Tafarkin sunnah



Yüklə 2,75 Mb.
səhifə3/51
tarix28.10.2017
ölçüsü2,75 Mb.
#17506
1   2   3   4   5   6   7   8   9   ...   51

RAYUWAR IBNU TAIMIYYAH1

Wane ne Ibnu Taimiyyah?

Sunansa Ahmad xan Abdulhalimu xan Abdussalami xan Abdullahi xan Haliru xan Muhammadu xan Haliru xan Aliyu xan Abdullahi. Ya shahara da sunan Ibnu Taimiyyah saboda kakarsa da ake kira Taimiyyah. Ana kuma ce ma sa “Majduddini”. Sannan ana ce ma sa “Numairi” saboda shi xan qabilar Banu Numairi ne. Ana ce ma sa kuma “Harrani” saboda Harrana ne garin da aka haife shi. Sannan ana ce ma sa “Dimashqi” saboda a garin Dimashqa ne ya girma, ya yi karatu.



Asalinsa

Ibnu Taimiyyah xan asalin qasar Turkiyyah ne. Don an haife shi a garin Harrana wadda take arewa maso gabascin qasar ta Turkiyyah. An haife shi ne a ranar litinin 10 ga watan Rabi’ul Awwal 661H. Amma bayan shekaru shida sai iyayensa suka yi hijira daga qasar zuwa qasar Siriya in da suka sauka a babban birnin Dimashqa, hedikwatar Sham. Dalilin hijirar tasu kuwa shi ne kauce ma fitinar ‘yan Tattar waxanda suka auka ma garuruwan musulmi suka yawaita varna da zubar da jinainan bayin Allah ba li ba la.

Game da mahaifansa kuwa, shi xan gidan malanta ne. Domin ya sami kansa a tsakanin iyaye da kakanni da ‘yan’uwa ma’abuta karatu. A lokacin da zasu yi hijira kuwa babu abin da ya wahalar da su kamar littafai da ke tare da su masu xinbin yawa, ga su kuma suna gudun maqiya. Ba domin kiyayewar Allah ba ma ba zasu tsira da rayukansu zuwa Sham ba.

Isarsu qasar Sham ke da wuya mahaifin Ibnu Taimiyyah Shihabuddini ya fara koyarwa da wa’azi a babban masallacin Jum’ah na Dimashqa wanda ake kira Al-Jami’ul A’azam masallaci mafi girma. Daman shi fitaccen malamin furu’a ne a mazahabar Hambaliyyah. Nan take aka shugabantar da shi ga babbar makarantar hadisin nan da aka sani Darul Hadis As-Sukkariyyah, aka kuma ba shi gida a cikin makarantar in da nan ne xansa Ibnu Taimiyyah ya girma.

Kafin haka, kakan Ibnu Taimiyyah Majduddini sanannen malami ne da ya yi wallafe-wallafe a fannin hadisi da Usulul Fiqhi. Shi ne mawallafin littafin nan na Muntaqal Akhbar wanda Imamus Shaukani ya yi wa sharhi a cikin Naulul Auxar.

Haka ma baffansa Fakhruddini, malami ne fitacce da ya wallafa babban littafin Tafsirin Alqur’ani. Shi ne kuma wanda ya gaji Ibnul Jauzi a kujerarsa ta karantarwa da babban mimbarinsa na Bagadaza. Kuma Ibnu Taimiyyah ya yi karatu a wurinsa.



Tashinsa da Iliminsa

Ibnu Taimiyyah ya tashi a gidan ilimi kamar yadda muka gani. Ya kammala hardar Alqur’ani a cikin quruciya. Sannan ya kula da sanin ilimoman Fiqihu da Hadisi da Tafsiri da Arabiyyah. Ya soma karantarwa da fatawa da rubuta littafai da tattaunawa da malamai Munazara tun bai wuce shekaru ashirin ba. Koda ya cika shekaru talatin an fara yi masa laqabin Mujtahidi kuma “Mai raya Sunnah”.

Yana da matuqar wuya a iya sifaita baiwar da Allah ya yi wa Ibnu Taimiyyah ta fuskar ilimi. Masu ba da labarinsa na ganin kasawarsu wajen bayyana irin hikimomin da ke tattare da shi ta wannan haujin. An lisafta malaman da ya gurfana a gabansu don xaukar karatu aka tarar sun zarce malamai xari biyu. Akwai kuma littafan da ya karanta su sau da yawa a wurare daban-daban kamar Musnad na Imamu Ahmad.

Game da nasa littafai shi kuma, Ibnu Taimiyyah ya wallafa sama da littafai hamsin a fannona daban-daban na addini, banda qananan wallafe-wallafensa da aka tara cikin Majmu’ul Fatawa mai sifili talatin da bakwai. Ya ishi mai karatu misali abin al’ajabi cewa, duk da yake Ibnu Taimiyyah bai wallafa Tafsirin Alqur’ani ba, amma malamai daga bisani sun wallafa shi daga cikin littafansa. Ma’ana an tattara wuraren da ya yi sharhi akan ayoyin Alqur’ani daga cikin littafansa a tsakankanin maganganunsa da kafa hujjojinsa, sai ga shi an samu kusan kammalallen Tafsiri mai Mujalladi huxu.


Mujaddadi Ibnu Taimiyyah

Muna iya cewa, Allah gwanin sarki ya tashi Ibnu Taimiyyah ne a wani lokaci da buqatar irinsa ta yawaita. Don kuwa a wancan lokaci al’umma tana fama da matsaloli da rikitta da tashin hankula na ciki da na waje. Daga cikin gida musulmi na fama da rabuwar kai, da yawaitar qungiyoyi da yaxuwar bidi’ah da raunin ilimin furu’a. Ga kuma lalacin da ya yaxu a cikin jama’a da zaluncin sarakuna da kwaxayin malamai. Tsibbace-tsibbace da bokanci da duba sun zama gama-gari a cikin al’umma. Daga waje kuma ‘yan mishan sun kai ma musulmi farmaki, ‘yan Shi’ah masu kiran kansu Faximawa sun haxa kai da su. Sannan ga Tattar sun shelanta mummunan faxa da musulunci da musulmi a duk in da suke a wancan lokaci.

Shaihun musulunci ya fuskanci duka waxannan matsaloli da nufin magance su. Ya kuma samu taimakon Allah matuqa a wajen cimma wannan gurin nasa. Ga shi kuma Allah ya ba shi makamai da ya wuyata a samu wanda ya yi tarayya da shi a dukansu. Mutum ne da aka sifaita shi da kaifin basira da qarfin qwaqwalwa, har wasu ma na ganin bai tava sanin abu ya manta da shi ba. Yana da qarfin tuna ayoyin Alqur’ani da nassosan hadissai da maganganun malamai na kowane fanni. Don haka ya kasance mai kaifin hujja wadda take yanke wuyan abokin gaba nan take. Ga shi kuma jarumi da ba ya tsoron ko-ta-kwana. Don haka ba ya da ja da baya ga abin da ya sa gaba. Sannan yana da kwarjini a idon jama’a da kyawawan xabi’u da suka daxa soyar da shi ga mutane. Ga shi mutum mai kishin gaskiya da qoqarin yaxa ta. Haxa da halinsa na gudun duniya da rashin kula da jin daxinta. Irin wannan malami Allah ya xora shi a kan kyakkyawar hanya irin ta Annabawa wane irin canji kake tsammanin al’umma ba za ta ci moriyarsa ba ta hanyarsa?

Xan Taimiyyah nan take ya rurrusa aqidun da suka zame ma musulunci tsutsar goro ta hanyar rubuce-rubucensa da wa’azozansa da karantarwarsa. Ya kece raini a wajen wargaza aqidun Yahudawa da na ‘Yan mishan. Ya yi faxa da qungiyoyi mabiyan son zuciya irin mulhidai da zindiqai da ‘yan Shi’ah da waxanda suka wuce wuri a Sufanci. Ya yi kira ga koma ma littafin Allah da Sunnar Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama ba tare da ta’assubanci ga wani mutum ko qungiya ko mazhaba ba.

Sa’annan ya kira sarakuna da talakawa zuwa ga yaqar kafirai waxanda suka keta hurumin musulmi, musamman dai Tattar. Ya kuma fita ya yi yaqi a matsayin xaya daga cikin sojoji.

Tare da haka kuma Ibnu Taimiyyah ya kafa wata makaranta da Allah ya yawaita almajiranta tun daga wancan zamani har zuwa yau, kuma tana ci gaba da bunqasa har a naxe qasa. Wannan makaranta tasa tana mutunta magabatan Sahabbai da Tabi’ai da waxanda suka biyo bayansu, da shugabannin mazhabobi, tana kuma la’akari da ra’ayoyansu da fatawoyinsu baki xaya. Tana kuma rinjayar da nassi ingantacce idan ya zo daga Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama a kan maganar kowa kome darajarsa. Wannan makaranta dai tana da xaruruwan littafai da dubaiban malamai a cikinta. Dukkaninsu suna jingina kansu ga Sunnah da biyar magabata ba ga shi Ibnu Taimiyyah xin ba.


Jarabawar Da Ibnu Taimiyyah ya Gamu da Ita

Yana da wuya Allah ya xaukaka wani bawansa ba tare da ya gamu da wasu jarabawoyi ba a rayuwarsa. Wannan ita ce sunnar Allah ga Annabawa da malamai mutanen kirki.

Shehun musulunci ya gamu da jarabawoyi da dama a sakamakon jihadinsa na makami da na alqalami waxanda suka dagula ma sa jin daxin rayuwa. Zamu faxi wasu daga cikinsu a taqaice kamar yadda suka zo a tarihinsa daga littattafai da dama.

A shekarar 696H ya gamu da qyashin abokan tafiya, malamai, waxanda suka xauki littafinsa Al-Fatwal Hamawiyyah suka kai qararsa da shi a wurin mahukunta. Sun bi duk hanyoyin da suke iyawa wajen murxa maganarsa da ba ta irin ma’anar da suke so su jingina ma sa. A wannan lokaci sarki Saifuddin Jagan ya goyi bayan Ibnu Taimiyyah, ya kuma husata da waxanda suka kafa adawa da shi. Don haka wannan jarrabawa ba ta daxe ba ta kuranye.

A shekarar 705H lokacin da farin jinin Ibnu Taimiyyah ya gama bayyana, bayan an ga rawar da ya taka a yaqin da aka yi da Tattar, har kuma ya samu kusanci da hukuma abin da ya ba shi damar sa a kawar da wasu varnace-varnace. Nan take sai qurjin hasada ya sake vallewa a zukatan wasu malamai daga cikin sufaye. Sai wani malami da ake kira Nasrul Mambiji da wani malami bamalike ana ce ma sa Ibnu Makhluf suka tafi hedikwatar sarauta da ke qasar Masar suka kai qarar Ibnu Taimiyyah suna tuhumar sa da gurvata aqidun jama’a. Suka kafa hujja da littafinsa na Al-Aqidatul Wasixiyyah. A nan ma sarki ya ba da umurni aka zaunar da shi tare da manyan malamai in da aka karance littafin nasa, daga qarshe kuma aka barrantar da shi daga sava ma magabata. Sai ma a wannan karon ya samu takardar yabo daga Sarkin Musulmi.

Wata xaya bayan faruwar wannan, sai waxannan malaman suka sa sarki ya rubuta ma sa wata takarda ana neman sa da zuwa Misra don ya bayyana a gaban sarki. A wannan karon da tuhumar yana neman sarauta! An dai zaunar da shi a gaban Ibnu Makhluf don ya yanke ma sa hukunci, abin da xan Taimiyyan ya qi yarda da shi, kasancewar shi ne abokin husumar da ya kai qararsa. Shehul Islami sai da ya share wata goma sha biyu cur a gidan kaso kafin a nemi ya fita, in da shi kuma ya qi fita ya ce, sai an bayyana ma sa laifinsa. Daga qarshe ya fita daga kurkukun bayan ya cika wata goma sha biyar da sati biyu bisa ga nacewar wani basaraken garinsu.

Wata bakwai bayan fitowarsa sai aka sake mayar da shi a cikin watan Shawwal na 707H saboda ya ci gaba da zama a Masar mutane na amfana da shi. A wannan karon sai ya kasance mutane suna tururuwa a gidan kaso don gaishe shi da yin fatawa a wurinsa, abin da ya daxa cinna wutar gaba a tsakaninsa da waxanda ke biyar sa da baqar yadiya.

Bayan fitowarsa ma, xan Taimiyyah bai fasa abin da yake yi na karantarwa da fallasa miyagun aqidu ba. Wannan ya sa aka xauke shi daga Alqahira zuwa Iskandariyyah da nufin ya haxu da ‘yan dabar garin su kashe shi. Ana haka ne sai aka samu canjin gwamnati lokacin da sarki Muhammad xan Qalawun ya sake koma ma kujerar sarauta sai ya mayar da Shehul Islami zuwa hedikwatar ta Masar. Daga nan kuma suka fita a shekarar 712H da nufin yaqar kafiran Tattar, sai Allah ya mayar da maqiyan garuruwansu ba tare da an yi yaqi ba. Don haka, sai Ibnu Taimiyyah ya koma gida Sham, in da ya haxu da tarbo wanda ba a tava ganin irinsa ba, bayan ya yi shekara bakwai da sati bakwai a qasar Masar tun wancan kiran da aka yi ma sa.

Ko bayan komawarsa gida Shehul Islami ya ci gaba da samun matsaloli da malamai masu qaramin sani da taurin kai. Kamar yadda suka yi cah a kansa wai don ya ce, in mutum ya yi rantsuwar saki kaffara kawai zai yi, aurensa na nan. Haka ma don cewar da ya yi saki uku na komawa xaya idan an yi su zama guda. Waxannan malamai ba su samu sukuni ba sai da suka sa aka hana shi fatawa a shekarar 719H.

A shekara ta 720H aka sake iza qeyar babban malamin zuwa gidan kaso in da ya share wata biyar da kwana goma sha takwas.

A shekara ta 726H wasu alqalai sun tsoma bakinsu a cikin rikicin Ibnu Taimiyyah da maqiyansa, in da aka wallafa wata fatawa ta qarya aka jingina ta gare shi, wai ya haramta ziyarar qabarin Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama da na sauran Annabawa. Alhalin shi kuwa ya rarrabe tsakanin ziyararsu ne ita kaxai da kuma haxa ta da yin tafiyayya. Ya labarta savanin magabata a kanta, sannan ya nuna karkata ga hanawa idan ya kasance an yi tafiyayya saboda ita. Ya kuma bayyana hujjojinsa na ingantattun hadissai. Wannan rikicin ma dai sai da ya sake mayar da wannan bawan Allah a gidan maza, in da ya samu damar da ya yawaita wallafe-wallafe gami da bautar Allah Ta’ala.

A shekara ta 728H aka fitar da duk littafan da ke tare da shi da alqalumma da tawadar da aka samu a wurinsa, saboda wani malami da ake kira Ikhna’i ya kai qarar sa, don ya yi ma sa raddi, kuma wai ya jahiltar da shi. A nan ya zama dole Ibnu Taimiyyah ya haqura ya duqufa ga zikiri da sallah da karatun Alqur’ani da yake waxannan suna a kansa tun zamanin quruciya.


Rasuwarsa

Allah ya karvi ransa a gidan maza na birnin Dimashqa yana da shekaru 67 waxanda suke cike da karantarwa da haquri da jihadi. Ya rasu kafin wayuwar garin litinin 20 ga watan Zul Qi’ida 728H.

Bai yi aure ba ballantana ya bar zuri’a. Bai kuma tava furta kalima xaya da take nuna rashin sha’awarsa ga auren ba. To, ko me ya hana shi cin moriyar wannan Sunnah? Sanin gaibu sai Allah.
Littafan da Aka Duba Don ba da Tarihinsa

Al’Uqudud Durriyyati Min Manaqibi Shaihil Islami Ibni Taimiyyati na Muhammad xan Ahmad xan Abdulhadi, tahaqiqin Muhammad Hamid Al-Faqi, bugun Darul Katib Al-Arabi.

Al’A’alamul Aliyyati na Bazzar, tahaqiqin Zuhair Shawish, bugun Al-Maktabul Islami, Beirut, Lebanon.

A’ayanul Asri na Ibnu Aibak As-Safadi, tahaqiqin Ali Abu Zaidah da wasu, bugun Darul Fikri, Beirut, Lebanon.

Ad-Durar Al-Kaminatu Fi A’ayanil Mi’ati As-Saminti, na Hafiz Ibnu Hajar Al-Asqalani, tahaqiqin Sayyid Jad Alhaq, bugun Jami’ar Ummul Qura, makka, Saudi Arabia.

Buhus An-Nadwatil Alamiyyati An Shaihil Islami Ibni Taimiyyati, tahaqiqin Muqtada Hasan, bugun Dar As-Sami’i.

Da’awatu Shaikhil Islami Ibni Taimiyyata Wa Asaruha Fil Harakatil Islamiyyatil Mu’asirati, na Salahuddin Maqbul, bugun Majma’ul Buhusil Ilmiyyati, New Delhi, India 1412H/1992M.

Dhailu Xabaqatil Hanabilati, na Hafiz Ibnu Rajab Al-Hambali, tahaqiqin Muhammad Hamid Al-Faqi, bugun Darul Ma’arifati, Beirut, Lebanon.

Shajaratuz- Zahab Fi Akhbari Man Zahab, na Ibnul Imadi Al-Hambali, bugun Darul Fikri, Beirut, Lebanon.

Shaikhul Islami Wa Juhuduhu Fi Ilmil Hadis, na Firiwa’i, bugun Darul Asimati.

Husulul Ma’amul Min Kalami Shaikhil Islami Ibni Taimiyyata Fi Ilmil Usul, na Abdurrahman xan Abdullahi Al-Amir, bugun Darul Waxan, Riyadh, Saudi Arabia, 1423H/2002M.

Ibnu Taimiyyah: Hayatuhu Wa Asruhu, na Imam Muhammad Abu Zuhrata, bugun darul Fikril Arabi, Alqahira, masar. 1898H/1974M.
Godiya

Wannan aiki ya xauki tsawon shekaru da dama, amma a wannan shekara da muke cikinta ta Hijirar 1429 ya daxa kankama sosai. Kuma a tsakkiyar aikin ne Allah ya karvi xaya daga cikin masu himma a aikin, shi ne Dr. Ibrahim Bello wanda ya ba da lokacinsa da kuzarinsa sosai don ganin nasarar aikin, sai dai ajali ya riske shi tun bai ko gama kabbarar harama a cikin aikin ba. Muna roqon Allah ya isar da ladarsa ta wannan aikin don ta zamo haske a cikin qabarinsa, ya kuma tara mu da shi a Darus-Salami.

Ya zama tilas a kan wannan cibiya bayan godiya ga Allah, ta yi kevantacciyar godiya ga kwamitin da ya yi aikin na fassara, musamman sakatarensa Alhaji Aliyu Rufa’i wanda himmarsa a aikin ta zarce ta kowa. Ya kuma ba da gudunmawa mai tarin yawa a wajen fassarar ita kanta, sannan ya taimaka ainun a wajen bitar da ta share sama da watanni uku. Haka kuma qwarewarsa a sanin qa’idojin rubutun Hausa ta taimaka mana matuqa. Ba mu da wata sakayya a gare shi sai addu’a; Allah ya sa aikin ya zamo sanadin tsira. Sai kuma Mal. Aminu Ibrahim Maru da Sheikh Usman Sarkin Vurmin Jabo waxanda da su ne aka aza harsashin aikin tun da farko. Muna roqon Allah ya yi musu sakayya kyakkyawa.

Sai cibiyar fassara da take Runjin Sambo a qarqashin jagorancin Dr. Tahir Muhammad Argungu. Su ma muna godiya a kan nasu qoqari.

Gudunmawar masu saka aikin a cikin na’ura mai qwaqwalwa ita ma ba abar mantawa ce ba. Waxannan sun haxa da Al-Irshad Computers na Mal. Aminu Mustafa Digar Agyare da Aliyu Kambaza Business Centre da ke kan titin Amir Yahaya duk a nan Sokoto.

A can kuma qasar Masar in da aka buga littafin Alhaji Uba Ahmad Ibrahim, wakilin gidan rediyon doce-belle ne ya yi tsaye don ganin aikin ya tafi daidai bisa haruffan Hausa, da kuma daidaita ayoyin Alqur’ani bisa haruffan xab’i na birnin Madina. Allah ya saka ma su ga baki xaya da mafificin alherinsa.

Wannan gabatarwa ba za ta kammala ba sai mun miqa godiya ga jagororin wannan Cibiya da waxanda ke taimaka ma ta ta fuskoki daban-daban. Allah ya ba kowa ladar qoqarinsa, ya kuma xora mu bisa shiriya a cikin zantukanmu da ayyukanmu.

Daga qarshe ina miqa godiya tare da yabawa ga uwargidana Mamar Mu’azzam a kan bitar da ta yi wa littafin daga bisani, da gyare-gyaren da ta yi masu ma’ana.1

Allah ya daxa tsira da aminci ga shugabanmu Muhammadu da iyalansa da Sahabbansa baki xaya. Alhamdu Lillah.

Baban Ramlatu,

Muhammad Mansur Ibrahim

Sokoto.


24 ga Rajab 1429H (26-07-2008M)
GABATARWAR SHEIKH GUNAIMAN

Wanda Ya Taqaita Littafin

Yabo da godiya Sun tabbata ga Allah Mai girma, mai rinjayar da gaskiya a kan qarya, wanda ya ce:

ﭽ ﮒ ﮓ ﮔ ﮕ ﮖ ﮗ ﮘ ﮙ ﮚﮛ ﮜ ﮝ ﮞ ﮟ ﮠ ﭼ الأنبياء: ١٨

A’a, muna jefa gaskiya a kan qarya, sai (qarya) ta koma halakakka. Kuma bone ya tabbata a gare ku saboda abin da kuke Siffantawa1.

ﭽ ﮙ ﮚ ﮛ ﮜ ﮝﮞ ﮟ ﮠ ﮡ ﮢ ﮣ ﭼ الإسراء: ٨١



Kuma ka ce: “Gaskiya ta zo, kuma qarya ta lalace. Haqiqa, qarya ta kasance lalatacciya.2

ﭽ ﭑ ﭒ ﭓ ﭔ ﭕ ﭖ ﭗ ﭘ ﭙ ﭼ سبأ: ٤٩



Ka ce, “Gaskiya ta zo, kuma qarya, ba ta iya fara (kome). Kuma ba ta iya mayarwa3

Ina gode masa, godiya mai albarka. Ina shedawa babu abin bauta da cancanta sai Allah shi kaxai ba ya da abokin tarayya. Kuma Annabi Muhammadu bawansa ne, Manzonsa. Ya aiko shi da shirIya da addini na gaskiya don ya rinjayar da shi a kan sauran addinai. Ko maqiya sun qi ko sun so.

Bayan haka, babu shakka, wannan littafi Minhajus Sunnah na daga cikin manyan Littafan da shahararren malamin nan Ahmadu xan Abdulhalimi xan Abdussalami, wanda aka fi sani da “Ibnu Taimiyyah” ya wallafa, wanda a cikinsa ya xaura sirdin fafata yaqi da qarya, ya tarwatsa gungun maqaryata da karnukan farautarsu, ya kuma taimaki gaskiya. Wannan shi ya qarfafa buqatar da ke akwai musamman ga matasa musulmi, da su tunkari wannan littafi don cin moriyar abin da ya qunsa.

Wannan bukata ta fi qarfafa a wannan lokaci, inda annobar Shi’ah ta barbazu, ta kai caffa a wasu garuruwan musulmi. A wasu wuraren ma, ta yaga ta ciza, ta saki dafinta. Ta yaudari waxanda suka jahilci lamarinta, ta hanyar shigar burtu. Babu Shakka wannan littafe waraka ne ga wanda ya kamu da rashin lafiyar Shi’ah.

Wani abin al’ajabi shi ne, inda za ka taras da cewa, dukan qungiyoyin bidi’ah, vacewarsu ba ta yi zurfin ta mabiya Shi’ah ba, waxanda ke tinqaho da ci gaban sarkin baka. Kullum suna qara kutsawa cikin duhun dajin vata, amma suna ganin sun fi kowa shiriya, bayan suna yaqar masoyan Allah da Manzonsa. Littafansu sun cika har sun batse da zage-zage da la’antar manya-manyan bayin Allah; ba su kunyar kafirta manyan Sahabbai irinsu Abubakar da Umar da Usmanu Allah ya yarda da su ballantana qananansu. Sun kuma yi haka ne kawai saboda Sahabban nan sun bice wutar tsafi, suka rugurguza gumakan Farisa.

Duk wanda ya buxe shafukan littafan ‘yan Shi’ah, zai ga yadda suka cika su fal da riwayoyin kafirta Sahabbai Raliyallahu Anhum. Su a wajensu yin haka ya zama tamkar ibada, har ma suna raya cewa wanda bai shiga sahunsu ba, ya zama abincin wuta. A cikin Littafinsu Al Wafi sun ce, wai, Allah ba zai karvi aikin wanda ba mabiyi Shi’ah ba, kome kyawon sa. Haka kuma a wani Littafi Alkafi mai muhimanci ainun a wurinsu, sun bayyana baqar adawarsu ga musulunci, da ma wanda ya zo da musuluncin gaba xaya.

A wautar mabiya Shi’ah, sun ce, Allah ya saukar da Alqur’ani ne domin ya bayyana abubuwa guda biyu kawai. Na farko shi ne, nuna matsayin Ali Raliyallahu Anhu ta hanyar bayyana darajarsa da ta iyalansa. Na biyu kuma shi ne, aibanta Sahabban Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama da fallasa su. Wannan shi ne ya kai su ga tuhumar cewa, mafi yawan sassan Alqur’ani mai girma sun halaka ta hannun Sahhabai Allah ya yarda da su.

Dukan tunaninsu da harkokin addininsu sun dogara kacokan a kan qarya, wadda suke zuqa ma limamansu. Sun cika shafa wa Sahabban Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama kashin kaji, ta inda har sun jingina su ga munafunci. Sai dai mu, muna sane cewa, sara da sassaqa ba su hana gamji toho. Allah wadaran ‘yan Shi’ah, ya cika su da tsoro, ya kunyata su, gami da ‘yan kanzaginsu.

Kodayake asalin wannan littafi ya qunshi bayanai iri-iri na martani ga masu aqidar Shi’ah da masu kore qaddara da masu falsafa, na zavar wa kaina kevantuwa ga abin da ya shafi Shi’ah kawai, saboda irin kariyar da ke tattare a wannan vangare ga abin da ya shafi tsarin shugabanci, da alfarmar Sahabbai da kuma mutuncin uwayen muminai (Matan Annabi, Sallallahu Alaihi Wasallama).

Ban shigar da kalma ko xaya ba ta qashin kaina a cikin wannan aiki, dalili da cewa, mawallafin littafin (Ibnu Taimiyyah) bai bar wata kafa ta yin haka ba. Ya riga ya xinke shi da hujjoji masu qarfi. Allah ya saka masa da alheri, ya sa mu yi tarayya da shi a cikin ladar wannan gagarumin qoqari nasa, Amin.

Allah shi ne mafificin wanda ake roqo. Tsira da amincin Allah su tabbata ga fiyayyen halitta Muhammadu xan Abdullahi da iyalan gidansa da Sahabbansa.

0.1 GABATARWAR IBNU TAIMIYYAH

Shehul- Islami Ibnu Taimiyyah ya ce:

Yabo da godiya su tabbata ga Allah Mai girma da xaukaka. Wanda Ya ce:

ﭽ ﭾ ﭿ ﮀ ﮁ ﮂ ﮃ ﮄ ﮅ ﮆ ﮇ ﮈ ﮉ ﮊ ﮋ ﮌ ﮍ ﮎ ﮏ ﮐﮑ ﮒ ﮓ ﮔ ﮕ ﮖ ﮗ ﮘ ﮙ ﮚ ﮛ ﮜ ﮝ ﮞﮟ ﮠ ﮡ ﮢ ﮣ ﮤ ﮥ ﮦ ﮧ ﮨ ﮩﮪ ﮫ ﮬ ﮭ ﮮ ﮯ ﮰ ﮱ ﯓ ﭼ البقرة: ٢١٣:



Mutane sun kasance qungiya xaya (a kan gaskiya. Daga bisani sai suka yi savani, wasu suka bi gaskiya, wasu suka bi vata) sai Allah Ya aiki Annabawa suna masu bayar da bishara kuma masu gargaxi. Kuma ya saukar da Littafi da gaskiya tare da su. Domin (Littafin) ya yi hukunci a tsakanin mutane, a cikin abin da suka sava wa juna a ciki; kuma babu waxanda ya sava a cikinsa, face waxanda aka bai wa shi daga bayan hujjoji bayyanannu sun je musu, domin zalunci a tsakanin su. Sai Allah ya shiryar da waxanda suka yi imani ga abin da suka sava a cikinsa na gaskiya da izininsa. Kuma Allah yana shiryar da wanda yake so, zuwa ga hanya madaidaciya1.

Na shaida babu abin bauta da cancanta sai Allah shi kaxai, ba ya da abokin tarayya, kamar yadda ya shedi kansa da cewa;

ﭽ ﭤ ﭥ ﭦ ﭧ ﭨ ﭩ ﭪ ﭫ ﭬ ﭭ ﭮ ﭯﭰ ﭱ ﭲ ﭳ ﭴ ﭵ ﭶ ﭷ ﭼ آل عمران: ١٨

Allah ya sheda cewa, haqiqa, babu abin bautawa da cancanta face shi. Su ma mala’ikku da ma’abuta ilimi sun shedi haka. Yana tsaye da adalci. Babu abin bautawa face shi, mabuwayi, mai hikima.2

Kuma na shaida Annabi Muhammadu bawansa ne, Manzonsa. Cikamakon Annabawa, wanda Allah ya sifanta shi da cewa;

ﭽ ﮬ ﮭ ﮮ ﮯ ﮰ ﮱ ﯓ ﯔ ﯕ ﯖ ﯗ ﯘ ﯙ ﯚ ﯛ ﭼ التوبة: ١٢٨

Haqiqa Manzo daga cikinku ya je muku. Ba ya son duk abin da ke wahalar da ku. Mai kwaxayi ne ga (shiriyar) ku Mai tausayi ne, mai jinqai ga muminai”3

Tsira da amincin Allah su tabbata ga Annabi Sallallahu Alaihi Wasallama.

Bayan haka;

Wasu ‘yan’uwa Ahlus-Sunnah Sun isko ni da littafin Minhajul karamati fi Ma’arifatil Imamati na wani malamin Shi’ah, inda ya ke tallar hajarsa ta Shi’anci, tun ma ba a fadar sarakuna ba.

Littafin ya samu karvuwa ga mafi yawan waxanda ba su fahimci addini ba. Kuma ya samu taimakon qungiyar Shi’ah ta Baxiniyyah, mavarnata. Waxanda suka samo tushe daga malaman falsafar Yahudanci, ta Sabi’awa, waxanda ba su ganin kan kowa da gashi. Sun fanxare ma tafarkin Annabawa, sun juya ma musulunci baya, suka mayar da addini zavi son ka. Ba haka ba ma, lamarin addini a wajensu yana da matsayi irin na jam’iyyar siyasa, wadda a ke da zavin shiga da fita a kowane lokaci. Ita kuwa annabta a idanunsu, wata hanyar holewa ce kawai da kyautata zaman duniya.

Wane mutum! Ire-iren waxannan marubuta fa da daxewa sun watsu a sassa na duniya, inda jahilci ya barbazu sakamakon qamfar malamai masana shari’a, masu tumbuke shukar vata da aka dasa cikin al’umma. Mabiya Shi’ah sun qware wajen lavewa ga sabara su harbi barewa, musamman wajen aqidar qaryata Manzanci a fa kaice. Bugu da qari kuma sun halaka mutane masu ximbin yawa ta hanyar yaudara.

Qungiyoyin Shi’ah da na Jahamiyya su ne manya –manyan qofofin shigowar nau’ukan varna da damfara, musamman waxanda aka shigar cikinsunayen Allah da Siffofinsa da Littafansa. Kamar yadda aka samo tabbacin hakan daga limaman qungiyoyin Karramiyyah da Baxiniyyah da sauran tarkacen zindiqai.

Shi wanda ya kawo min littafin, ya shaida mini cewa, suna amfani ne da littafin wajen yaxa gurvatacciyar aqida, musamman a gidajen masu mulki da masarautu. Za a iya tabbatar da haka, lura da cewa marubucinsa ya rubuta shi ne musamman ya aika shi ga sarki Khudabandah. A nan ne waxanda suka isko ni da littafin suka nemi in yi fashin baqi game da varnar da ke cikinsa. Saboda a ceto bayin Allah a kuma fallasa maqaryata. Sai na amsa musu da cewa, ai wannan littafi hujja ne a wajen masu shi, kodayake a cikin asiri sun jahilci cewa, babu komi cikin sa, sai shirme da maganganu marasa kan gado.

Abin da ya kyautu mu fayyace a nan shi ne, a gane cewa, su dalilai sun rarrabu ne zuwa gida biyu. Akwai dalilai na tsintsar Ilimi kuma akwai na kaifin hankali. Abin kaico shi ne, su mabiya Shi’ah, idan ka lura da ra’ayinsu da kyau za ka san cewa, sun vace vari. Domin sun rasa ilimi da hankali gaba xaya. Sun yi zo-zo zo da waxanda Allah Ya sifanta da cewarsa

Kuma suka ce: “Da mun zamo muna saurare ko muna da hankali da ba mu kasance a cikin ‘yan sa’ira ba.1

Rubuce- rubucensu sun cika sun batse da qissoshi da labaran cin qanzon kurege, ga su kuma da wauta kamar xiyan fari. Sun goge wajen mayar da fari baqi a sashen riwaito hadisi, ba ruwan su da tacewa tsakanin maruwaici maqaryaci da wanda ba shi ba. Ba su dogara da komi ba face zato da an-yi-an-ce. Ga su da biyar ra’ayoyin malamansu a makance. Kuma suna jin cewa, wannan hanya da suke a kai itace a’ala, musamman a fagen kafa dalili. Wannan irin hali shi ya kai su har suka fantsama, suka faxa cikin jerin gwanon Mu’utazilawa da masu kore qaddara. Kamar yadda a wani lokacin kuma sai a tsince su a tashoshin Mujassimah da Jabariyyah. Wani abin al’ajabi da mamaki a nan shi ne, duk da irin zurfin vacewar waxannan qungiyoyi da aka zayyano, ‘yan Shi’ah sun zarce su nesa ba kusa ba a fagen rashin fahimtar lamurra. Wanda hakan ya sa malamai suka haxu a kan cewa, qungiyarsu ta fi kowace qungiya dolanci da jahilci. Sun tafka varnar da Allah ne kawai ya san iyakacinta a cikin al’umma.

Qungiyoyin Isma’iliyyah da Nusairiyyah da Baxiniyyah da Yahudawa da Kirista, manya- manyan arna da zindiqai, duk ta qofar Shi’anci suka samu hanyar barbaza varna a cikin musulunci bayan sun rinjayi wasu garuruwan musulmi, ta hanyar zubar da jini da kwashe dukiyoyinsu. Hasali ma duk qasar musulmin da masifar yaqi ta faxa ma, za ka taras da cewa, hakan ya faru ne bayan qullin qawancen makirci tsakanin kafirai da mabiya Shi’ah. Misalin faruwar irin wannan ba ya lissafuwa a duniya.

Dalilin wannan qazamin qawance nasu, ba ya rasa nasaba da cewa tun asalatan, Shi’ah ta fito ne daga cikin tsatson zindiqai da munafukai, da suka bayyana a zamanin Sarkin Musulmi Aliyu xan Abu Xalib Raliyallahu Anhu. Babbar aniyarsu ita ce faxa da Musulunci. Wannan shi ya sa Aliyu Raliyallahu Anhu ya hanzarta xaukar qwaqqwaran matakin wargaza gungunsu, ta hanyar lallasa musu nau’ukan azaba iri- iri, bayan da ya fahimci cewa, tsawa da gargaxi ba su bishe su. Ya yi amfani da bulala, ya koma yana qona su da wuta. Da lamarinsu ya vaci sai ya zaro takobinsa ya tunkare su cikin hanzari a fusace. Daga nan suka ce, qafa me na ci ban ba ki ba. Suka kama gudu ba waiwaye.

Dalilin da ya sa Sarkin Musulmi Aliyu xan Abu Xalib Allah ya yarda da shi ya xaukar wa mabiya Shi’ah wannan mataki shi ne, saboda faifayewar su a wajen yabonsa, inda suka fifita shi sama da darajar halifa Abubakar Raliyallahu Anhu da Sarkin Musulmi Umar xan Haxxabi Raliyallahu Anhu wanda shi a wajensa bai tava fifita kansa a kan waxannan Sahabbai ba. Abin da ma ya tabbata daga wajensa shi ne, an ji shi da bakinsa yana cewa: “Abubakar ne ya fi kowa girman daraja a cikin wannan al’umma, sannan Umar, in ban da Manzonta”. Imamul Buhari a cikin ingantaccen littafinsa ya riwaito cewa, muhammadu xan Hanafiyya xan Ali Raliyallahu Anhu ya tambayi babansa cewa, wane ne mafifici daga cikin Sahabbai? Sai wancan jawabi ya zama amsa ga wannan tambaya.

Wannan shi ne dalilin da ya sa malaman farko ba su yi savani ba a kan fifikon Abubakar da Umar Raliyallahu Anhuma a kan sauran al’umma. Wajen da suka yi muhawara kawai shi ne, tsakanin Aliyu da Usmanu yardar Allah ta tabbata a gare su, wane ne ba wane ne ba? Abin mamaki wai, kare da tallar tsire, tarihi ya nuna cewa, malaman Shi’ah na farko-farko, kai! har ma da na baya- bayansu an ji su suna fifita Abubakar Raliyallahu Anhu a kan sauran Sahabbai. Abdul Jabbar Al hamadani ya cirato daga littafin Tathbitun Nubuwah cewa; Abul qasim Al balakhi a cikin raddin da ya yi wa xan Rawandi ya ce, wani ya tambayi Shariku xan Abdullahi cewa; wa ya fi matsayi a tsakanin Abubakar da Ali? Sai ya kada baki da hanzari ya ce, Abubakar mana. Sai mai tambayar a cikin mamaki ya ce; “Kai da kanka ke faxin haka?” “To, ina amfanin kusancin ka ga Ali?”. “Ai duk wanda bai yarda da cewa wannan magana haka take ba, to ba shi ba Ali”. in ji Malam Shariku. Ya ci gaba da cewa, na rantse da Allah, watarana na ga Aliyu Raliyallahu Anhu da idanuna ya hau kan mimbari yana huxuba, ya na cewa, ku saurara, ku sani cewa mafi alheri daga cikin wannan al’umma bayan Annabi Sallallahu Alaihi Wasallama shi ne Abubakar sannan Umar yardar Allah ta tabbata a gare su. Kana ganin cewa zai kyautu a yi biris da wannan magana tasa? Na rantse da Allah, Aliyu Raliyallahu Anhu ko alama ba maqaryaci ba ne.


Yüklə 2,75 Mb.

Dostları ilə paylaş:
1   2   3   4   5   6   7   8   9   ...   51




Verilənlər bazası müəlliflik hüququ ilə müdafiə olunur ©muhaz.org 2024
rəhbərliyinə müraciət

gir | qeydiyyatdan keç
    Ana səhifə


yükləyin