | qeydiyyatdan keç
    Ana səhifə


yükləyin