Mawallafi Dr. Abd Ar-Rahman bin Abd Al-Kareem Ash-Sheha



Yüklə 241,3 Kb.
səhifə12/29
tarix05.01.2022
ölçüsü241,3 Kb.
#66966
1   ...   8   9   10   11   12   13   14   15   ...   29
GIDAN LAHIRA:

muminan da suka gasgata manzannin su kuma suka raya lokutan su cikin biyayya ga Allah kuma sukabi umurnin sa sannan kuma suka nesanci abubuwan dayayi hani dasu zasu shiga aljanna ma'anbociya ni'ima wacce take cike da bubuwan na ni'ima wanda ido baitaba ganin suba sannan kunne bait aba jin suba zuciya ma bata taba tunanin suba zasu tabbata cikin wannan rayuwa har abada kamar yadda Allah ya fad cewa: " a cikinta suna da abubuwan da duk sukayi marmari suna masu dawwama acikinta, ya kasance alkawari akan ubangijin ka abun tambaya (16) suratul furkan.

Zasu rika ci da sha a cikinta basazu yi datti ba ko wari sannan kuma bazasu rika yin fitsari ba da bayan gida da majina ba, abun da sukaci zai rika fita ne ta hanyar gyatsa da zufa me kamshi kamar miski, babu rashin lafiya ko annoba, me kira zai kirasu yana ce masu ku zauna a cikinta kuna masu lafiya bazakuyi rashin lafiya ba har Abadan sannan zaku rayu babu mutuwa a cikinta har Abadan sannan zaku kasance samari a cikinta har Abadan bazaku tsufa ba, kuma za'a ta baku ni'ima a cikinta bazaku taba shan wahala ba har Abadan, kamar yadda manzon Allah s.a.w ya bada labara. Muslim ne ya rawaito hadisin.

Su kuma kafirai wanda suka rika karyata wa da jayayya da manzannin su da abunda sukazo dashi suna cikin wuta zasu dawwama acikinta, Allah madaukaki yana cewa: " wanda suka kafirta suna da wutan jahannama bazasu mutu ba a cikinta sannan kuma baza'a sassauta masu abazarta ba, da haka ne muke sakama duk wanda ya kafurta (36) zasu rika ihu a cikinta suna cewa ya ubangijin mu ka fitar damu zamuyi aikin kwarai ba irin wanda muka aikata ba abaya, shin bamu rayaku ba tsawon lokaci da wanda zayyi tunani yakeyin tunani a ciki sannan kuma masu gargadi sun zo maku, ku dandana azzalumai basu da wani mataimaki (37)" suratu fadir. Suna cikin azaba wacce bata yankewa, Allah madaukaki yace: " lallai wanda suka kafirta da ayoyin mu da annu zamu jiyar dasu wuta, duk lokacin da fatarsu ta zagwanye da wuta zamu sake masu wata fatar sabuwa domin su dandani azaba, lallai Allah ya kasance mabuwayi me hikima (56)" suratun nsa'i.

Abincin su a cikinta shine kaya wacce ake kira da suna (dari'u) itace mafiya muni cikin nau'o'in kaya, Allah madaukaki yace: " basu da wani abinci face kayar dari'u, bata sanya kiba sannan kuma bata gusar da yunwa (6)" suratul jasiya.

Da kuma bishiyar zakkum wacce take fita daga cikin wutan hajim wacce da za'a saukar da reshenta guda daya duniya da ta bata masu kayayyakin rayuwan s, Allah madaukaki yace: " lallai bishiyan zakkum, abincin masu sabo ne kafirai, kamar mai ce wacce take zagwanyar da kayan ciki saboda zafinta" (suratul dukkan ayata 43-46).

Ruwan kurji da zufa da jinin dake fita daga namar su shine abinshan yan wuta, Allah madaukaki yana cewa: " basu da wani mai taimakon a ranan ko abincin sai ruwan kurji babu wanda ke cin wannan abinci sai kafirai (suratu hakkah ayata 35-37).

Ruwan shansu kuma shine ruwa me tsanannin zafi wanda yake tsunka hanji da zagwanye fatar jikin su, Allah madaukaki yace: " za'a shayar dasu da ruwa me tsananin zafi wanda zai tsunka masu makoshin su" suratu Muhammad ayata 15.

Tufafin su kuwa a cikin wuta anyi shi ne da dalma na wuta an dinka masu shi kamar yadda Allah ya bayyana haka cikin fadin sa: " wanda suka kafirta an dinka masu kaya daga wuta, za'a rika zuba masu ruwa me tsananin zafi daga kawunan su (19) zata rika tsuntsunka masu kayan cikin su da zagwanar masu da fatar jikin su (20) sannan kuma suna da kuraku na karfe (21) duk lokacin da suka so fita daga cikinta saboda tsananin bakin ciki sai a dawo dasu ace masu ku dandani azabar wutar da kuke karyatawa (22)" suratul hajji.

Daganan ne rayuwan ta hakika zata fara a gidan da ake dawwama da tabbata har Abadan babu mutuwa, manzon Allah s.a.w yace: " idan aka shigar da yan aljanna cikin aljanna, aka shigar da yan wuta cikin wuta sai me kira yayi kira yace: yaku mutanen aljanna ku dawwama acikinta babu mutuwa, yaku mutanen wuta ku dawwama acikin ta kuma babu mutuwa" sahihul buhari, sannan kuma tirmizi ya rawaito shi da Ibn hibban kuma wannan lafazin nashi ne.

Mutum me hankali shine wanda yake aiki tukuru domin ya tsira a wannan rana sai ya fara yima kansa hisabi yaga cewa yana kan tafarki na gaskiya da addinin na gaskiya ko kuma a'a?, Allah madaukaki yace: " lallai Allah baya zalumtar mutane da komai sai dai mutane su suke zalumtar kawunan su (44)" suratu yunus.




Yüklə 241,3 Kb.

Dostları ilə paylaş:
1   ...   8   9   10   11   12   13   14   15   ...   29




Verilənlər bazası müəlliflik hüququ ilə müdafiə olunur ©muhaz.org 2024
rəhbərliyinə müraciət

gir | qeydiyyatdan keç
    Ana səhifə


yükləyin