Tafarkin sunnah


Garin Neman Qiba an Samo Rama



Yüklə 2,75 Mb.
səhifə16/51
tarix28.10.2017
ölçüsü2,75 Mb.
#17506
1   ...   12   13   14   15   16   17   18   19   ...   51

2.10 Garin Neman Qiba an Samo Rama

A qoqarin ‘Yan Shi’ah na ganin jikinsu yafi na musulmin duniya yin vul-vul, sai gashi sunfi kowa rama, wanda hakan ta sa mazahabarsu zama cibiyar vata da varnace-varnace. Bari kaji..

Xan Shi’ar ya ce: Muna son masu hankali da su sa idon basira su gane mana waxanda sukafi cancanta da amincin Allah, tsakanin waxanda su ka tsarkake Allah da mala’ikunsa da Annabawansa da imamansa. Suka kuma tsarkake shari’ar sa daga duk wata qazanta. Da waxanda suka vata sallar su sanadiyar qin yin salati ga imaman da Allah ya zavar masu. Suka koma suna ambaton imaman wasunsu, shin waxannan ne suka fi ko waxanda suka tsaya kan zavin Allah suka watsar da wanin sa?

Kaji tambayar mutumin naka!

Martaninmu a nan shi ne: qoqarin da kuka yi na kore wa Allah Ta’ala waxancan siffofi na kamala, waxanda suka hada da: Rayuwa, ilimi, qudura, magana, cikakken iko, so, qi, yarda da fushi. Sai ka ce Allah yafi qarfin waxannan siffofi balle ya siffanta da su. Kuma wai za’ayi su dace dashi tunda sandararrun abubuwa da siffofi ma na da su?.

To ku sani wannan ba wani abin mazan gwari ne ba. Nakkasa alqaxarin Ubangiji ne da Annabawansa kuka yi. Kuma zance ne kuka yi irin na jahamiyawa. Waxanda ke cewa: Tsarkake Allah daga kama da wanin sa, na wajabta kore waxancan siffofi daga gare shi. A kan haka sukace Allah Ta’ala ba ya da rai, jahili ne, kasasshe, kurma, kadar kasuwa. Bai so bai qi, bai yarda bai fushi. Ba a ganin sa, kuma ba ya da hannu a cikin komai. Kuma a karansa, ba ya iya sukkuna komai.

To ka ga haka, sun kamanta Allah da sandararrun abubuwa nakkasassu;

adai dai lokacin da suka kore masa siffofin cika da kamala. Ka ga kenan

wannan ba tsarkakewa ce ba. Qazantawa ce da gurguntawa.

Abin da ake cewa tsarkakewa a wannan babi, shi ne: kore wa Allah duk wata naqasa da ke takin saqara da wata siffa ta kammala ta yarda ba ta yiwuwa su sha innuwa xaya. Wato a kore masa: mutuwa, da angaje, balle barci. A kore masa: kasawa, jahilci, da bukata, kamar yadda ya kore wa kansa su a cikin littafinsa. Wato a lokaci xaya, tabbatar masa da duk wata siffa ta kamala, tare da kore masa kishiyoyinsu; na naqasa. A kuma tsarkake shi da ga yin kama da wani abu daga cikin halittarsa, ta kowace fuska, tare da kore masa duk wata naqasa, ba tare da iyakancewa ba. Haka kuma a tsarkake shi daga yin kama da wani abu a cikin waxancan siffofi da aka tabbatar masa na kamala.

Wannan kenan. Ta vangaren Annabawa kuma, sai aka wayi gari kun kore masu abin da Allah Ta’ala ya tabbatar masu na kamala da xaukakar daraja. Waxanda ke samuwa garesu ta hanyar tuba da neman gafara. Wanda hakan ke xaukaka darajar su ninkin-ba-ninkin. Da wannan mugun aiki naku, sai aka wayi gari kun qaryata abin da Allah Ta’ala ya fadawa duniya ta wannan fuska; kuka canza wa tuwo suna. Kuka ce wai ciratar xan Adamu daga duniyar jahilai da vata da zalunci zuwa ta ilimi da shiriya da adalci, naqasa ne gare shi.

Kun jahilci kasancewar haka wata ni’ima da qudura mafiya girma daga wurin Allah. A inda yake xaukaka darajar wasu bayi nasa daga matakin naqasa zuwa na kamala. Ta yadda xayan su zai iya kasancewa mai iko akan xanxana alheri da sharri, da tantance banbancin su. Har a wayi gari son da yake na ganin alheri ya tabbata, sharri ya gushe, ya shafe na wanda alheri kawai ya sani. Kamar yadda Umar xan Haxxabi Radiyallahu Anhu ya ce: Ba za a iya yi wa musulunci sukuwar salla, a yi wa xan mansa dai dai ba. Sai an wayi gari al’umma ta haifi wanda bai son komai na jahiliyya ba.

Wannan kenan.Shi kuwa zancen tsarkake imamai, wani abu ne na kunya da bai kamata mai hankali ya fada ba,musaman ixan akayi la’akari da wancan imamin mai taken “Malam Babu”,wanda baya da wani amfani duniya da lahira.

Haka kuma zancen tsarkake shari’ah daga qazanta da qasqanci, wani abu ne tuni an riga an rufe littafinsa. Domin kuwa bayani ya riga ya gabata akan cewa a cikin mas’alolin da Ahlus-Sunnah suka yi ittifaqi a kansu a matsayin shari’ah, babu xaya da keda ko da amon qazanta balle qasqanci. Savanin ’yan Shi’ah waxanda mazahabarsu ke maqil da qazantattu kuma qasqantattun mas’aloli irin waxanda ba mai su a duniyar musulunci.

Bari kuma mu koma ga cewar da ya yi:.........ko waxanda su ka bata sallarsu sakamakon qin yin salati ga imaman da Allah ya zabar masu. Suka koma suna ambaton imaman wasunsu.

To, a nan xayan biyu. Ko dai ya kasance xan Shi’ar na nufin yi wa imamai goma sha biyunan nasu salati wajibi ne. Koko a’a, wajibi dai ne a yi wa wani kevantacce daga cikinsu, ko kuma wani can baqon haure; wanda dai ba Annabi Sallalahu Alaihi Wasallama ba. Ko kuma ya kasance yana nufin yin salati ga mutanen gidan Annabi Sallalahu Alaihi Wasallama kacokwan wajibi ne.

Idan xan Shi’ar na nufin fassara ta farko, to, ko shakka babu hakan ta tabbatar da kasancewarsu kwatarnen vata da varna, da yi wa shari’ar Muhammadu Sallalahu Alaihi Wasallama tawaye. Domin kuwa da mu da su babu wanda tilas ba ta sa ya san cewa Annabi Sallalahu Alaihi Wasallama bai umurci musulmi ya yi wa wani daga cikin imaman nasu goma sha biyu salati ba, daxa ko a cikin sallah ne ko wajen ta. Kuma babu wani musulmi ma da aka samu yana aikata haka a zamaninsa. Babu kuma wanda ya riwaito haka daga Annabi Sallalahu Alaihi Wasallama, ta hanya ingantatta ko mai rauni. Kai! Hasali ma ba wajibi bane a kan wani musulmi ya riki xaya daga cikin imaman goma sha biyu shugaba, alhali ga Annabi raye, balle har yi masa salati acikin sallah ya zama wajibi.

Duk kuwa wanda ya ce yi wa waxannan imamai salati cikin sallah wajibi ne, har kuma ya vata sallar wanda bai yi haka ba, to ya canza alqiblar addinin MuhammaduSallalahu Alaihi Wasallama ya mayar da shi wani abu, kamar yadda Yahudawa da nasara suka sauyawa addinin Annabawansu fasali.Wannan abun da ‘yan Shi’ah ke qoqarin tabbatarwa, baya tabbatuwa. Domin kuwa sallar da musulmi suka yi zamanin rayuwar Annabi, ingantattace bisa haxuwar kan al’umma tabbas. Tattare kuma da rashin yin salati ga imaman a cikinta.

Idan kuwa xan Shi’ar ya ce a’a muna nufin fassara ta biyu ne, wato wajabcin yin salati wa mutanen gidan su Annabi Sallalahu Alaihi Wasallama saboda matsayin da suke da shi.

To, sai mu ce masu: Mutanen gidan su Annabi yawa ne da su. Matansa kaf, da gaba xayan banu Hashim, har ma da banu Abdul-muddalibi, a bisa wani zance, duk Ahlun-nabiyi ne. Kuma Shi’ah imamayya ba su ganin mafi yawan waxannan bayin Allah da gashi a kai. Domin a wurin su abbasiyyawa ba kowa ba ne. Musamman halifofi daga cikinsu. Ga shi kuwa suna daga cikin Ahlu Muhammadin. Haka kuma suna sukar lamarin duk wanda ya yarda da shugabancin Abubakar da Umar Radiyallahu Anhum. Ga shi kuma mafi rinjayen banu Hashim sun yarda da shugabancinsu, Duk wanda yake xan halas daga gidan Hashim yana tare da Abubakar da Umar Raliyallahu Anhumam sai fa ‘yan qwarori. Amma in ban da su, duk wani ma’abuci ilimi da kishin addini a wannan gida baya qyamar Abubakar da Umar Raliyallahu Anhumam.

Babban abin ban mamaki ko ince ban ta kaici da waxannan ‘‘yan Shi’ah, duk bai fi tattare da irin tinqahon da suke yi na so, da girmama mutanen gidansu Annabi Sallahu Alaihi Wasallama. Sai gashi kuma sune a gaba, a lokacin da Tatar suka far wa bagadaza, Hedikwatar Hilafar musulunci a lokacin. Su dai ‘yan Shi’ah nan sune suka yi masu jagora suka salwantar da rayukan musulmi Hashimawa. Waxannan Allah ne ka xai yasan adadinsu, balle daxa waxanda ba su ba. Suka kuma kashe kusan mutum dubu xari da goma sha takwas da xari tara da saba’in a cikin sasannin Bagadazar. Suka kuma kashe Halifan lokacin, Ba abbase. Suka ribace mata da kananan yaran Hashimawa; Aka hada kan ‘yan matan Hashimawa da wasunsu duk aka kai wa Yazidu da takwarorinsa sarakuna. Duk haka ta farune da taimakon ‘rafelawa.

Ka ko ga babu wata qiyayya da za’a nuna wa Alu Muhammadin Sallalahu Alaihi Wasallama wadda ta kai haka. Ko shakka babu.

Kai! In ta kaice maka labari, babu wani abu da ‘yan Shi’ah za su soki lamirin wani da shi, a wannan babi, face hakan tafi cancanta da su ,nesa ba kusa ba.
2.11 Na Gaba ya yi Gaba

Xan Shi’ar ya yi qoqarin karkata akalar wasu darajoji na Sayyidina Ali, tare da kafa hujja dasu, don tabbatar da fifiko da imamancinsa. Ga abin da yake cewa:

Abu na shida: Ai ba da banza jama’ar Shi’ah ‘yan-sha-biyu suka zavi Sayyidina Ali a matsayin shugaba abin yi wa da’a ba gare su, sun yi haka ne saboda ganin irin darajoji da martabobin da basu qidayuwa. Waxanda masoya da magabatansa su ka riwaito, waxanda kuma ke tabbatar da kasancewarsa xan goma.

Bayan wannan kuma sun ga iri aibubban da wai junansu su ka riwaito a kan wasu Sahabbai waxanda yawansu ya zarta hankali amma ba su samo aibi ko xaya ta a kan sayyidina Ali. To wai a kan haka ne su ka sakakance da babu wanda ya cancanci saurarawa da shiga gaban sahu sai shi, wai saboda ya sami shedar tsarki daga bakin masoya da maqiya.

Sun kuma yi watsi da duk wanda ba shi ba, saboda ganin waxanda ma suka yarda da shugabancin nasa, sunyi masa raxan-raxan ta hanyar riwaito abun kunya a kansa. Wanda hakan ke hana shugabancinsa karvar sunansa a shari’a.

Xan Shi’ar ya ci gaba da cewa, kuma yanzu za mu ambaci kaxan daga cikin darajojin Alin, waxanda suka inganta a wurin Ahlus-Sunnah. Domin kuwa littafai da zantukan da suka aminta tare da dogara a kansu duk sun naqalto su. Za mu kuma yi haka ne, don ta zama hujja a kansu ranar alkiyama. Inji shi.

Daga cikin waxannan darajoji akwai abin da Abul-Hasan Al-Andalusi ya riwaito a cikin littafin: Al-jam’u Bainas-sihahis-sitta, da: Muwaxxa Maliku, da ingantattun littafan Buhari da Muslimu, da sunanu Abu Dawuda, da sahihu Tirmizi, sahihu Nisa’i, daga Ummu–Salmata matar Annabi Sallalahu Alaihi Wasallama wadda tace: Ayar da Allah Ta’ala ke cewa: Allah na nufin ya tafiyar da kazanta kawai daga gareku, ya ku mutanen babban Gida! kuma ya tsarkake ku, tsarkakewa.(33:33) ta sauka ne ga Manzon Allah Sallalahu Alaihi Wasallama a lokacin da yake xakinta. Ta ce: a lokacin ina zaune daura da kofa. Sai na ce ya Manzon Allah! ina fatar dai ni ma ina daga cikin mutanen gidanka xin nan, sai ya karva mata da cewar: Anya? Ina dai yi maki fatar alheri ki na dai daga cikin matar Annabin Allah. Taci gaba da cewa: A lokacin da wannan abu ke faruwa, Ali da Fatima da Hassan da Husaini Radiyallahu Anhum duk suna cikin xakin nawa. Sai kuwa ma’aiki ya yafa masu mayafinsa, ya ce: Ya Ubangiji waxannan su ne mutanen gidana. Allah ka tafiyar da kazanta daga garesu, ka kuma tsarkake su tsarkakewa.

To abin da za mu gayawa wannan xan Shi’ar a matsayin martani, a kan wannan magana shi ne: Na farko dai ya sani, Nagaba ya yi gaba. Domin kuwa darajojin halifa Abubakar da Umar Radiyallahu Anhum waxanda suka tabbata a cikin ingantattun hadisai, sun fi waxanda suka tabbata na darajojin halifa Ali Radiyallahu Anhu yawa da kabri.

Kuma waxannan hadisai da ya ambata. Ya ce kuma suna kunshe a cikin ingantattun littafan hadisan Jumhurun musulmi, kuma wai amintattun littafai da zantukan su duk sun nakalto su, qarya ce yake yi wa Jumhurun. Domin kuwa masana ilimin hadisi sun yi ititfaqi a kan kasancewar mafi yawan waxancan hadisai da ya ambata qarya, ko masu rauni. Su ku wa waxanda suka inganta daga cikinsu ba su xauke da wani abu da ke nuna imamancin Ali, ko fifikon darajar sa a kan Abubakar da Umar. Hasalima bai kevanta da darajojin da hadisan suka qunsa ba; ya dai yi tarayya da wasu ne daga cikinsu. Savanin darajojin da suka tabbata na Abubakar da Umar Raliyallahu Anhu waxanda babu wanda ya yi tarayya da su, a cikin mafi yawan su. Musamman ma dai Abubakar Raliyallahu Anhu wanda bai yi tarayya da kowa ba a cikin gaba xayan darajojin da ya kevanta da su.

Su kuwa abubuwan kunyar da ya ce an riwaito na waxannan halifofi uku, wai ya sani sun fi qarfin haka. Idan ma har wani abu ne, sai dai a ambace shi “qorafi”. Amma ba abin kunya ba. Sannan kuma, babu wani qorafi da za’ayi kan su, face akwai kwatankwacin sa ko wanda ya fi shi, da za’a iya yi kan Ali Raliyallahu Anhu.

Ka ga da haka, ta tabbata duk abin da ya faxa a wannan fasali kar ya ce cas. Nan gaba kaxan kuma za mu tona asirinsa a kan haka, dalla-dalla, in Allah ya so.

Wannan kenan, idan kuma ba ka manta ba, xan Shi’ar ya ce wai: Shi’ah ‘yan-sha-biyu sun riki imamu Ali shugaba a gare su. Saboda ganin irin yadda masoya da magabata suka yi masa wankan tsarki, tare kuma dayin biris da duk wanda ba shi ba. Saboda kasancewar har waxanda ma suka yarda da shugabancinsu nada qaiqayi a zukatan su a kansu.

To, kafin muje ko ina, muna tabbatar wa ‘yan Shi’ah cewa wannan magana qarya ce. Domin kuwa waxanda ba su yarda da Ali Raliyallahu Anhu ba, su ne kan gaba wajen sukar sa. Hasali ma yawan QungIyoyin da ke sukar lamirin sa su ne mafiya rinjaye, idan akayi la’akari da masu qorafe-qorafe a kan Abubakar da Umar da Usmanu Raliyallahu Anhu da kuma waxanda suka wuce wurin cikin girmama Alin kansa; wato “Gulatu”.

Ka ga dai tumun fari, Harijawa sun yi ittifaqi a kan kasancewar Ali kafiri. Wai Kuma duk da haka sun fi Gulatu daraja a idon musulmin qwarai; saboda su Gulatun, a wurinsu Sayyidina Ali Allah ne. Sukan kuma sassafta wani lokaci su ajiye shi matsayin Annabi.

Ba wannan kawai ba. Jamhurun musulmi sun fi ganin Harijawa da sauran Sahabban da suka shaya daga da Ali tare da su, da gashi aka, a kan ‘‘yan Shi’ah masu aqidar biyar imamai goma sha biyu. Waxanda ke kan aqidar kasancewar Alin imami ma’asumi.

Wani abun kuma da zai qara tabbatar wa ka da irin yadda halifofin can uku na kafin Ali, suka yi masa fintinqau a wannan fage, shi ne irin gaba xayan al’ummar Amada ke saka masu bakin albarka, idan ka cire ‘yan Shi’ah la’anannu. Duk da kuwa Harijawan can da ke kafirta Ali Raliyallahu Anhu da Marwaniyawa da suka xauke shi matsayin wani qasurgumin azzalumi. Suka kuma sa qafa sukayi fatali da halifancinsa. Duk waxannan mutane sun yarda da shugabancin Abubakar da Umar, har ma da na Usman Raliyallahu Anhu tare da zama qarqashin tutocinsu, tattare kuwa da kasancewar babu zumunci a tsakaninsu da su ko na anini. To, ta yaya za a ce wai masoya da magabata su yi wa Ali Raliyallahu Anhu wankan tsarki, tare da yin kunnen uwar shegu da waxancan halifofin uku. Alhali kuwa wannan ingantattar magana da muka fada ta cika kunnen duniya?

Haka kuwa tabbataccen abu ne cewa mutanen da ke sa wa waxancan halifofi uku bakin albarka daga cikin wannan al’umma, su ne mafi yawa da girman daraja a cikinta. Su kuwa masu yi wa Ali Raliyallahu Anhu kwarar vawan kalgo, ta hanyar naxa masa rawanin kafirci da fasiqanci da varna, qungiyoyi ne sanannu kuma tantantattu. Amma kuma tattare da ha akan sun yi wa ‘‘yan Shi’ah ko-ta-kwana a fagen ilimi da kishin addini, da qarfin tuwo. Ko alama ‘‘yan Shi’ah ba su kai su ba a wannan fage. Balle su yanke su da takobin hujja ta hankali da basira, ko su goga a kaifunsu a kan fandun dutse ranar fama.

Kuma kasan wani abu? Babu qungiya xaya daga cikin qungiyoyin can da ke kafirta Ali ko ganinsa azzalumi, da aka sheda da wani aiki na ridda. Savanin waxanda ke kuxa da kwarzanta shi tare da sukar lamirin waxancan duwatsu guda uku na daular musulunci. Wato kamar Nusairiyya (Al-Galiyah) waxanda ke jin shi Allah ne. Da Isma’iliyah (Al-Mulhidah) waxanda har gwamma Nasiriyya da su. Da kuma Galiya, waxanda ke jin shi Annabi ne. Duk waxannan qungiyoyi kafirai ne murtaddai. Bisa shaidar Allah da Manzonsa da duk wani malamin musulunci na gari.

Ko shakka babu duk wanda ke da masaniya da addinin musulunci komai qanqantarta, ba ya musun kafirci duk wanda ya naxawa wani mutum rawanin ubangizantaka. Ko ya yi imani da wani Annabi bayan muhammadu Sallallahu Alaihi Wasallama koko a’a anabcin ba nasa ba ne, na Aliyu ne mala’ika Jibrilu ya kai masa a kan kuskure.

Haka kuma ba ya musun musulncin Harijawa. Waxanda ke kafirta

Ali Raliyallahu Anhuda la’antarsa. Da kuma na waxanda suka yaqe shi suka kuma la’ance shi daga cikin Sahabban Mu’awiyah da Bani Marwanu da wasunsu. Waxannan mutanen gaba xayan su musulmi ne. Domin sun yarda da musuluncin da shari’o’insa; suna salla, suna azumi, suna zakka, suna hajji. Suna kuma haramta duk abin da Allah da Manzonsa suka haramta. Babu mutum xaya daga cikinsu wanda kafircin sa ya bayyana. Duk wanda ya san tarihin musulunci ya san waxannan mutane na matuqar girmama musulunci da shari’o’insa.

Ka ga hakan ta tabbatar mana da cewa,cewar da xan Shi’ar ya yi wai gaba xayan magabata sunyi wa Sayyidina Ali wankan tsarki, savanin waxancan halifofi uku, qarya ce kawai.


2.13 Hadisin Mayafi ba Hujja ba ne

Shi kuwa hadisin mayafi ko shakka babu ingantacce ne. Domin kuwa Ahmada da Tirmizi sun riwaito shi da ga cikin hadisan Ummu Salma. Haka kuma Muslimu ya riwaito shi a cikin ingantaccen littafinsa, daga cikin hadissan Aisha, wadda tace: Watarana da hantsi Annabi Sallallahu Alaihi Wasallam ya fita yafe da wani mayafi mai faxi na baqin gashi. Sai ga Hasan xan Ali ya iso, sai ya gayyace shi ciki. Sai kuma ga Husaini ya iso,shi ma ya gayyaceshi, sai kuma ga Fatima ta iso, ita ma ya gayyace ta, qarshe kuma sai ga Ali ya iso, shi ma ya gayyace shi ciki. Sannan ya ce: Allah na nufin kawai ya tafiyar da qazanta kawai daga gare ku ya ku mutanen Babban Gida! Kuma ya tsarkakeku tsarkakewa (33:33).

Abin da muka son tabbatarwa anan shi ne,wannan hadisi tattare da ingancinsa, ba ya zama hujja akan imamancin Ali,kamar yadda xan Shi’ar ke qoqarin tabbatarwa.

Dalininmu shi ne: Kasancewar ba Ali kawai Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallam ya gayyata a cikin mayafin ba,balle ace ya gayyaci Fatima, Hassan da Husaini, ka kuwa san mace bata shugabanci, ka ga kenan wannan falalar bata nufin tabbatar da lasisin shugabanci ga waxannan mutane.A’a abu ne da wasu keda hakki a kansa.

Iyakar fassarar da wannan hadisi ke iya xauka itace: Annabi Sallallahu Alaihi Wasallam ya roi Allah ya tafiyar da kasanta daga waxannan mutane, ya kuma tsarkake su tsarkakewa. Wato su zama mutane masu tsoron Allah a dalilin tsarkin can da tsarkakewa.

Shi kuwa nisantar qazanta da Allah ya yi alkawali abu a kan kowane mumini, kamar yadda aka ambaci gaba xayan mumine da tsarki. Dubi abin da Allah ke cewa: Allah baya nufin domin ya sanya wani kunci a kanku kuma amma yana nufin domin ya tsarkake ku, ya kuma cika ni’aimar sa a kanku (5:6).

A wata ayar kuma ya ce: Ku karvi sadaka da dukiyoyinsu kana mai tsarkake su, sanan kana mai tabbatar da kirkinsu. (9:103).

A wata ayar kuma ya ce: Haqiqa, Allah yana son masu tuba, kuma yana son tsarkakewa (2:222).

To, ka ga iyakar abin da wanan hadisin ke nufi, shi ne Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama ya roi Allah Subhanahu Wa Ta’ala akan aikata alheri da nisantar sharri, Amma ba imamanci ba.

Ka kuwa ba afi Abubakar siddiqu Raliyallahu Anhu ba a fagen aikata alhairi. Tun da har Allah Ta’ala ya bayar da labarinsa da cewa, shi mafi taqawa ne wanda yake bayar da dukiyarsa, alhali yana tsarkaka. Alhali babu wani mai wata ni’ima wurinsa wanda ake neman sakamakonta. Face dai neman yardar Ubangijinsa mafi xaukaka. To, lalle ne zai yarda (da sakamakon da za a ba shi) (92:17-21).

Haka kuma cewar da Allah ya yi: Kuma masu tserewa na farko daga Muhajirun da Ansar da waxanda suka bisu da kyautatawa, Allah ya yarda daga gare su, kuma ya yi masu tattalin gidajen aljanna: qoramu suna guxana a qarqashinsu. Suna madawwama a cikinsu har abada. Wancan ne babban rabo mai girma (9:100) na tabbatar da cewa waxannan bayin Allah sun tsaya tsayin daka akan aikata abin da Allah ya yi horo dashi, da nisan tar abin da Allah ya yi hani da shi. Domin sai da haka ne suke iya samun wannan sakamako na yar dar Allah.

Ka ga kena a haka, kanfa, kazantar da samun cikakken tsarki daga zunubi sun zama daga cikin siffofin su. Kuma sun yi tarayya da mutanen can huxu (ahlul baiti) a cikin wancan bakandamin du’a’i da Annabi Sallallahu Alaihi Wasallam ya yi masu.

Ba wannan ma ka wai ba, tarihi ya tabbatar da cewa akwai mutane da dama; ba waxancan huxun ba. Waxanda Manzon Allah ya roi Allah ya yi salati a kansu. Ya kuma rokar wa wasu masu yawa aljanna da gafarar allah da wasu muhimman abubuwa daba waxannan ba. Waxanda suka fi waccan du’a’i girma. Amma kuma hakan ba ta wajabta zaman waxanda ya yi wa du’a’in na biyu mafiya girma a kan sabikunal auwaluna.

Kuma dalilin da ya sa Annabi Sallallahu Alaihi Wasallam ya yi wa Ahlul- kisa’i wannan du’a’i, shi ne kasancewar nisantar qazanta da zankake wajibi a kansu. Saboda haka ya roi Allah ya taimakesu a kan tabbatar da haka. Don kada kashinsu ya bushe; su wayi gari ana Allah waddai da su, kuma cikin azaba.

Wannan du’a’i da Annabi ya yi masu, da kasancewarsa karvabbe a wurin Allah, zai sa waxannan mutane su zama abin madalla da lulluvewa da rahama.
2.13 Tilas Mai Hawan Ruwa ya yi Babban Masaki
Xan Shi’ar ya yi qoqarin kafa hujja a kan fifikon darajar Ali Raliyallahu Anhu da imamancinsa, da ayar da Allah Ta’ala ke cewa a cikin ta:

ﭽ ﭑ ﭒ ﭓ ﭔ ﭕ ﭖ ﭗ ﭘ ﭙ ﭚ ﭛﭜ ﭝ ﭞ ﭟ ﭠﭡ ﭢ ﭣ ﭤ ﭥ ﭦ ﭧ ﭨ ﭩ ﭼ المجادلة: ١٢



Ya ku waxanda suka yi imani! Idan za ku ganawa da Manzon Allah, to ku gabatar da ‘yar sadaka(58:12)

Xan Shi’ar ya kafa hujja da cewa, Sarkin Musulmi Ali xan Abu Xalib Raliyallahu Anhu ya ce: Babu wanda ya yi aiki da wannan aya daga cikin Sahabbai sai ni. Kuma albarkaci na ne Allah ya sassautawa wannan al’umma al’amarin wannan aya.


Martani:

Ya kamata xan Shi’ar ya fahimta cewa wannan ummarni da Allah Subhanahu Wata’ala ya yi, na gabatar da wata ‘yar sadaka don gana wa da manzon. Bai zama wajibi a kan kowane musulmi ba. Balle wanda bai yi ba yayi laifi. Wajabcin ya ta kaita ne a kan wanda lalurar ganawa da manzo ta kama. To, kuma sai akayi sa’a, a lokacin da wannan ayar ta sauka Ali Raliyallahu Anhu ne kawai wannan bukatar ta ganawa da manzo ta kama. Bai kuma yi wata-wata ba sai ya gabatar da sadakar. Kamar yadda dai malamai suka yi ittifaqi.

Ka ga kenan, wannan ummarni dai- dai yake da ummarnin da Allah ya yi da yanka hadaya, ga wanda ya hada hancin aikin hajji da na umara lokaci xaya. Ko kuma wanda aka datse.
2.14 Ayar:

ﭽ ﯓ ﯔ ﯕ ﯖ ﯗ ﯘ ﯙ ﭼ التوبة: ١٩

Xan Shi’ar ya ce an samo daga Muhammad xan ka’abu al-kwrari, wanda ya ce: Watarana Xalhatu xan Shaibata; xan Bani Abdud-xari, da Abbas xan Abdulmuddalibi, da Aliyu xan Abu xalib sun yi musanyyar alfahri wa junansu wai. Na farkon ya ce: In na ga dama sai in buxe Ka’aba in kwana ciki tun da a hannuna mabuxanta suke. Na biyun kuma ya ce: Ni kuma tunda ni ke shayar da Alhazzai ruwa, in na so sai in kwana a cikin masallacin. Shi kuwa na ukun, wato Sayyidina Ali, wai sai ya ce: To duk kusaurara. Ni nayi malinku. Don na share tsawon wata shida ina fuskantar Ka’abar ina sallah, kafin kowa ya yi. Kuma nine Antaru sarkin yaqin Manzon.

Wai rufe bakunan su keda wuya sai Allah ya saukar da ayar da ke cewa:



Shin kun sanya shayar da mahajjata da ruwar da masallaci mai alfarma kamar wanda ya yi imani da Allah da ranar lahira, kuma ya yi jihadi a cikin hanyar Allah? Ba su dai-dai ta a wurin Allah. Kuma Allah ba ya shayar da mutane azzalumai( 9:19).
Martani:

Martanimu a kan wannan magana shi ne: Wannan hadisi dai qarya ne. Domin babu wani littafi daga cikin littafan hadisi da ya zo da shi. Kuma kayan cikin hadisin na daxa tabbatar da haka. Bari ka ji:

Mutumen can na farko da xan Shi’ar ya ambata; wato Xalhatu xan Shaibatu, babu shi a cikin kundin tarihin musulunci. Shaibatu xan Usmanu xan Xalhatu shi ne wanda aka sani mai hidimar xakin Ka’aba. Ka ga wannan kawai ya isa tabbatar da rashin ingancin hadisin.

Sannan cewar da ya yi wai xan Abbas ya ce: in na ga dama sai in kwana a cikin masallacin (Ka’aba) To, xan saurari wannan magana da kyau. Ka kuma tambayi kanka, wace daraja ce kega wanda ya kwana a cikin masallacin Ka’aba, balle har ya kafa wa wani hujja da shi?

Haka kuma cewar da ya yi Ali Raliyallahu Anhu wai ya ce: Na share wata shidda ina fuskantar Ka’abar ina sallah kafin kowa.

Wannan magana ce da babu mai musun kasancewarta karya. Domin kuwa tarihi ya tabbatar da cewa tsakanin musuluntarsa da ta Zaidu da Abubakar da Khadijah Raliyallahu Anhu bai fi kwana xaya ba ko qasa ga hakan ba. To ya ya za’a ce ya riga kowa sallah da wata shiddah? Ko a ce ya ce shi ne gishirin yakokan Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama Tunda tare da dubban mutane akayi su, ba shi kadai ba?


Yüklə 2,75 Mb.

Dostları ilə paylaş:
1   ...   12   13   14   15   16   17   18   19   ...   51




Verilənlər bazası müəlliflik hüququ ilə müdafiə olunur ©muhaz.org 2024
rəhbərliyinə müraciət

gir | qeydiyyatdan keç
    Ana səhifə


yükləyin