Tafarkin sunnah



Yüklə 2,75 Mb.
səhifə31/51
tarix28.10.2017
ölçüsü2,75 Mb.
#17506
1   ...   27   28   29   30   31   32   33   34   ...   51

Martani na Huxu:

Kar fa ‘yan Shi’ah su manta, ijma’i a wurinsu ba hujja ne ba sai idan akwai wani ma'asumi a ciki. To, idan suka riqe shi hujja a kan tabbatar da ma'asumancin ma'asumi, hakan ta haifar da kwan-gaba-kwan-baya kenan. Watau ma'asumancin ma'asumi ba zai tabbata ba sai da yawun bakinsa. Kuma yawun bakin nasa ba zai iya zama hujja ba, sai idan an tabbatar da ma'asumancinsa. Ka ga kenan babu abin da ke iya tabbata daga cikin biyun.

A haka, kowa ya gane hujjar da ‘yan Shi’ah ke qoqarin kafawa a kan ma'asumancin wani busar kura ce. Kuma ba su da wata hujja ko madogara ta ilimi a kan duk abin da suka faxa. Tattare da wannan rashin makama da ya yi masu tarnaqi, za su ce mana: Ai sayyidina Ali Raliyallahu Anhu ne da kansa ya ce: "Ni ma'asumi ne kuma duk wanda ba ni ba, ba ma'asumi ba ne". Da za su ce mana haka a lokacin da muka nemi su faxa mana inda suka samo wannan wariya. Sai mu gaya masu cewa, ai ko wannan qarya da suka yi wa Ali xin, ba ta iya zama hujja yankakka. Domin kuwa magana ce, sallatatta da kowa ma ke iya bugun qirji ya faxa.

Haka kuma da za a qaddara tabbatuwar duniya da buqatar shugaba ma'asumi, to sai kuma a fantsama cikin kogin neman tantance shi. Da kuma a kan wannan tafarki za mu yi kicivis da xan Shi’ah Ba’isma’ile, mu nemi ya faxa mana ko waye ma'asuminsa, da kuma dalilin da ya sa yake ganin babu wani ma'asumi bayansa. Ina tabbatar maka babu wata hujja da zai iya tabbatarwa gamsassa a kan haka. Qarshenta zai shiga tubka da walwala ne, yana turmurza hancin kansa da kansa. Haka qarshen shi ma xan sha biyu zai kasance. Don ko dama walkin aro ne ke gindinsu wanda suka aro daga wurin Qadariyyawa, na imani da wajabcin riqo da mafi ingancin abu a cikin komai.

A kan wannan zance ne ‘yan Shi’ah suke gina aqidar wajabcin samar da shugaba ma'asumi. Da wannan zance nasu kuwa da na waxancan duk shirme ne. Domin da su ma za a tage su a ce sai sun kawo hujja karvavva a kan haka, za su kama ‘yan soshe-soshe ne. Domin kuwa asalatan hujjarsu ba ta wuce kawai, zancen wanda ma'asumancinsa bai tabbata ba, wanda suka ce ya ce: Shi ma'asumi ne.

Da kuma ‘yan Shi’ah za su kutso nan su ce, to, idan har hankali ya tabbatar da buqatar samar da shugaba ma'asumi, ko bisa qaddarawa ne. Kuma aka sami cewa Ali Raliyallahu Anhu ya furta da bakinsa ya ce: "Ni ma'asumi ne". To babu abin da zai hana a sakar masa zama hakan, don babu wani da ya yi iqirarin haka in ba shi ba.

To, sai mu ce masu: Wannan ba ta fisshe ku. Domin kuwa ko an qaddara samuwar ma'asumi a duniya tabbas. To, ba za a rufe ido a karvi zancen wani don kawai ya yi qarfin halin cewa: "Ai ni ne ma'asumin" ba. Don tana yiwuwa ya kasance wani na can ma'asumin na gaskiya ba shi ba. Ko da kuwa ba wanda ya ji shi yana kururuta cewa shi ma'asumi ne. Domin kuwa yana yiwuwa ya rufa ma kansa asiri, ya qi bayyana ma'asumancinsa. Kamar yadda ‘yan Shi’ah suka yardar wa Malam-na-Voye cewa ya rufa wa kansa asiri, ya fake don tsoron azzalumai.

To, duk da ma hakan akwai buqatar a tabbatar da cewa shi Ali Raliyallahu Anhu ya saka wa kansa rigar ma’asumantaka, kafin a yarda da hakan, ko da an daure an qaddara yiwuwarsa. Allah kuwa Ya tsare Ali, don tabbas bai ce haka ba.



Ga Kuma Amsa ta Biyar

Idan har ‘yan-sha-biyu ba su da wata hujja a kan wannan matsala ta ma'asumanci sai zancen da suka cirato daga ma'asumin. To, mun ji mun karvi zancen nasa, a cikin wannan matsala. Amma ba za mu kammala karvar zancen ba don mun yi imani da cewa babu wani mahaluki a duniyar nan da zai iya cirato zancen daga gare shi, ta hanya mutawatira, a yayin da muke da dubun-dubatar riwayoyi daga gare shi, waxanda ke tabbatar mana da cewa bai tava qudurta shi ma'asumi ne ba.



Amsa ta Shida

Damar da shi Alin ya ba wa alqalansa ta su yi hukunci da abin da ya sava wa ra’ayinsa, na tabbatar da cewa, ba ya ji a ransa ko masoso cewa shi ma’asumi ne. Ta tabbata da isnadi ingantacce cewa, Ali Raliyallahu Anhu ya tava cewa: "Ra’ayina ya yi daidai da ra’ayin Umar a kan kada a sayar da waxanda suka haifi ‘ya’ya maza daga cikin kuyangi a da. Amma yanzu ina ganin ana iya sayar da su". Nan take sai wani alqali daga cikin alqalansa, wanda ake kira Abidatus Salmani ya ce: "Ra’ayin can naka da ya yi daidai da na Umar, a matsayinku na jama’a ya fi soyuwa gare mu bisa wannan ra’ayin naka a matsayinka na tilo".

Haka kuma alqali Shuraihu ya kasance yana hukunci da ijtihadinsa, ba tare da ya shawarci Alin ba, ko neman tabbatarwarsa. Kuma Alin bai tava walwale hukuncin da ya yi ba. Hasali ma abin da yakan ce masu shi ne, ku yi hukunci kamar yadda kuka saba yi. Kuma ma da yawa shi kansa ya kan yi wata fatawa ko hukunci, ya kuma dawo ya walwale wannan ijtihadi da ya yi, da wani ijtihadin daban. Kamar dai yadda hakan kan faru ga takwarorinsa Sahabbai. Kuma waxannan, zantuka da muka riwaito daga gare shi, da isnadai ingantattu suna nan jibge.

3.1 Wai Allah ne ya Naxa Ali!

Xan Shi’ar ya ce: Fuska ta biyu, lalle wajibi ne ya kasance akwai nassi a kan duk wanda zai zama shugaba (Imami) saboda mun riga mun tabbatar da cewa, ba zai yiwu a bar mutane da zaven ba. Kuma saboda duk wanda za su zava da kansu ba zai fi wani na daban ba. Kuma zaven nasu yakan iya haifar da yamutsi da tashin hankali da fitinu waxanda suka fi girma. Kuma babu wani daga cikin shugabannin wannan al’umma wanda shugabancinsa ya tabbata a nassance, sai fa Ali. Kuma kan malamai ya haxu a kan haka. Kenan shi ne kawai wanda shugabancinsa ya inganta.



Martani:

Gaba xayan waxannan zantuka, na farko da na biyu shirme ne. Amma jayayyar da ake da ita ta fi qamari a kan zance na biyu, wato cewa, an yi ij’ma’i a kan nassancin shugabancin Ali kawai. Domin kuwa akwai qungiyoyin mutane da dama, daga cikin magabata da waxanda suka rufa masu baya, daga cikin masana Hadisi da Furu’a da Falsafa, da suka tafi a kan cewa akwai nassi a kan shugabancin Abubakar Raliyallahu Anhu. Akwai kuma wata qungiya ta ‘yan Shi’ah da suka tafi a kan cewa akwai nassi a kan Abbas.

Ka ga kenan cewar da ya yi, an yi ijma’i a kan Ali, qarya ce da ximinta. Shi kuwa wannan xan Shi’ah, marubucin wannan littafi, duk da yake yana daga cikin fitattun ‘ya’yan qungiyar tasa to, ko shakka babu gaba xayansu jahilai ne. Idan ba haka ba, kai ka san ba ta yiwuwa ga wanda ke da isasshen ilimi a kan zantukan malamai ya yi iqirarin haxuwar kansu a kan irin wannan xanyar magana.!

Wata fuska ta martani kuma ita ce: Gaba xayan wannan kaiwa da komowa da muke ta yi da ku, ba ya wuce neman yarda da kasancewar nassi a kan shugabancin wani ko qin yarda da shi. To, idan har muka yarda da kasancewarsa, a matsayinmu na Ahlus-Sunnah, abin da kuke cewa a cikin dame na biyu na wannan magana ya faxi; wato cewarku nassi ya kasance ne a kan Ali. Don ko mun riga mun turmuje ku da hujja, don mun tabbatar maku da akwai masu cewa akwai nassi a kan Abubakar. Idan kuwa muka qi yarda tun farko da akwai nassin, kenan wajabcin samun nassi a kan shugabancin wani ya faxi, domin babu mu a cikin ijma’in.

Sanannen abu ne cewa, ijma’i a wurinku ba hujja ba ne, zancen ma'asumi shi ne hujja. Kenan sai an koma an lalabo zancen wanda ake iqirarin ma'asumancinsa kafin a iya tabbatar da ingancin nassin ko ma samuwarsa. Ka ga kenan a qarshe da nassin da ma'asumancin babu wanda zai tabbata. Balle zancen wani da zai ce: "Ai Ni ne ma'asumin da ake nufi, ni ne kuma wanda nassi ya tabbatar da shugabancinsa" ya zama hujja. To, ai ba a gama gane ingancin zancen nasa ba. Ka ko ga ko shakka babu irin wannan ruxu da kwan-gaba-kwan-baya, kai matuqa ne a fagen jahilci.

Harwayau dai akwai tambaya a nan, shin cewar can da kuka yi, dole ne ya kasance akwai nassi a kan shugabancin duk wanda za a shugabantar, shin kuna nufin ne, dole ne ya kasance an samu nassin Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama ya faxa qarara a cinkinsa cewa: “Wane ga shi, shi ne halifa idan na wuce. Saboda haka ku saurare shi, ku yi masa xa’a” shi kenan kuma ya tabbata halifan da haka? Koko hakan ba ta isa, sai jama’a sun taru sun naxa shi?

Idan kuka ce, kuna nufin sharaxi na farko. To, sai mu amsa maku da cewa, mu kan ba mu yarda da wajabcin samun nassi a cikin irin wannan siga ba. Haka ma ra’ayin Zaidiyya ya yi daidai da na jama’a a kan rashin yarda da irin wannan nassi. Kun kuma san Zaidiyyar nan wani reshe ne a Shi’ah. Kuma ba ku xauki suna da wata matsala da Ali ba balle ku tuhumce su.

Haka ita kuwa cewar da xan Shi’ar ya yi wai: Saboda rashin nassi a kan shugabancin wanda ya kamata ya zama shugaba ne, aka samu jayayya da tajin-tajin. To, a nan sai mu ce: Ai, ko da mun qaddara samuwar nassi ko nassosa a kan wanda ya cancanci shugabanci, aka kuma bi diddigin waxannan nassosa aka tabbatar da ba su da sankara, don qarfin hujja da dalilinsu ya isa ko ina. To, hakan ba za ta hana jayayya da tajin-tajin ba. Domin kuwa ko a cikin hukunce-hukunce hakan kan faru. Hakan kuwa kan kasance ne saboda ba kowaxanne hukunce-hukunce ne aka samu bayaninsu filla-filla a nassance ba, ta yadda da soja da farar hula daga cikin al’umma kowa na iya fahimtarsu.

To, idan kuwa har irin waxannan nassosa na iya wadatarwa a cikin abin da ya shafi manya-manyan al’amurra, waxanda sanin su ya ke wajaba a kowane zamani, to kuwa wadatuwa da su a cikin qananan al’amurra, irin naxin wani shugaba tantantacce ya fi cancanta. Dama kuma mun riga mun bayyana maku a baya kaxan cewa, abu ne mai sauqi Annabawa su furta nassosa a kan hukunce-hukuncen manyan abubuwa savanin qanana.

To, kuma harwayau da waxancan nassosa za su taho da bayyanin dalilai a kan kasancewar wani sashe daga cikin jama’a, mafiya cancanta da shugabanci fiye da wasu, to sai a wadatu da hakan, a fita batun naxa wancan a matsayin halifa.

Kuma ai ka ga, dalilan da suka tabbatar da kasancewar Abubakar Raliyallahu Anhu mafi cancanta da shugabancin, bayyanannu ne. Babu kuma wani Sahabi da aka samu ya ja tsawo a kan haka. Ko waxanda suka yi ‘yar tankiya a cikin wannan sha’ani daga cikin Ansaru, ba sun yi haka ne, saboda suna musun kasancewar shi Abubakar Raliyallahu Anhu mafifici daga cikin Sahabbai Muhajiruna ba. Shi wanda ya wakilce su a cikin wannan tankiya ya nemi a naxa halifofi biyu ne; xaya daga cikin Ansaru xaya daga cikin Muhajiruna.

Da wani daga cikin dakarun ‘yan Shi’ah zai yi qarfin halin murza gashin baki ya ce mana, ai da Ansaru na da iko da sun hana wancan shiri na naxa halifa xaya kuma daga cikin muhajiruna, bisa qaddara samuwar waxancan nassosa. To, sai mu kuma mu mayar wa kura da aniyarta, mu ce, ko da akwai waxancan nassosa ai da su Ansarun na iya fatali da su; su juya masu baya.

Kamar yadda muka faxa kuma, nassosan hukunce-hukunce iri biyu ne: i) Nassi Gama-gari, wanda ya shafi ginshiqan hukunce-hukunce, da kuma ii) Nassi Rava-danni.

Idan cewar da kuka yi dole ne a samar da nassi a kan shugaba, kuna nufin nassin da zai tantance sharuxan shugaba da na talakawa da hakimai da su mufuti, da shedu da liman da ladan da kwamandan yaqi, da ire-iren waxannan hukunce-hukunce. To, sai mu ce ku mayar da wuqarku kube. Domin dama akwai su jibge, Alhamdu lillahi. Babu wani hukunci daga cikin sauran hukunce-hukunce, da aka bari huntu a wannan vangare.

A xazu kun kafa hujja a kan wannan nassi da cewa zai hana al’umma faxawa a cikin ruxani, wanda ka iya haifar da varnace-varnace masu girma fiye da irin waxanda kuka wajabta samar da nassi don kawarwa.

To, kada ku manta da cewa akasin haka ne ya faru. Domin kuwa tsawon kwanakin halifancin Abubakar da Umar da Usmanu Raliyallahu Anhum irin waxancan varnace-varnace ba su faru ba. Sun dai faru ne a lokacin halifan da kuke iqirarin samuwar nassi a kansa, ba tare da kowa ba. A zamaninsa ne al’amurra suka dagule. Sai ga shi nassin da kuke riqewa a matsayin abin da zai kawo zaman lafiya da kwanciyar hankali, bai kasance haka ba. Waxancan halifofi kuwa da ba ku xauka bakin komai ba, a zamaninsu ne wancan abu na rahama da luxufi da kuke rajin samuwarsa ya tabbata; ana zaton wuta maqera sai ga ta masaqa.

Ba mamaki, dole hakan ta kasance saboda kun wajabta wa Allah abin da ba ya wajabtuwa a kansa. Kun kuma bayar da labari irin na qanzon kurege, sai hakan ta tabbatar da kasancewarku maqaryata, jahilai.

3.2 Wane Nassi ne ke Iya Samuwa?

Ko dai ya kasance Annabi Sallallahu Alaihi Wasallama ya bayar da labarin mutumin da zai gade shi, tare da kwarzanta yadda shugabancin nasa zai kasance. Ta haka sai gaba xayan al’umma ta gane cewa, lalle idan aka naxa wane za a ce madalla. Domin ya sami tabarrukin shugaban halitta. Kun ga ba sauran wata jayayya. Ko bai buxa baki ya ce ai ga ni ni ne ba, sai al’umma ta zave shi. Kamar yadda ta faru ga Abubakar da Umar Raliyallahu Anhuma.

Ko kuma ya kasance Annabi Sallallahu Alaihi Wasallama ya bayar da labarin irin abubuwan da ke tabbatar da nagartar shugabanni. A kuma ga faruwarsu qarara, kamar yadda aka gani a lokacin halifancin Abubakar da Umar xin dai harwayau.

Ko kuma ya umurci wani daga cikin waxanda ke zuwa ziyararsa a lokacin da yake jinya, da cewa, idan ta Allah ta kasance gare ni ku bi wane. Ko kuma idan wani abu ya faru ku nemi wane. Ka ga hakan kenan ta tabbatar da kasancewar wanen halifa, bayan wancewarsa. Irin haka kuwa ta faru a kan Abubakar Raliyallahu Anhu a hadisin waccan mata da muka gabatar.

Ko kuma a taras da wata takarda da ya rubuta, ya bayyana cewa: Haqiqa Allah da muminai ba za su aminta da shugabancin kowa ba sai na wane. Haka xin ma ta faru a kan Abubakar Raliyallahu Anhu.

Ko ya yi umurni da sa wani mutum gaban sahu idan shi ya cika. Ka ga sai wannan ya zama halifa bayansa, ba tare da wata hamayya ba.

Ko a samu ya yi horo da kwaikwayon sunnar halifofi shiryayyu masu shiryarwa. Ya kuma faxi takamaiman lokacin da halifancinsu zai kasance. Da ha kansai a gane cewa duk waxanda suka ci nasarar zama halifofi a tsakanin wannan lokaci su ne shiryayyun halifofi da ya yi magana a kansu.

Ko ya kevance wasu zavavvun mutane, ya ba su wasu ayyuka, da ake iya riqawa matsayin silali. Kamar yadda ya zo a cikin Buhari da Muslimu cewa, ya ce wa Aishah: “Ki kira mini babanki da wanki, ina son in rubuta ma Abubakar wata takarda, da zata hana mutane su yi savani a kansa”. Sai kuma dai ya ce: “Ba komai. Allah da Muminai sun kau da kai daga kowa ban da Abubakar”. Da haka sai aka san cewa Abubakar ne Allah Ya zava. Shi ne kuma kawai wanda muminai za su yi wa muba’yi’a. Hakan kuwa ita ta faru.

Kuma akwai wasu hadissai ingantattu da ke tabbatar da cewa, shi ma Abubakar xin ya san da haka. Ya dai kame bakinsa ne saboda hillanci irin na Baquraishe. Kamar yadda Annabi Sallallahu Alaihi Wasallama ya kame nasa. Domin idan al’umma ta dace da wannan zave na Allah da Manzonsa, ba tare da katsalanda ko tirsasawar kowa ba, hakan za ta fi haifar da alheri gare ta, tare da nuna irin iliminta da matsayin da take da shi a wurin Allah.

3.3 Wai Ali Kaxai ke Iya Kare Shari’a

Xan Shi’ar ya ce: Abu na uku: Haqiqa wajibi ne shugaba ya kasance mai kiyaye al’farmar shari’a, bisa dalilin yankewar wahayi, tunda Annabi Sallallahu Alaihi Wasallama ya wuce, da kuma kasawar Alqur’ani da Sunnah a kan bayyana qananan hukunce-hukunce filla-filla, da kuma abubuwan da za su ci gaba da faruwa zuwa ranar qiyama. A kan haka dole ne a samu wani shugaba, wanda Allah Ta’ala zai naxa da kansa. Ya kuma kasance tsararre daga talalaviya da kuskure (ma'asumi). Don kada wasu hukunce-hukunce su salwanta. Ko a qara wasu a cikin na asali a kan ganganci ko kuskure. Babu kuwa wanda ke da waxannan siffofi sai Ali, ijma’an.



Martani:

Martaninmu a nan zai kasance kamar haka:-



  1. Ba mu yarda dole ne sai an samu wani mutum guda wanda zai kiyaye alfarmar shari’a ba. A’a, a imaninmu tsare alfarmar shari’a wajibin al’umma ne baki xaya. Domin kuwa yadda taron jama’a za su tsare alfarmarta wani mutum xaya tal ba zai iya ba. A yayin da ita kuwa jama’ar tana iya kiyaye alfarmar shari’a yadda mutum xaya zai iya, har ma ta daxa. Domin ko a fagen ba da labari, maganar mutane da yawa ta sha malin ta mumtum xaya. A kan haka, duk lokacin da hukuncin shari’a ya samu shedar wani adadi na jama’a amintattu to, buqata ta biya. Ko banza ma'asumancin taron jama’a ya fi girma a kan ma'asumancin wanda ba Annabi ba, ko waye shi. Ko da an qaddara kasancewar Abubakar da Umar da Usmanu Raliyallahu Anhu ma’asumai, to abin da Muhajiruna da Ansaru suka riwaito ya fi wanda kowanensu zai riwaito a xaixaice. Wani kuma abin lura shi ne, a duk lokacin da aka sami mafi yawan mutane na sukar wani mai riwaya, to, babu wani hukunci na shari’a da ke iya tabbata ta hanyar sa. Balle daxa a sami da yawa daga cikin al’umma na kafirta shi. Amma mutawatiri shi ne haxuwar bakin mutane da yawa akan batu ko da kuwa ba a gama tantance kasancewarsu adilai ba.

  2. Tun da yake ka ambaci ma'asumanci a farkon wannan magana. To, ba mu sani ba ko za ka aminta da wanda zai kiyaye alfarmar shari’a ko da kuwa ba ma'asumi ne ba? Idan ka aminta, sai mu ce, ba mu yarda da cewa, Ali ne ya fi kowa tsare alfarmar littafin Allah da sunnar Manzonsa ba, ko kuma ya fi kowa naqaltar su. Abin da muka yi imani da shi shi ne, Abubakar da Umar sun fi shi naqaltar littafin Allah da sunnar da Manzonsa.

  3. Shin kiyaye alfarmar shari’a da wannan shugaba zai yi a matsayinsa na ma'asumi, na nufin babu wani abu na shari’a da za a iya gane ingancinsa sai ta bakinsa? Koko hakan na yiwuwa ko ba da shi ba? In dai har ana iya kiyaye alfarmar shari’a ba sai da shi ba, to, babu buqatar kasancewarsa kenan ballai zamansa ma'asumi. In kuwa kun ce, ba a iya sanin kome sai ta bakinsa. To, kenan babu wata hujja da za a iya kafawa a kan doron qasa, sai an jingina ga abin da ya riwaito. To, ya za mu tabbatar da riwayar kafin mu san ma’asumi ne? Kuma babu wani ma’asumi in ba shi ba?

  4. Me zai hana ‘yan Shi’ah su gamsu da abin da Allah Subhanahu WaTa’ala Ya wadatar da al’umma da shi na tsare shari’a a qarqashin kowaxanne mutanen ilimi kamar ilimin Alqur’ani da na hadisi da furu’a da makamantansu? Da haka, ai Allah Subhanahu WaTa’ala Ya hutar da al’umma daga buqatar wani mutum xaya a cikin wannan nauyi.

  5. Idan har tsare alfarmar shari’a da karantar da ita ba ya yiwuwa sai ga mutum xaya, kuma ma'asumi. To, ai shi wancan da kuke jiran bayyanarsa yau shekarunsa fiye da 460 yake a voye, bai karantar da kowa wani abu na shari’a ba. A tsawon waxannan shekaru wane ne ya karantar da ku Alqur’ani da tarihin Annabi da hukunce-hukuncen da ya zo da su? Idan kun ce: Mun sami gaba xayan waxannan ilimoma ne ta hanyar abin da muka gada na kunne ya girma kaka. To, kenan kun yarda kunne ya girmi kaka na iya tabbatarwa da tsare alfarmar shari’a da karantar da ita gaba xaya. Al’ummar Annabi kuwa ta samu komai na shari’a ta mafi ingancin hanyoyin da kunne ya girmi kaka. Ba ta buqatar ma’asumanku.

  6. Me kuke nufi da yankewar wahayi da kasawar Alqur’ani da Sunnah a kan yin bayani dalla-dalla? Kuna nufin bayanin hukunce-hukuncen qananan abubuwa? Koko manyan da ke da dangantaka ta qud-da-qud da su? Ai ba wani zance na shugaba da ya wuce irin wannan matsayi. A duk lokacin da shugaba zai yi wani zance da mutane, dole ne ya yi shi a sigar ta gama gari don ya haxe matsayinsu na taro. Ba abu ne mai yiwuwa gare shi ba ya kevance aikin da kowa zai yi a xaixaice a kowane lokaci, da kevantattar magana ba. To, ina laifin Manzon Allah don ya yi irin wannan? Kuma ina laifin Alqur’ani? Wannan shi ne kasawa? In ko kuna nufin Manzon ya kasa furta dukkan kalaman da ake buqata, to, babu wanda yake iya yin su, don shi ne mafi cikar girma a kan duk wani Imami da za ku kawo.

  7. Allah Ta’ala Ya riga ya gaya mana cewa:

ﭽ ﮖ ﮗ ﮘ ﮙ ﮚ ﮛ ﮜ ﮝ ﮞﮟ ﭼ إبراهيم: ٤

Kuma ba mu aika wani Manzo ba face da harshen mutanensa, domin ya bayyana masu (14:4)

Ya kuma ce:

ﭽ ﮁ ﮂ ﮃ ﮄ ﮅ ﮆ ﮇ ﮈﮉ ﭼ النساء: ١٦٥

Domin kada wata hujja ta kasance ga mutane a kan Allah bayan (zuwan) Manzanni (4:165)

Kuma Ya ce:

ﭽ ﭥ ﭦ ﭧ ﭨ ﭩ ﭪ ﭫ ﭼ النور: ٥٤

Kuma babu abin da yake a kan Manzo face iyarwa bayyananna (24:54).

Da waxansu ayoyi masu kama da waxannan.

To, a nan sai mu ce: Shin bayanin da Manzo ya yi wa halitta ya isa hujja a kansu ko bai isa ba?

Cewa bayanin nasa bai isa hujja ba, na tabbatar da manufar wanda ya ce haka; na nufin ayoyin ba su karva sunansu ba. Idan kuwa muka aminta da cewa bayanin nasu ya isa hujja, to, ba a da buqatar da wani bakanike, wanda mutane za su yi qishirwar bayaninsa, balle kiyaye alfarmar karantarwarsa. Hasali ma irin baiwar da Allah ya yi wa mutane ta qarfin basirar hardacewa da karantar da zantukan Manzon Allah, da bayaninsa, ta wadatar a wannan fage. Kuma ga shi Allah ya yi alkawarin kiyaye alfarmar abin da ya saukar na wahayi, ta yadda ba a iya canza komai ko qara shi a cikinsa.

A taqaice wannan iqirari da waxannan hasararrun mutane ke yi, na cewa addinin musulunci ba zai kai gaci ba, balle a fahimce shi, sai da sa hannun wani mutum kevantacce, ita ce varna mafi girma da wani zai iya yi wa asalin addini. Duk kuwa wanda zai faxi irin wannan magana, tattare da kuma ya san abin da yake sakamakonta, to, babu shakka zindiqi ne, kuma mulhidi, wanda ke nufin yamutsa hazon addini. Kuma duk wanda ake riwaitowa tare da yayata irin maganar daga bakinsa, to jahilci da vacewarsa sun wuce min-sharrin.


  1. Yau da kullum ta tilasta wa mafi yawan musulmi sanin cewa, fiye da kashi casa’in cikin xari na wannan al’umma sun sadu da saqonnin Alqur’ani da Sunna ne ba ta hanyar Ali ba. Domin kuwa a lokacin da Umar Raliyallahu Anhu ya ci birane da yaqi, ya tura wasu Sahabbai a matsayi malamai zuwa Sham da Iraqi don su karantar da jama’a su kuma wayar masu da kai. Kuma ta hanyar mutanen waxannan garuruwa ne ilimi ya bazu a cikin duniyar musulunci. Abin da Allah Ya hukunci Ali Raliyallahu Anhu da isarwa ga musulmi na ilimi bai fi wanda xan Mas’udu da xan Jabalu da takwarorinsu suka isar ba. Wannan magana kuwa da nake gaya maka sananna ce a duniya. Kuma da za a tsaya ga iyakar abin da shi Ali Raliyallahu Anhu ya faxa na addini, da an wayi gari yau addini sai gida-gida. Duk abin da aka riwaito daga Ali, ba wani mai yawa ne ba, idan ana zancen addini gaba xaya. Kuma ko wannan xan kaxan ma bai iso ma al’umma ta hanya mutawatira ba. Kuma ga shi a wannan zamani namu babu wani ma'asumi, balle mu koma gare shi don tantance riwayoyin, sai Malam-na-Voye da kuke cewa. ‘Yan Shi’ah dai kun ji kunya in kun san ta.

3.4 Wai Dole ne a Samu Shugaba Ma’asumi!

Xan Shi’ar ya ce: Abu na huxu: Haqiqa Allah mai iko ne a kan samar da shugaba ma'asumi, kuma halin da duniya ke ciki na nuna buqatar haka. Yin haka kuwa ba wata varna ba ce. Saboda haka samar da shi ta wajabta. Kuma kan malamai ya haxu a kan cewa, duk wani wanda ba Ali ba, bai cancanci wannan matsayi ba. Kenan babu yadda za a kauce wa kasancewarsa wannan shugaba. Ba kuma abin da ya rage. Domin ikon Allah a kan haka ya bayyana. Kuma buqatuwa ga hakan ta bayyana, saboda rikice-rikicen da ke faruwa a duniya. Ta kuma bayyana cewa babu wata varna a cikin yin haka, domin da an fahimci akwai ta, da buqatar samar da shi xin ta kau. Shi kuwa wajabcin samar da shi ya tabbata ne saboda, da zarar iko da buqata sun tabbata, abin da zai iya kuma yi masu shamaki ya kau, to aiki ya wajaba.



Martani:

Wannan magana tasa ta ginu ne a kan yarda da ijma’i. Mun kuma riga mun tabbatar da cewa, da zarar ijma’i ya tabbata a matsayinsa na ma'asumi, to al’umma ba ta da buqatar da Ali Raliyallahu Anhu ya kasance ma'asumi. Kamar yadda idan ma'asumancin bai samu ga ijma’in ba, to, duk wani dalili da za a kafa da shi a kan kasancewar Ali ma'asumi ba karvavve ba ne. Ka ga da haka kenan gaba xayan fuskokin biyu sun yi duhu.

Wani abun mamaki ma shi ne irin yadda ‘yan Shi’ar nan ke kodayaushe, qoqarin kafa hujja a kan duk abin da suke iqirari, da Nassi da Ijma’i. Sai ka ji suna cewa: Akwai nassi ko kan malami ya haxu a kan kaza. Alhali kuwa su ne mafi nisan mutane daga sanin nassosa da wuraren da kanun malamai suka haxu, da yadda ake kafa hujja da su. Savanin Ahlus-Sunnahti Wal-jama’ah. Waxanda sunansu ma kawai na nuna irin yadda sha’aninsu ke tsattsage da nassosa ingantattu da magana da harshe xaya in sun fi su dubu (Ijma’i). ka ga ashe kenan idan ana neman masu biyar Nassi da Ijma’i sau da qafa, da zarar an same su, magana ta qare, mai zuwa Makka ya haxu da Annabi.

Bari mu koma ga wancan iqirari nasu, mu yi bayanin dalilan da suka sa muke ganin sun vace a cikinsa, ta fuskoki kamar haka:



Yüklə 2,75 Mb.

Dostları ilə paylaş:
1   ...   27   28   29   30   31   32   33   34   ...   51




Verilənlər bazası müəlliflik hüququ ilə müdafiə olunur ©muhaz.org 2024
rəhbərliyinə müraciət

gir | qeydiyyatdan keç
    Ana səhifə


yükləyin