Tafarkin sunnah



Yüklə 2,75 Mb.
səhifə29/51
tarix28.10.2017
ölçüsü2,75 Mb.
#17506
1   ...   25   26   27   28   29   30   31   32   ...   51

3.0 ZANGO NA UKU:

DALILAI NA HANKALI

Xan Shi’ar ya ce: Fasali na uku wanda zai yi magana a kan dalilan da ke tabbatar da cancantar sarautar Sarkin Musulmi Aliyu xan Abu Xalib, shugaba bayan wucewar Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama. Duk da yake waxannan dalilai na da matuqar yawa, ta yadda ba za a iya qididdige su ba. Saboda haka za mu ambaci mafi muhimmanci daga cikinsu, ta hanyar karkasa su gida huxu. Inji shi:

Waxannan dalilai guda biyar ne. Na Farko: Lalle ne duk wanda zai shugabanci al’umma bayan Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama a matsayin Imamu, to, ya kasance ma'asumi. Wannan dalili kuwa shi zai tabbatar da cancantar Aliyu Raliyallahu Anhu da wannan kujera.

“Dalilinmu a kan goshin wannan magana inji xan Shi’ah, wato wajabcin samar da shugaba ga jama’a da zancen kasancewarsa ma'asumi shi ne: Kasancewar mutun wata halitta da Allah Subhanahu Wa Ta’ala Ya sa wa son zama cikin taro, ta yadda rayuwarsa za ta yi qunci da tasgaro matuqa, idan ya ce zai rayu shi kaxai. Saboda buqatunsa na samun abin ci da sha, da sutura da wurin bacci kodayaushe, ba za su samu tabbatuwa ba, matuqar ya yi tsinbirin gata. Dole ne yana da buqata da gudunmawar wasu mutane irinsa, waxanda kowane daga cikinsu, har da da shi kansa, zai tsare wa xan’uwansa wata daga ta waxancan buqatu. Ta wannan hanya ce kuwa kawai jinsin xan adam zai iya ci gaba da wanzuwa a bayan qasa”.

“Irin wannan haxuwa kuwa, wuri xaya da nufin zama, ta gadi haifar da qeta da son kai. Ta yadda wasu daga cikin mazaunan za su yi qyashin abin da ke hannun wasu har ma su yi gurin gushewarsa ko dawowarsa a hannunsu ta hanyar qwace ko yaudara. Wanda hakan kan haifar da qunci da tajin-tajin da tashin fitinu. Ka ga a irin wannan yanayi, dole ne a samar da shugaba ma'asumi wanda zai hana mutane zaluntar juna da wuce iyakoki. Ya tabbatar da ganin kowa ya tsaya wurinsa tare da qwato wa wanda aka zalunta haqqinsa daga wanda ya yi zalunci da kuma sadar da kowane haqqi ga mai shi. Duk kuwa wanda zai hau wannan matsayi, lalle ne ya kasance ba ya kuskure ko mantuwa ko savo. Idan kuwa ya kasa cika waxannan siffofi, to zaune ba ta qare ba. Don har yau dai al’ummar na da buqata da wani shugaban ba shi ba. Domin kuwa toshe kafafen kurakuran a cikin al’umma ne dalilin da ya sa aka naxa shi, To, idan har kuwa shi ma irinsu ne, an yi faxuwar guzuma kenan ka ga dole a nemo wani shugaba wanda ba ya kuskure. Idan shi ma ya bi hanyar na gabansa, to babu hus. Haka al’amarin zai ci gaba da tafiya yana kwan-gaba kwan-baya”.

Xan Shi’ar ya ci gaba da cewa: “Shi kuwa abin da qirjin wannan magana ya qunsa, wato ma'asumancin Aliyu Raliyallahu Anhu a matsayin shugaba abu ne bayyanane. Domin kuwa babu xaya daga cikin Abubakar ko Umar ko Usmanu wanda ma’asumancinsa ya tusgo bisa haxuwar malamai. Amma ta tabbata cewa Ali Raliyallahu Anhu ma'asumi ne. Saboda haka shi ne ya kamata ya zama magajin Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama na farko”.



Martani:

Gaba xayan waxannan maganganu; goshin da qirjin, vatattu ne. Bari mu fara da farko, inda ya ce: Dole ne a samar da shugaba ma'asumi wanda zai hana mutane zaluntar juna da wuce iyakoki, ya tabbatar da ganin kowa ya tsaya wurinsa, tare da qwato wa wanda aka zalunta haqqinsa daga wanda ya yi zalunci, da kuma sadar da kowane haqqi ga mai shi. Ya kuma ce, duk wanda zai hau wannan matsayi, lalle ne ya kasance ba ya kuskure ko mantuwa ko savo.

To a nan sai mu ce: Mu ma Ahlus-Sunnah mun yarda da wannan dalili da ke wajabtar da samar da shugaba ga jama’a. Amma inda gizo ke saqa shi ne, wane ne ma'asumin? Amsa a nan ita ce: Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama. Kuma wajibi ne a kan kowane mutum a kowane zamani ya yi xa'a da biyayya gare shi. Kuma Alhamdu lillahi, abin da ke hannunmu na horo da hani, waxanda ya yi wa al’ummarsa, ya fi cika da kamala a kan abin da xaixaikun shugabanninku suka sani na horo da hani, waxanda voyayyen imaminku ya yi.

Ko shakka babu, shugabanci da ma'asumancin Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama su ne mafiya bayyana da tabbata. Kuma ga shi babu wani daga cikin al’ummarsa wanda ya jahilci horace-horace da hane-hanen da ya yi. Magana ta qare. Wannan shi ne matsayinmu.

Su kuwa ‘yan Shi’ah, qololuwar abin da za su gaya maka a kan sha’anin nasu ma'asumin shi ne har yanzu bai riga ya bayyana ba, ana nan ana ta dakon isowarsa. To, ba wannan ma kawai ba. Babu wani mutum a duniya ko da kuwa daga cikin ‘yan Shi’an, da zai bugi qirji ya ce ya san wani horo ko hani daga wannan imami na voye, kamar irin yadda gaba xayan al’umma suke da cikakkar masaniya da shari’o’in da Manzonsu Muhammadu Sallallahu Alaihi Wasallama ya zo masu da su. Ta yadda ba su da buqata da wani shugaba wanda ba shi ba. Ko wani Wanda zai yi labu da wasa da abubuwan da wannan addini nasu ya qunsa. Domin kuwa duk abin da suke da buqata da shi, don gudanar da ayyukan addini, Manzon ya riga ya zazzage masu shi. Ba kamar xaixaikun masu da’awar wancan shugaba ma'asumi ba, waxanda ba su san komai dangane da shi ba ko da an qaddara samuwarsa. Har yau dai baya ga Aliyu Raliyallahu Anhu babu wani daga cikin imaman can da ake wa gogen ma’asumanci, da ya tava jagorantar mutane a zahiri. Sai ko Al-Hasan da ya yi na wata shida.

Muna da cikakkar masaniya kuma yankakka, cewa akwai mabiyan wannan imami voyayye, a qasar Yaman da Khurasana da waxansu qasashe, da ba su san abu xaya wanda ya yi umurni ko hani da shi ba. 'Yan korensa ne kawai ke wasa da hankalin mutane.

Amma ka ga waxanda suka gaji ilimin da Muhammadu Sallallahu Alaihi Wasallama ya zo wa duniya da shi, sun san komai a cikinsa filla-filla. Kuma suna sanar da sauran mutane shi tsakani da Allah; ba ragi ba qari, fiye da yadda waxanda ke waqen bin Ali Raliyallahu Anhu suka san matsalar da irin yadda suke isar da ita ga duniya. Iyaka kawai abin da suke qoqarin tabbatarwa shi ne wajabcin samar da shugaba ma'asumi a raye.

To, muna tabbatar masu da cewa, wannan magana tasu vata ce, ta fuskoki kamar haka:



Fuska ta farko: Ba a tava samun wani shugaba, a inda aka fito, da waxannan sifofi da suka zayyana ba. Haka kuma a wannan zamani namu. Wanda dai ke da waxannan sifofi shi ne wanda ko a wurin mabiyansa sunansa Malam-na-Voye, balle a wajen masu hankali a cikin al’umma. Su a wurinsu sunansa Malam-babu.

To duk kuwa wanda yake haka, babu wani abu daga cikin manufofin shigabanci, da ke iya tabbatuwa ta hanyarsa, asalatan. Kai duk wanda ma za a shugabantar wa mutane, ko da kuwa iliminsa da adalcinsa ba su taka kara sun karya ba, matuqar dai ga shi a sarari, to ya fi fa’ida gare su bisa ga irin wannan da babu wata hanya da zai iya amfanar da su da ita da komai.

Ko da kuwa mabiyan shi wannan ma'asumin voye, sai sun nemi gudunmawar wasu mutane a kan wasu al’amurra nasu. Waqen kasancewarsa majivincin al’amuransu kawai suke yi. Amma idan suka tashi neman wani agaji sai su nema daga wani qasurgumin kafiri ko azzalumi. Idan kuwa har wannan ma'asumi da ake jira ya kasa amfanar da ko waxanda suka yi imani da shi a cikin wani sha’ani nasu na duniya ko lahira, ba ta yadda za a yi ya iya tabbatar da wani abu na gallar shugabanci da manufofinsa ga wani.

To, idan ko har babu wata manufa daga cikin waxannan manufofi na shugabanci da ke iya tabbata ta hanyar Malam-na-Voye, to, kuma ba mu da buqatar tabbatar da hanyoyin rashin yiwuwar haka. Domin kuwa ba don guga tana guga ake sayenta ba. A’a sai don a jawo ruwa da ita. To idan kuwa har ta tabbata cewa babu wata rijiya a gari da ke da ko xigo na ruwa, to zancen guga vata lokaci ne. Kamar dai a ce ne ga mutane na buqatar agajin abinci da abin sha masu kama kaza. Kuma qabila kaza ce kawai ake iya samun su daga gare su. Amma kuma tarihi ya tabbatar da cewa ko veran masallaci ya san da zaman wannan qabila saboda tsananin rashi da talauci. Ka ga ai ba magana.

To kamar haka ne babu wata fa’ida da za’a samu a cikin neman duk wani abu da ake da masaniyar babu shi. Ko kuma biyayya ga wanda ba ya da amfani ko masoso. Ai ana buqatar shugaba ne don xayan abubuwa biyu: Ko dai don wani ilimi da ya kevanta da shi, don ya isar da shi ga mutane ta hanyar karantarwa. Abu na xaya kenan. Na biyu Kuma, ko don ya taimaki mutane da qarfin mulkinsa a kan aiki da wani ilimin da suka riga suka sani.

To, shi wannan Malam-na-Voye da ake jiran bayyanarsa, ba ya iya amfanar da al’umma da xayan waxannan abubuwa biyu. Duk ma abin da suke da shi na ilimi, sun same shi ne daga cikin zantukan waxanda suka gabace shi. Ta fuskar aiki kuwa, sukan nemi gudunmawar musulmi ne, a cikin abubuwan da kansu ya haxu da nasu a ciki. Idan kuwa ba su sami haka ba, sai su nemi gudunmawar kafirai da zindiqai da makamantansu.

Kar ka yi mamakin wannan magana tawa. Idan ba ka sani ba, Allah bai halicci mutane mafiya ragganci da jahilci kamar waxannan mutane ba, tattare kuwa da gogen da suke yi na kasancewa mabiyan ma’asumi. Alhali kuwa ita wannan kalma ta ma’asumi na nufin siffantuwa da cikakken ilimi da qarfin iko na aiwatarwa. Amma su, da ilimin da ikon ba su da ko xaya. Hakan kuwa ita ke tabbatar da koruwar duk abin da suke waqa. Kuma babu xaya daga cikin shugabannin da aka yi, wanda manufofin shugabanci suka tabbata ta hannunsa albarkacin xaya daga cikin waxancan imamai goma sha biyu. Idan kuma ka cire Ali Raliyallahu Anhu ka yi qasa da lissafi, za ka taras cewa, babu wani abu na ilimi ko kishin addini da suka qarar da mutane da shi, fiye da yadda takwarorinsu ke iyawa da yi. Abin da Zainul Abidina da xansa Baqiru da jikansa As-Sadiq suka kasance suna karantar da mutane a zamaninsu, daga cikin abin da Allah ya sanar da su, bai fi wanda sauran malaman zamaninsu ke karantarwa ba. Kai akwai malaman da ma suka fi su ilimi da amfanar da jama’a a wancan zamani. Babu wani ma’abuci ilimi da bai san haka ba.

To, ko da ma za a qaddara cewa sun fi kowa ilimi da kishin addini a wancan zamani, ai wannan ba wani abu ne ba. Domin tarihi bai ambaci wani tasiri da ma’abuta ilimi da kishin addini suka yi, a fagen tabbatar da mutane a kan gaskiya da hana su varna, ta hanyar amfani da qarfin iko ba, kamar yadda ma’abuta mulki suka yi.

To, sauran imamansu bayan ukun da muka ambata, musamman ma dai biyun na qarshe, ba su da wani ilimi da tarihi ya tabbatar da al’umma ta qaru da shi, ko wani qarfi da ta yi shinge da shi. Matsayinsu bai fi na sauran Hashimawa ba, waxanda mutane ke gani da gashi a ka don kusancinsu da Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama da fuskar dangantaka. Ilimin da su ke da shi na abubuwan da suke da buqata da su a musulunci, bai fi na sauran takwarorinsu ba. Shi ne kuma irin ilimin da fararen hula daga cikin musulmi ke da shi.

Amma abin da ma’abuta ilimi suka kevanta da shi na sannai, su ba su sami wani rabo daga cikinsa ba. Saboda haka ne ma ba a yi almajircin ilimi a wurin su ba, kamar yadda aka yi ga waxancan uku na farko. Da kuwa mutane a lokacinsu sun san akwai abin, da sun je nemansa. Amma ka san ba wanda ya san abin da ya ke buqata kamar mai neman ilimi

Wani abu da zai tabbatar maka da haka shi ne, duk wanda ke da ilimi da girman asali, za ka tarar da asalin ya taimaka ga kwararowar mutane zuwa gare shi don su qaru. Ai ka ga da yake xan Abbas na da tarin ilimi, al’umma ta ji ta kuma fa’idantu da shi. Kuma babba da yaro kowa ya ji sunansa.

Haka Imamus-Shafi’i, nasabarsa ta Quraishawa ta qara fitowa da shi fili, ilimin da ya ke da shi na fiqihu da sauran fannona ya bayyana, aka qaru da shi.

Amma da zarar mutum ya tarar da babu abin da yake nema a wurin da ya yo qarere, ko tashen batun ba zai yi ba. Yau da za a cika duniya da waqen cewa ai wane qwararren malami ne a fannin likitanci ko Nahawu, aka cicciva shi har wasu daga cikin masana likitanci ko Nahawu suka ziyarce shi. Amma suka tarar da cewa bai san abin da suke nema a cikin waxannan fannoni ba. za su koma inda suka fito ne. Ka ga koxa shi da xaukaka sunansa da jahilai suka yi bai daxa shi da komai ba.

Wannan kenan. Kuma sai Shi’ah ‘yan-sha-biyu suka tsallaka suka je wurin Mu’utazilawa suka aro wasu aqidu da suka danganci siffofin Allah da makamantansu. Ita kuma matsalar shugabanci sai suka azizita ta har ta fi Annabta matsayi a wurin su.

Suka ci gaba da cewa: Al’adu da shuxewar kwanuka sun tabbatar mana da sanin cewa, a duk lokacin da jama’a suke qarqashin jarumin shugaba wanda ake tsoro, ake kuma yi wa biyayya ko ba don Allah ba. Sai don iya shugabancinsa da shinfixa hannayensa. Haka ta fi sa su kasancewa mafi zama kusa ga shiriya da nisantar varna. Balle daxa idan babu shugaban baki xaya, sai a wayi gari qunci da yamutsi sun mamaye su, su kuma zama nesa qwarai daga shiriya.

To, ka ga wannan matsala ita ce kanwa uwar gami, a cikin sha’anin sa hankali gaba a cikin addini. Sanannen abu ne da ba mai musun sa, sai wanda ya jahilci halin rayuwa, bai kuma san qa’idar xorewar zaren tunani a cikin kai ba. Daga nan sai suka ce: Idan kuwa har hakan za ta taimaka ga xauke nauyin hukunce-hukunce, ai kuwa tabbatar da wanzuwarsa ya zama wajibi. Don haka sai suka ambaci siffofin shugaban, waxanda suka haxa da ma'asumanci da waninsa.

Wasu daga cikinsu suka tambayi kansu da cewa: Ah, to idan mun ce shugaba rahama ne da taimako ga xauke nauyin shari’a, to ai ba mu tare da shi yanzu! Ba kuwa yadda za a yi luxufi da taimakon wanda ba ya nan ya wanzu. Idan kuwa har ta tabbata ba za a iya samun wannan luxufi ba matuqar dai imamin yana fake, ga kuma nauye-nauyen shari’a sun tabbata, kenan cewar da muka yi shugaba luxufi ne a cikin addini ta tashi. Kuma ba mu da bakin sake sharxanta ma'asumancin wani shugaba.

Sai kuma suka ba junansu amsa da cewa, a’a, ai muna nufin ne luxufin wancan shugaba da ke fake, na samuwa ne ga waxanda suka san da zamansa, suna nan bayyane. Waxanda kawai wannan luxufi ba zai sama ba, su ne waxanda ba su yarda da kasancewarsa imaminsu ba. Kamar dai yadda luxufin sanin Allah ba zai samu ga wanda bai san shi ba.

A qarshe suka ce: Qaryar waccan tambaya ta qare, sanadiyyar wannan bayani. Saboda haka suna nan kan bakarsu na kururuta wajabcin ma’asumancin shugaba.

Kawowarsu nan ke da wuya sai aka ce masu: To, idan kuwa luxufinsa na iya saduwa da ku yana faken kamar yadda zai sadu da ku idan ya bayyane, kenan wajibi ne ku wadatu daga bayyanarsa, don ba ta da wani amfani. Sai kawai ku ci gaba da biyayya gare shi yana faken har ku mutu. Mun kuwa san wannan ba shi ne manufarku ba.

Sai suka sake karvawa da cewa, ai abin da muke nufi da saduwar luxufinsa ga waxanda suka yi imani da kasancewarsa shi ne ta hana su kusantar miyagun ayyuka. Kamar yadda kuma za su ci gaba da kasancewa idan ya bayyana. Amma ita bayyanar tasa za ta wajabtar da wani abu da ba wannan ba. Wato bayyanarsa za ta kwave hannuwan azulumai daga taushe muminai da suka yi. Ta kuma karve dukiyoyin da masu iko suka qwace ta mayar wa masu su da abinsu. Ba wannan kawai ba, za ta kuma kawar da azzulaman daulolin da mu ba mu iya kawarwa, sai da taimakon wannan imami na voye.

To a nan sai a tuna wa ‘yan Shi’ah cewa: Kar fa ku manta, shugaban nan da kuka ce luxufi ne, shi ne wanda hankulla da al’adun rayuwa suka sheda. Wanda kuma kuka ambata da cewa duk lokacin da jama’a suke qarqashin mulkin jarumin shugaba wanda ake tsoro, ake kuma yi wa xa’a ko ba don Allah ba. Hakan za ta sa su kasancewa mafi zama kusa da shiriya, da nesa-nesa da varna. Bayan wannan kuma kuka sharxanta kasancewarsa ma'asumi. Kuka kafa hujja da cewa, saboda da ita ne kawai shugabancin nasa zai iya tasiri. Amma kuma sai ga shi gaba xayan imaman da suka kasance kafin wannan da ake jira, babu xaya daga cikinsu da ya taka wannan rawa; babu wanda ya kasance mai qarfin iko da zartarwa daga cikinsu. To qaqa kenan? Kun ga maganar can taku ta zama sharholiya.

Tsawon kwanukan da Ali Raliyallahu Anhu ya yi yana halifa, abubuwan da ya gudanar na halifanci da zartarwa ba su kai na waxanda suka gabace shi ba. A yayin da sauran waxanda da suka biyo bayansa daga cikin imaman naku babu wanda ya gudanar da wani abu na iko da zartarwa.

To, daxa balle shi wancan bawan Allan na voye, wanda babu ko harafi xaya na abin da ya gudanar, domin ko ganin sa ba a tava yi ba.

Yau da waxanda suka yi imani da samuwarsa, za su ji cewa, fiye da shekaru 460 kenan da ya faku, kuma saboda jin tsoro ne ba zai iya bayyana ba, balle ya gudanar da hukunce-hukunce. Kuma kodayake can fake xin ba ya da ikon bayar da wani umurni ko hani, to, za su fahimci cewa ashe saboda haka ne qunci da varna suka yi kanta a cikinsu. Kuma a qashin gaskiya haka ne; babu wani bananci a cikin wannan magana.

A kan wannan dalili ne kake ganin qungiyoyin ‘yan Shi’ah sun fi kowace qungiya kasancewa cikin qunci da varna, da yawan savani ta hanyar kace-nace, da bankaura. Irin yadda kashe-kashe da savani da zaluntar juna ke gudana tsakaninsu, ko tsakanin waxanda ke qarqashin jagorancin kafirai albarka. Daxa balle waxanda ke cikin taragon musulmin direba. To idan ka dubi wannan sai ka ga wane luxufi ne waxannan mabiya na wannan “Malam-na-Lave” suka samu?

Shi dai imani da kasancewar Allah Ta’ala samamme, rayayye, mai iko a kan komai, yana kuma horo da yin xa’a gare shi tare da tanadin lada ga wanda ya yi, yana kuma hani daga savo, tare da shirin azabtar da wanda bai ji bari ba. Imani da waxannan abubuwa na daga cikin manya-manyan abubuwan da ke sa tsoron Allah da kwaxayin rahamarsa a cikin zukata. Ta yadda sanin zai kasance tafarkin samun lada da jinqayinsa. Daga nan sai ka ga an dage a kan aikata abubuwan da ya yi umurni da su, da nisantar waxanda ya hana. Za ka taras da duk wanda ya kai wannan matsayi yana samun tashin hankali a duk lokacin da ya savi Allah ko a kan kuskure ne. Saboda ya kwana da sanin cewa Allah masani ne kuma mai iko. Kuma sunnarsa ta riga ta gudana a kan saka wa masu biyayya da alheri da azabtar da waxanda suka kangare. To, ya za a kwatanta wannan sani na Ubangiji da yake da wannan xinbin fa’ida da sanin Malam-na-Boye?

Duk mutumin da aka san babu shi fiye da shekaru xari huxu, kuma bai iya azabtar da kowa ko da da baqar magana, ba ya kuma da abin da zai ba wani na lada. Hasali ma tsoron mutane yake yi, saboda haka yake fake; ba zai iya fitowa ba, balle ya bayar da wani umurni ko hani. Sanin akwai irin wannan mutum ba zai sa a aikata abin da ya yi horo da shi, ko a bar abin da ya hana ba. A maimakon haka ma sanin da ake da shi na kasancewarsa da tsoron da yake da shi, za su sa ne kawai a daxa kutsa kai cikin miyagun ayyuka. Musamman ma kasancewa an xauki tsawon lokaci ba a ji ya karrama wani ko ya gyara wa wani zama ba.

To mu qaddara ma yakan bayyana sau xaya bayan kowace shekara dari ya xan zartar da wani xanyen hukunci. Ba zai kama qafar xaya daga cikin shugabanni a fagen luxufi ba, ko da kuwa bayan kowace shekara goma ce yake bayyana, ko ma ce bayan kowace shekara xaya. Ba dai zai kama qafar shugabannin da ke tare da jama’a kodayaushe ba a fagen amfanarwa, tattare kuwa da abin da ke tuzgowa daga gare su na zunubbai da zalunce-zulunce a wasu lokutta. Sun dai tsayar da shari’ar Allah, ta hanyar zartar da hukunce-hukunce na horo da zuba qoqari a cikin kwaxaitar da jama’arsu ga yin ayyukan xa’a, fiye da yadda wanda ba ya ko bayyana gare su daga bana sai baxi. To daxa balle wanda ya salwanta sukutum; masu hankali suka tabbatar da rashin wanzuwarsa. Waxanda ke waqen akwai shi xin ma, suna da yaqinin cewa, kasasshe ne, matsoraci; bai ma tava tavuka wani abu irin wanda xaixaikun mutane ke tavukawa ba, daxa balle irin abin da shugabanni ke yi.

To wace irin jaruntaka ce ko kwarjini irin wannan mutum ke da su, da har za a shakkarsa? Wane iko ke ga irin wannan balle har ya shimfixa hannunsa a kan mutane, ko ya zama mai taimaka masu ga kasancewa mafi zama kusa ga shiriya!

Duk wanda ya yi xan batun zuci a cikin wannan lamari, zai tabbatar cewa jahilci da girman kai da wautar waxannan mutane sun isa. Ganin irin yadda suka sakankance da kasancewar samun luxufin wannan mahaluqi na voye, tattare kuma da kasancewarsa kasasshe, kamar yadda wai za su sami luxufin nasa ko da bayyana ya yi. Kuma wai sakamakon amincewa da kasancewarsa samamme a cikin halin nasa na kasawa da tsoro, a can faken, daidai yake da kasancewarsa a fili, kuma a cikin halin maza kuta da aminci. Wai kuma tsurar ruwan zatin wannan masaniya luxufi ce a karan kanta ga wanda ya siffanta da ita, kamar sanin Allah Subhanahu WaTa’ala. Tirqashi wani aiki sai jahili.

Fuska ta biyu:

Muna son mu ji ta daga bakinku ku ‘yan Shi’ah. Shin cewar da kuka yi, dole ne a samar da shugaba ma'asumi wanda zai tsare aikata waxancan abubuwa da kuka ce kalmar luxufi ta qunsa, na nufin wajibi ne ga Allah Subhanahu WaTa’ala Ya halicci mutum mai waxancan siffofi ya kuma tabbatar da samuwarsa. Ko ko a’a wajibi ne ga mutane su yi masa bai’a a matsayin shugaba bayan Allah Ya samar da shi?

Idan kuna nufin wajabci na farko, to qaryarku ta sha qarya. Domin kuwa Allah Subhanahu WaTa’ala bai halicci mai irin waxancan siffofi ba. Qul xin abin da kuke iya cewa shi ne, ai Ali Raliyallahu Anhu ma'asumi ne. Amma ai ko shi xin, tarihi ya tabbatar da cewa Allah Subhanahu WaTa’ala bai arzutta shi da wata halitta a cikin jikinsa ko rundunarsa ba, wadda za ta iya ba shi damar aikata irin waxancan abubuwa da kalmar ta luxufi ta qunsa a wurin ku.

Ku da kanku ma, kuna faxa wa duniya cewa sayyidina Ali Raliyallahu Anhu ya kasance mai rauni kuma audugar kasuwa, wanda aka zalunta a zamanin halifofi uku na kafinsa. Kuma a daidai lokacin da ya haxa runduna don xaukar fansa, sai aka sami wata runduna daban, ta yaqe shi. A qarshe ma dai ko irin abin da waxancan halifofi uku suka gudanar na alheri, waxanda kuke xauka azzalumai, Allah bai ba shi ikon gudanarwa ba.

Ka ga kenan waxancan halifofi uku ne, suka dace da taimakon Allah har suka shimfixa waxancan alherai, irin waxanda shi Ali Raliyallahu Anhu ya kasa aikatawa. Kenan dai, a haka ta tabbata Allah bai halicci irin wannan ma'asumi da kuka ba shi shawarar halittawa ba.

Idan kuma kuka ce, muna nufin wajabci na biyu ne. Wato ai Allah Ya riga ya halicce shi. Muna dai cewa ne ya zama wajibi kan mutane su yi masa bai’a, su kuma taimake shi.

A nan sai mu ce maku kun ci tuwon gigi. Babu wasu mutane daga cikin mabiya ko magabta da aka samu sun yi haka. Wato babu wani daga cikin waxancan ma'asumai da kuke tutiya, wanda mutane suka mara wa baya, ko Allah Ya taimaka. Kun kuma san ba yadda za a yi waxancan nasarori na luxufi su tabbata a hannun shugaba sai tare da haxuwar hancin waxannan gudunmuwowi guda biyu. Da zarar kuwa an rasa su, to, ba magana. Don hangen dala ai, ba shi ne shiga birni ba.

Fuska ta uku:

Idan dai gaba xayan abubuwan da ke iya tabbatar da waccan galla ta shugabancin ma'asumi, sun kasa samuwa. Da yawa ma daga cikin sharuxxan samuwarsu sun shuxe, me zai hana mu qaddara cewa ma'asumancin ne aka rasa? Idan kuwa har ta tabbata an rasa ma’asumancin, ko dai saboda rashin cancantar shi wanda ake gani ma'asumin, da iya xaukar rawanin, ko babu ma’asumacin ma samsam. Duk dalilin da ya tabbata daga cikin waxannan dalilai biyu, xaya ne.

To a kan haka, ta yaya aka samo wajabcin halittar shugaba ma'asumi a ma'aunin hankali, a kan Allah Subhanahu WaTa’ala?

Kuma ko da wannan wajabci ya tabbata a kan Allah, to ai zai halicci ma'asumin ne domin ya zama sanadin kyautatuwar rayuwar al’umma duniya da lahira. Amma sai ga shi wannan ma’asumi naku, Allah ya halacce shi kasasshe, ta yadda ba zai iya tabbatar da wannan guri ba. Hasali ma varnace-varnacen da suka afku, da babu shi da ba su afku ba. Fuska ta gaba za ta qara tabbatar da wannan.



Fuska ta huxu:

Tabbas, ko da Allah bai halicci wannan ma'asumi naku ba, sharrin da ke gudana a bisa doron qasa ba zai wuce haka ba. Domin kuwa babu mai musun cewa samuwarsa ba ta daxa duniya da komai ba, ta fuskar raguwar sharrora. Babu wata illah qwaya xaya tal, da za a iya cewa, samuwarsa ce ta kawar da ita. Hasali ma samuwar tasa, ta sa mafi yawan al’umma sun qaryata shi, sun qulla gaba da magoya bayansa, sun kuma wai zalunce shi da mabiyansa, kamar dai yadda kuke faxa. Kuma ma wai a kan haka ne sharroran da Allah kaxai ne ya san iyakarsu suke ta faruwa.

Harwayau, a hankalce kasancewar sayyidina Ali Raliyallahu Anhu da sauran imamai goma sha biyu da makamantansu ma'asumai, ta kasa hana abin da ya faru ya faru. Domin kuwa ai kun ce zamanin halifancin magabatansa da na waxanda suka biyo bayansa cike yake da zalunci da sharri. Kenan akwai ayar tambaya a kan ma'asumancinsu. Qoqarce-qoqarcen da su waxancan ma'asumai naku suka yi na kawar da sharri daga bisa doron qasa, abu ne da ko wanda ba ma'asumi ba yake iyawa. Ka ga kenan kasancewarsu ma'asumai, kamar yadda kuke waqantawa, ba ta haifar da alheri ba, sai sharri.

Ka ko ga hikimar Allah Subhanahu WaTa’ala ba za ta bari ya halicci wani abu, don tabbatar da alheri ba, amma a qarshe ya kasance bai tabbatar da shi ba, sai sharri.

To a nan ‘yan Shi’ah na iya cewa, ai wannan sharri ya faru ne a sanadiyyar zaluncin da mutane suka yi wa wancan ma'asumi. Sai mu ce: Idan dai har Allah Subhanahu WaTa’ala a cikin hikimarsa, ya san manufar da ya halicci ma'asumin naku domin ta, wato tabbatar da alheri ba za ta tabbata ba, sai dai ma sharrin ya qara qamari, kenan babu wata hikima a cikin halittar tasa. Allah kuwa ba zai yi haka ba. Domin kuwa yin haka, kamar mutum ne ya xauki xansa ya danqa hannun wani don ya koya masa tarbiyya, alhali ya san haka ba za ta samu ba. A maimakon haka ma qara vata shi zai yi. Kai ka ga akwai mutum mai hikima da zai aikata haka?


Yüklə 2,75 Mb.

Dostları ilə paylaş:
1   ...   25   26   27   28   29   30   31   32   ...   51




Verilənlər bazası müəlliflik hüququ ilə müdafiə olunur ©muhaz.org 2024
rəhbərliyinə müraciət

gir | qeydiyyatdan keç
    Ana səhifə


yükləyin