Tafarkin sunnah


Shaidar Malamai a Kan ‘Yan Shi’ah



Yüklə 2,75 Mb.
səhifə5/51
tarix28.10.2017
ölçüsü2,75 Mb.
#17506
1   2   3   4   5   6   7   8   9   ...   51

1.4 Shaidar Malamai a Kan ‘Yan Shi’ah

A baya an ambaci wani littafi mai suna Minhajul-Karamati. Amma a haqiqanin gaskiya kamata ya yi sunan nasa ya kasance Minhajun- Nadamati. Domin kuwa nadama littafin ya qunsa ba karama ba. A cikin rubutun, marubucin ya bi sawun malamansa ne a duniyar Shi’ah irin su Mufid da alamjiransa kamar Xusi da ire-irensa.

Irin waxannan rubuce-rubuce na ‘yan-sha-biyu ba abin da ke cikinsu sai qarya, irin wadda ke nuna su a fili, a matsayin manyan-manyan jahilai a sararin Subhana. Taqama kawai suke yi da harkar ilimi da nazari, amma abin ba haka yake ba. A haqiqa, idan kana neman mutane marasa kan gado, ga kuma qarfin hali a fagen qin ba nazari haqqinsa, to, da zarar ka yi kicivis da xayansu, to, haqarka ta cimma ruwa. Duk abin da suka dogara a kansa za ka taras ruvavve ne, da ya kamata a saka kwandon shara.

Malamansu naji da faxi, ba su da hanya qwaqqwara ta karvar riwaya sai ga azurakan mutane irin su: Abu Mikhnaf Luxu xan Yahya da su Kalbi, waxanda ma’abuta ilimi suka bada shedar cewa, shahararrun maqaryata ne su. Masana sirrin riwayoyin hadisi kuma, sun ba da shaidar cewa, ‘yan shi’a na daga cikin manyan maqaryata a duniya.

Malam Razi Baban Hatim ya riwaito daga Malik wanda aka tambaya game da matsayin ‘yan Shi’ah sai ya ce: “Ba a shiga batun su, kashedinka da karvar maganarsu, don gwanayen qarya ne su”. Baban Hatim kuma ya riwaito daga Imamus Shafi’i cewa: “Ban tava ganin maqaryatan mutane irin ‘yan Shi’ah ba”. Shi kuwa mashahurin malamin nan Yazidu xan Haruna cewa ya yi: “Ana iya karvar riwayar kowane xan bidi’a idan ba ya tallar ta, amma banda ‘yan Shi’ah, saboda maqaryata ne”.

Haka shi ma Malam Shariku, alqalin Kufa, wanda ya zauna da su, ya kuma san su sarai, kai, yana ma cikin almajiran sayyidina Ali ga shaidar da ya bayar a kansu: “Ana iya karvar ilimi a wajen kowa banda ‘yan Shi’ah. Saboda sun iya qera hadisan qarya, kuma sun xauki yin ha kan wata hanya ta shiga Aljanna”.

Haka kuma Malam Sulaimanu xan Mahrana wanda aka fi sani da A’amash yana cewa: “Qarya a wajen ‘yan Shi’ah ba bakin komai take ba. Babu mamaki ka ji su suna yaxa cewa sun kama wani malami na Allah da wata, saboda tsabar qazafi”.

Waxannan bayanai babu za’ida a cikinsu. Duba su a cikin Al –Ibanatul–Kubra na Ibnu Baxxata. Shi ma Abul–Qasim Al-Xabari ya riwaito cewa Imamus-Shafi’i ya ce: “Ban ga waxanda suka zarce ‘yan Shi’ah iya qarya ba a duk cikin qungiyoyin bidi’a baki xaya”.

Saqon da ake son a iyar a nan shi ne, malamai na duniya kaf sun fayyace cewa, ‘yan Shi’a su ne limaman maqaryata. Kuma har tinqaho suke yi da wannan matsayi. Suna cewa, mu addininmu duk taqiyyah ne. suna nufin halalta wa kansu fesa qarya a duk sadda suka ga dama. Wannan kuwa ba wani abin mamaki ba ne ga wanda ya san asalinsu.

Tattare da haka kuma sai ka ga suna zungurar magabatan wannan al'umma da cewa wai, gaba xaya sun yi ridda; sun bar lemar Musulunci.

Da 'yan Shi’ah suna da ganewa sun fi kowa cancantar waxannan sifoffin da suke jingina wa zavavvin bayin Allah. Saboda a duk lokacin da mutum ya tashi neman waxanda suke ridda da munafucci da zarar ya ci karo da gungun 'yan Shi’ah haqarsa ta cimma ruwa. Idan kuma a na son gano gaskiyar wannan zance, mutum ya yi nazari, game da rassan Shi’ah irinsu Galiyyah, da Nusairiyyah da Isma'iliyah. Duk wanda ya leqa ciki da wajensu, zai ga abin mamaki, kuma cikinsa zai xuri ruwa, ya juyo a firgice saboda gigita da tsoro game da zurfin tavarvarewar lamarinsu.

A sashen hukunce-hukuncen shari’ah ‘yan Shi’ah suna dogara ne kacokan ga riwayoyi waxanda aka ce an naqalto su ne daga Ahlulbaiti duk da yake mafi yawan riwayoyin na qarya ne. Su kuwa ba su iya tantancewa tsakanin ingantaccen Hadisi daga mai rauni ba. Idan ma an saki kari cewa, Hadisan da ake riwaito masu ingantattu ne, to, ba su kai ga Annabi Sallallahu Alaihi Wasallama ba. Amma sai suka gina wasu harsasai guda uku na shirme don su tabbatar da dacewar su karvi waxannan riwayoyin. Waxannan harsasan sun haxa da; cewa, kowanne daga cikin Ahlulbaiti ma'asumi ne; yana kafaxa-da-kafaxa da Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama. Na biyu kuma wai, duk abin da zai faxi tsararre ne. Na uku kuma duk abin da Ahlulbaiti suka yi ijma'i a kansa ya zama hujja. Kuma faxar xayansu ba ta kasancewa sai in sun yi ijma’i akan abu.

Waxannan abubuwa su ne tubalan da suka gina karvar riwayoyinsu a kai. Idan aka lura da kyau, su, ba su xauki Alqur’ani mai girma da muhimmanci ba, balle ya zama tushen da suke dogara a kansa. Haka ma Hadisi, to, balle kuma ijma'i ko qiyasi.

Maganar hankali da qiyasi a wurin ‘yan Shi’ah yana ta'allaqa ne ga rubuce-rubucen Mu'utazilawa waxanda a wani gefen sun xara 'yan Shi’ah hankali. Abin da ke nuna maka haka, shi ne, mu’utazilawa basu tava yin suka ga halifancin Abubakar da Umar da Usmanu Allah ya yarda da su ba. Magabatansu suna fifita Abubakar da Umar a kan sauran Sahabbai. Su kuwa 'yan bayansu sun kame baki ba su ce komai ba. Amma an samu kaxan da suka fifita Aliyu Raliyallahu Anhu a kan sauran Sahabbai Raliyallahu Anhu a nan ne ra'ayinsu ya zo xaya ba banbanci da na Zaidiyyah tare da cewa ba su yi ja-in-ja ga halifancin waxanda suka gabaci Aliyu xin ba. Harwayau wani sashe na Mu'tazilawa sun yi qawance da Zaidiyyah a gefen maganar Adalci da Imamah da fifita Ali a kan Usman.



1.5 Wai Imamah Ita Ce Tushen Addini!

‘Yan-sha-biyu sun tafi a kan cewa, idan ana magana game da tushe da asalin addini, to, shugabanci na gaba ga komai. Mai littafin da muke magana a kansa ya ce, muhimmancin littafin nasa yana da girma saboda yana qunshe da bayanin manyan mas'aloli waxanda suka shafi hukunce-hukuncen addini da kuma sha'anin shugabanci, wanda ta hanyarsa ake kai wa ga daraja maxaukakiya don kasancewar sa xaya daga rukunan Imanin da ake samun shiga Aljanna da tsira daga dukan fushin Allah. A kan haka ne ma a cewarsa, Annabi Sallallahu Alaihi Wasallama ya ce: “Wanda duk mutuwa ta riske shi ba a qarqashin wani shugaba ba, to, ya yi mutuwar jahiliyyah”.

Marubucin ya nemi kusanci da rubuta littafin nasa ne zuwa ga wanda ya kira shi Sarkin Sarakuna Ulijayo Khudabandah, bayan ya yi masa yabo wanda ya wuce iyaka. Sannan ya sa masa suna "Minhajul Karamati Fi Ma'arifatil Imamati". Ya kuma yi masa tsarin fasali-fasali kamar haka:


  • Fasali na Xaya: Bayanin Mazhabobi game da wannan mas’ala.

  • Fasali na Biyu: Wajibi ne abi ra'ayin Shi’ah ‘yan-sha-biyuh ga wannan mas'ala.

  • Fasali na Uku: Dalilai masu tabbatar da shugabancin Aliyu Raliyallahu Anhu bayan rasuwar Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama.

  • Fasali na Huxu: Bayani a kan Imamai goma sha biyu.

  • Fasali na biyar: Kakkausan suka game da shugabancin Abubakar da Umar da Usman Raliyallahu Anhum.

Tun a karon farko maganarsa cewa, shugabanci shi ne tushe, kuma shi ne mafi girman mas'ala cikin lamurran addini a wajen Musulmi, wannan zancen banza ne. Kuma yarda da hakan kafirci ne. Domin yin Imani da Allah da Manzonsa na gaba ga sha’anin shugabanci. Wannan shi ne abin da Malaman Shi’a da kansu suka yi ijma'i a kansa balantana Malaman Sunnah. Wannan kuma abu ne da ya zama tilas kowa ya sani. Babban Misali shi ne Kalmar Shahada wadda ita ce babbar qofar shiga musulunci. Kuma a kanta ne aka yi xauki ba daxin duk da ya gudana a tsakanin musulmi da waxanda ba musulmi ba.

Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama ya ce: “An umurce ni da in yaqi mutane har sai sun sheda babu wanda ya cancanci bauta sai Allah. Su kuma shaida cewa, ni Manzon Allah ne. Su kuma tsayar da sallah, su ba da zakkah. Idan suka yi haka, sun kare jinainansu da dukiyoyinsu sai da dalili.

Haka kuma Allah Maxaukakin Sarki ya ce:

ﭽ ﮨ ﮩ ﮪ ﮫ ﮬ ﮭ ﮮ ﮯ ﮰ ﮱ ﯓ ﯔ ﯕ ﯖﯗ ﯘ ﯙ ﯚ ﯛ ﯜ ﯝ ﯞ ﯟﯠ ﯡ ﯢ ﯣ ﯤ ﯥ ﭼ التوبة: ٥



Kuma idan watanni masu alfarma suka shige to, ku yaqi Mushrikai inda duk kuka same su, kuma ku kama su ku zaune musu dukkan madakata. To, idan sun tuba, kuma suka tsayar da Sallah, kuma suka bayar da zakka, to, ku sakar musu da hanyarsu. Haqiqa, Allah mai gafara ne, mai jinqai. Suratut Taubah: 5

Kuma a lokacin da Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama ya naxa Aliyu Raliyallahu Anhu a matsayin kwamanda zuwa Haibara, farkon abin da ya umurce shi da shi, shi ne ya fara kiran mutane zuwa ga Imani da Allah da Manzonsa. Ka ga a nan bai ce masa ya kira su ga imani da shugabanci ba. Sa'annan a duk lokacin da Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama ya samu rinjaye a kan wasu kafirai, farkon abin da yake shimfixa masu shi ne Imani da Allah da Manzonsa.Wannan ita ce hanyar kiyaye alfarmar jini da dukiya. Wannan ya zo daidai da faxar Allah Maxaukakin Sarki:

ﭽ ﮘ ﮙ ﮚ ﮛ ﮜ ﮝ ﮞ ﮟ ﮠﮡ ﮢ ﮣ ﮤ ﮥ ﮦ ﭼ التوبة: ١١

Sa'anan idan sun tuba kuma suka tsayar da Sallah, kuma suka bayar da zakka, to ‘yan’uwanku ne a cikin addini. Suratut Taubah: 11

Dubi yadda Allah a nan ya ambace su a matsayin ‘yan’uwa a addini dalili da tubar da suka yi. Kuma a duk lokacin da wasu suka rungumi musulunci a hannun Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama, ba tare da wata-wata ba yakan karve su a cikin farin ciki hannu biyu-biyu ba tare da an tsaya bincike, ko nuna masu wani matsayi ba game da lamarin shugabanci. Bugu da qari, babu ko samatar samun wani Hadisi ko bayani wanda ke nuna buqatar yin hakan ga duk wanda ya karvi musulunci.

A zahiri wannan ya nuna babu hanyar da za a zagayo cikin Musulunci har a iya nuna cewa mas'alar shugabanci ita ce mafi zama a'ala a gefen girma da muhimmanci. Idan kuwa a lokacin da Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama yake raye lamarin shugabancin bai zama wani rukuni da saninsa yake wajibi ba, wane ne ya isa daga baya ya lizimtar da shi a matsayin rukunin addini?

Wata tambaya muhimmiya a nan ita ce, ashe akwai wasu mutane mafiya xaukaka da daraja fiye da jama'ar da suka rayu da Imaninsu tare da mafificin halitta Sallallahu Alaihi Wasallama? Domin kuwa ya aka yi su ba su xauki wannan mas’ala da girma ba? Ba su fahimta ba ne, sai ku a yanzu kuka samu fahimta?

Abin da ya kyautu a gane a nan shi ne, ko da an xauka cewa sha'anin shugabanci da matsayinsa zai yiwu ya canza salo daga zamani zuwa wani, to, xaukar sa a matsayin mafificin abu katovara ce ta kai tsaye. Domin kuwa babu lokacin da ya kamata shugabanci ya yi qima da alkadari kamar zamaninsa Sallallahu Alaihi Wasallama. idan ko har ba a bashi wannan matsayi ba a zamaninsa, to, ya ko za a yi ya samu wannan matsayi daga baya?

Amma abin da yake tabbas shi ne, ita mas'alar Imani da Allah da Manzonsa, a kowane zamani ko yanayi ita ce mafi muhimmanci a musulunci. Don haka, duk wanda ya iya shata wani lokaci da cewa shugabanci a cikinsa ya shiga gaban komi har Imani da Allah, to ya shigar da kansa a cikin sarqaqiya.

To, idan ma haka ne, cewa shugabanci shi ne tushe mafi girma a musulunci, ya aka yi Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama har ya bar duniya bai bayyana haka ba, kamar yadda ya bayyana matsayin Imani da Allah da ranar Lahira da Sallah da Azumi da Zakka da Ayyukan Hajji?! Kuma dukan waxannan abubuwa babu wani nassi wanda ya kusanci kwatanta su da matsayin shugabanci.

Idan kuma ‘yan Shi’ah suka dage a kan cewa lalle sha'anin shugabanci shi ne mafi muhimmanci har a zamanin Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama wai saboda ganin cewa shi Annabin ne da kansa yake shugaba kuma Manzo a lokaci guda, sai mu ce, to, saurari waxannan bayanan:


Bayani Na Xaya:

Ko da wannan ya inganta, to, ba zai yiwu a ce, shugabanci ne a gaban sahun sauran lamurran addini ba, sai dai ko a ce, a wasu lokuta yana da qarfin matsayi. To, kuma a lokacin da ya fi kowane daraja ba ta zama mafi muhimmanci ba, to, yaushe za ta zama?


Bayani Na Biyu:

Har abada imani da Allah da gasgata manzanni ya fi maganar shugabanci qarfi. Wannan ita ce aqidar musulmi.


Bayani Na Uku:

In da haka ne, da Annabi Sallallahu Alaihi Wasallama ya yi gaggawar sanar da al’ummarsa kamar yadda ya bayyana masu sauran addini.


1.6 Wane Shugabanci ne ya fi?

Shi wannan xan Shi’ar da ya tafi a kan cewar shugabanci shi ne lamari mafi muhimmanci ga addini muna bin sa bashin bayani. Shin yana nufin cewa shugabancin Imamansu goma sha biyu ne? Ko kuwa kowanne daga cikinsu shugabancinsa a zamaninsa? Ko dai yana nufin yarda da mas’alar baki xayanta? Ko kuma yana nufin wata ma’ana ce ta daban?

Idan yana nufin shugabancin sha biyu ne da suke cewa, to, ai a zamanin Sahabbai da Tabi’ai ba a san shi ba. Kuma ma su kansu ‘yan Shi’ar cewa suka yi ba a sanin kowane Imami sai na gaba da shi ya ayyana shi. To, ya imani da abin da yake haka ke zama wajibi ballantana mafi girman wajibai?

In kuma yana nufin imani ne da kowane Imami a lokacin bayyanarsa, to, kenan tun daga shekara ta 260H har zuwa yau kuma har abada imani da voyayyen Mahadin da ba a tava gani ko aka ji xuriyarsa ba, ya fi imani da Allah da Manzonsa?

In ko ya ce, a’a, shi fa yana maganar yarda da shugabanci ne a dunqule. Sai mu ce, wane irin dunqulallen abu ne wannan da ya zarce imani da Allah da Manzonsa, kuma ya fi sallah da azumi da zakkah da hajji? Ku dai sake tunani!

In ko kuna da wata ma’ana da kuke nufi, to, ku bayyana muna ita!

Bayan wannan ana iya tsokaci ga wani vangare mai qarfi ainun wajen ruguza wancan tunani, tsokacin shi ne, kasancewar ba a wajabta ma mutane biyayya ga Annabi Sallallahu Alaihi Wasallama ba saboda kawai yana a matsayin shugaba, amma an wajabta haka ne saboda matsayinsa na Manzon Allah zuwa ga mutanen duniya baki xaya. Wannan shi ne matsayin da har qasa ta naxe ba zai canza ba. Kuma shi ne babban dalilin da ya sa xa'a zuwa gare shi a cikin kowane zamani ta zama tilas ga waxanda suka rayu tare da shi da waxanda suka zo bayan rayuwarsa.

Bayanai da dama ne za su iya qarfafa abin da ya gabata. Domin akwai yanayin da Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama zai yi umurni ko ya zartar da hukunci ga wani mutum guda ko wasu mutane, amma duk da haka sai hukuncin ya zarce ya shafi kowa da kowa. Kamar dai a lokacin da ya gargaxi wasu daga cikin Sahabbansa Allah ya yarda da su inda ya ce musu: “Kada ku rigaye ni yin ruku'i da Sujada”. Ka ga wannan hukuncin bai tsaya a kan waxancan jama'a kawai ba. A madadin haka, hukuncin ya shafi duk wani masallaci da ke koyi da liman a halin yin Sallah.

Haka kuma a wani lokaci wani ya yi wa Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama tambaya game da aikin Hajji cewa, na gabatar da yin aski kafin yin jifa a cikin rashin sani. Sai ya amsa masa da cewa: “Jifarka ta yi daidai”. To, shi ma wannan hukunci irin wancan ne; bai tsaya a kan mai tambayar kawai ba, a'a. Duk wanda ya sami kansa cikin irin wannan hali babu laifi a kansa.

Ga kuma qarin wani misali wanda a lokacin da jinin Haila ya riski uwar muminai Aisha Raliyallahu Anhu alhali tana cikin harama da Umrah, sai ya ce mata: “Ki ci gaba da sauran ayyukanki na Hajji, xawafi ne kawai ba zaki yi ba”. Ire-iren waxannan misalai su ke nuna banbancin da ke tsakanin biyayyar da ake yi wa Annabawa, da irin wadda ake ma Sarakuna da shugabannin siyasa a kowane zamani.

A gefen halifofin Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama kuwa, musamman waxanda suka biyo bayan wafatinsa, ba su banbanta ba daga wakillansa na zamanin rayuwarsa, a inda za ka tarar cewa, da zarar wani wakili ya ba da umurni, xa'a a gare shi ta zama wajibi. Dalili kuwa shi ne, umurnin nasa tamkar na Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama ne. Allah Maxaukakin Sarki ya ce:

ﭽ ﭳ ﭴ ﭵ ﭶ ﭷ ﭸ ﭹ ﭺ ﭻﭼ ﭽ ﭾ ﭿ ﮀ ﮁ ﮂ ﮃﮄ ﮅ ﮆ ﮇ ﮈ ﮉ ﮊ ﮋ ﮌﮍ ﮎ ﮏ ﮐ ﮑﭼ آل عمران: ١٤٤



Kuma Muhammadu bai zama ba face Manzo, Lalle ne Manzanni sun shuxe a gabaninsa. Ashe idan ya mutu ko kuwa aka kashe shi, za ku juya a kan dugaduganku? To, wanda ya juya a kan dugadugansa, ba zai cuci Allah da kome ba. Kuma Allah zai saka wa masu godiya.

Wannan ayar ta fayyace cewa, mutuwar Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama ba za ta dakatar da matsayinsa na Manzo ba. Amma yanzu da zarar wani basarake ko shugaba ya wuntsile ya mutu, sai a xauki muqaminsa a naxa wa wani domin shi an rufe nasa faifan, ya gama nasa ya yi kenan.

Haqiqa Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama ya isar da Mazanci, ya kiyaye amana tare da shimfixa adalci, ya baza nasiha cikin al'umma, ya taimaki addinin Allah da gaske, kuma ya kafu ga bautar Allah. Haka lamarinsa ya kasance har ya koma ga Mahaliccinsa. Wannan Shi ya sa xa'a gare shi ta zama dole, yana raye ko bayan wafatinsa. Domin bayan rasuwarsa addinin Musulunci bai buqaci wani ragi ko qari ba, kuma wannan shi ne musabbabin zaburar Sahabbai Allah ya yarda da su wajen tattara Al-qur'ani mai girma a waje xaya.

Amma kuma duk da haka, wani na iya shan iska ya ce, ai shi Annabin da kansa ya zama shugaba ne kawai a halin da yake raye, domin kuwa bayan rasuwarsa shugabanci ya koma ne a wuyan wani wanda ba shi ba. Mu kuma sai mu ce masa, kana so ne ka ce bayan rasuwarsa akwai mutumin da ake yi wa biyayya kamar yadda ake yi masa? Idan wannan ita ce manufarka, ai kuwa kowa ya sheda cewa wannan maganar wofi ce. Idan kuma yana so ne ya ce, yana nufin bayan wucewarsa an samu wakilinsa wajen zartas da lamurran da suka shafi umurni da haninsa, sai a ce da shi wannan ba baquwar magana ba ce, saboda ko a lokacin da yake raye ba baqon abu ba ne cewa, yana wakilta wani musamman lokacin da zai yi wata tafiya.

In aka ce, Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama ba ya umartar wani bayan rasuwarsa, amma lokacin rayuwarsa yana yin haka. Sai mu ce, umurnin Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama da ya bayar a lokacin rayuwarsa yana wajaba a yi masa xa'a ga wanda ya ji shi kai tsaye, da wanda maganar ta kai gare shi daga baya. Daman ko ai Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama ya ce: “Wanda duk ya halarci maganata ya isar da ita ga wanda bai halarta ba. sau da yawa wanda aka isar wa da saqo yakan fi wanda ya isar kiyaye saqon".

In an ce lokacin da yake raye yana hukunci a kan hukunce-hukunce na musamman, misalinsa shi ne; ba wani mutum kyauta, da zartar da haddi a kan wani mutum, da aika wasu sanannun mayaqa zuwa wani wuri. Sai a ce haka yake. Yi wa Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama xa'a wajibi ne ga abubuwan da ke kama da haka har ranar qiyama, savanin shugabanni. kodayake mai yiwuwa kafa dalili a kan abin da ya yi kama da wannan, zai iya wuyata. Kamar yadda ilimin abu na voyuwa ga wanda bai halarci abin da Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama ya faxa ba.

Wanda ya halarci abu shi ya fi sanin abin da Manzo ya faxa, kuma ya fi wanda bai halarta ba fahimta, kodayake ana iya samun waxansu da aka isar da saqon gare su, su fi waxanda suka ji maganarsa kiyaye umurnisa. Wannan fifikon tsakanin mutane yana da nasaba da sanin umurni ko hanin da Manzo ya yi ne kawai. Amma ba shi da wata alaqa da fifikon wajabcin yi wa Manzo xa'a.

Babu banbanci tsakanin wajabcin yi wa shugabanni xa'a a rayuwar Manzo, da yi masu ita bayan rasuwarsa. Wajabcin yi masa xa’ar ya game duk bayi bai xaya. Kodayake ana samun banbanci wajen hanyar isar da saqon, jinsa da fahimtar sa, wasu na samun saqon manzo game da wani lamari, wasu kuma su sami wani saqon nasa wanda wasu ba su samu ba. Saboda haka mutanen farko na fahimtar wani lamari nasa wanda mutane na biyu Ba su fahimta ba. Duk wanda ya yi umurni da abin da Manzo ya yi umurni da shi, to, ya wajaba a yi masa xa'a don biyayya ga Allah da Manzonsa, ba don xa'a ga wanda ya yi umurnin ba.

Idan mutane nada shugaba mai qarfi wanda ke umurni da abin da Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama ya yi umurni da shi, kuma yake hukunci da irin hukuncinsa, to, lamurransu za su daidaita. Saboda haka ba ya halalta a sa wani shugaba ba shi ba. Ba ya yiwuwa a samu wani mutum kamar sa bayan wucewar sa, ana dai samun wanda ya yi kusa da shi, wanda ya fi cancanta ya zama mai maye wurin Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama, saboda ya fi kusanci ga yin umurni da abin da Manzo yake umurni da shi da kuma hani ga abin da Manzo ya yi hani da shi.

Sanannen abu ne cewa, ba a cika yin xa'a ba ga umurninsa a mafi yawan lokuta sai in ya kasance mai cikakken qarfi da ikon da zai tilasta ma jama’a yin xa'a. Don haka dole ne ya kasance ya samu waxanda suka saxaukar da rayukansu don tabbatar da an yi masa xa'a. Addini dai dukansa xa'a ne ga Allah da Manzonsa. Duk wanda ya yi wa Manzon Allah xa'a to ya yi wa Allah xa'a.

Addinin Musulunci ko bayan rasuwar Manzo, yana nan a matsayinsa na xa'a ga Allah da Manzonsa. Xa'a ga shugabanni a cikin abin da Shari'ah ta ce ayi musu xa'a, shi ma xa'a ne ga Allah da Manzonsa.

Wannan ne ya sa tushen addini shi ne gasgata cewa, babu wanda ya cancanci bauta in ba Allah ba, da kuma cewa Muhammadu Sallallahu Alaihi Wasallama Manzon Allah ne.

Idan Shi’a ‘yan-sha-biyu sun ce: Hankali ya nuna wajabcin shugabanci, amma bai nuna Manzanci ba. Saboda haka shugabanci ya fi muhimmanci ta wannan fuskar. Sai a ce masu: to, ai ba gaba xayan malamai ne suka yarda da cewa, hankali na wajabta wani abu ba. To, in ma mun yarda da waxanda suka ce hankali na wajabta haka, sai mu ce abin da hankali ke wajabtawa na al'amarin shugabanci, kaxan ne cikin al’amurra na hankali. Don ko ai hankali ya yarda da kaxaita Allah da bauta, kamar yadda ya yarda da faxin gaskiya, adalci da makamantansu.

Haka kuma, duk wanda ta tabbata wurinsa cewa Muhammadu Manzon Allah ne, kuma ta tabbata cewa yi masa xa'a wajibi ne a kansa, ya kuma yi iyakar qoqarinsa wurin yin masa xa'a gwargwadon iko, Tabbas wannan zai shiga aljanna bai da buqata zuwa ga matsalar shugabanci. Duk ko wanda ya ce mai irin wannan ingantattar aqida ba zai shiga Aljanna ba, to, yana ban hannun makaho da nassoshin Al-qur'ani. Don ko sanannen abu a musulunci shi ne cewa, Allah ya wajabtar da Aljanna ga wanda ya yi imani da Allah da Manzo kuma ya yi musu xa’a.

Allah Maxaukakin Sarki ya ce:

ﭽ ﭹ ﭺ ﭻ ﭼ ﭽ ﭾ ﭿ ﮀ ﮁ ﮂ ﮃ ﮄ ﮅ ﮆ ﮇﮈ ﮉ ﮊ ﮋ ﮌ ﭼ النساء: ٦٩



Duk wanda ya yi wa Allah xa'a da Manzonsa waxannan suna tare da waxanda Allah ya yi ma ni'ima na daga cikin Manzanni da Shahidai da Salihai. Waxannan abokan arziki. Suratun-Nisa'i: 13

Shi dai Mahadin naku, mutane ba su da hanyar sanin sa, kuma ba hanyar sanin abin da yake umurni da shi da abin da yake hani da shi, da labaran da yake bayarwa. Idan mutum ba zai sami tsira ba sai ya yi wa irin wannan Mahadin naku xa’a, duk da yake ba a iya sanin me yake umurni kuma me yake hani, kenan babu wanda zai kai ga hanyar tsira.

In sun ce abin ba haka yake ba, domin idan Mahadin ya bayyana zai ba da umurnin a yi abin da ‘yan Shi’ar sha biyu suke a kai. Sai a ce: to babu buqatar kasancewarsa kenan. Domin abin da ‘yan Shi’ah ke a kai sananne ne ko da shi Mahadin ko babu shi. Daga nan za a san cewa, babu buqata ga samuwarsa. Kuma xa'a ga Allah ba ta rataya a kansa ba, balle samun tsira. Anan ne muke cewa, ba shi halasta iqirarin shugabancin irin wannan mutum, ballantana a ce wajibi ne a yarda da shi a matsayin haka. Wannan abu ne da yake bayyane ga wanda ya yi tunani amma 'yan Shi’ah sun fi kowa jahilci don ba su tunani.

A kan haka, babu dalilin da zai sa 'yan Shi’ah su rataya tsirar halittar Allah a kan wannan aqida ta Mahadi. Musamman da yake yau da gobe ta tabbatar da kasancewar ta tatsuniya.

Idan kuwa har suka nace a kan haka, to, lalle ne xayan abubuwa biyu zai tabbata. Wato maganarsu ta zama qarya muraran bisa hujjojin da muka gabatar. Ko kuma kamar suna cewa ne Allah Maxaukakin Sarki ya haramta wa bayinsa samun rahamarsa, qarshe kuma zai tattara su ya zuba wuta. Idan kuwa har haka ta tabbata to, su ne farkon waxanda suka tave, waxanda kuma za a azabtar, don ba su da wata masaniya da komai daga Mahadin nasu balle su nemi tsira. Iyakar abin da suka sani ‘yan riwayoyi ne daga malamansu da ba su taka kara sun karya ba dangane da shi.

In ko har wani xan Shi’a ya ce mana ya riwaito wani abu daga wurin wannan Mahadin to, tabbas shi maqaryaci ne.

Na ga wasu Malaman Shi’ah kamar Ibnul-Udi Al-hilli yana cewa: “Idan ‘yan Shi’ah suka yi savani game da wani abu a kan ra’ayi biyu, to, duk ra’ayin da ba a san mai shi ba shi ne gaskiya, don kuwa Mahadinmu yana a cikin sa”.

Wannan ita ce magaryar tuqewa ta jahilci da vata. Domin ko me zai hana in har akwai Mahadin ya zan yana cikin masu xaya ra’ayin, amma ba a faxe shi ba don ba a gan shi ba balle aji ra’ayinsa?

Asalin da ‘yan-sha-biyu suka gina addininsu a kai shi ne, abin da ba a sani ba da abin da babu shi. Suna zaton cewa, wannan shugaban nasu akwai shi kuma ba ya kuskure, alhali kuwa ba a san inda yake ba, kuma babu shi, da kuma shi samamme ne wanda ba ya kuskure, su ma sun yarda cewa, ba a iya sanin umurninsa da haninsa, tun da ba a ganin shi.

A kan haka babu yadda ‘yan-sha-biyu za su yi su tabbatar mana da wanzuwar wannan Mahadi balle shugabancinsa. Dalili kuwa shi ne shugaba, wato Imami, na karva wannan suna ne, a lokacin da ake iya saduwa da shi, ya kuma yi umurni a bi, ko dole. Idan kuwa haka ta faskara, to, duk wata hanya da za a bi don tabbatar da wanzuwar sa waqa ce kawai da baqar wahala. Kuma gaba xayan malaman Shi’ah ba su musun haka. Domin sun tafi tare da malaman da suka yarda da cewa, hankali na iya sanin abu mai kyau da mummuna.

In waxannan Shi’a ‘yan-sha-biyu suka ce, imaninmu da wannan ma'asumi da ake jira kamar imanin da ‘yan xariqa ke yi ne, game da Ilyasu, da Khadir, da Gausi da Quxubi da mutanen gaibi, waxanda ba a tabbatar da samuwarsa ba balle a san abin da suke umurni da hani. Duk wanda ya yarda da mutanen da aka ambata xin nan ba zai qi yarda da samuwar Mahadinmu ba.

To, bari mu ba ku amsa ta fuskoki kamar haka:


Yüklə 2,75 Mb.

Dostları ilə paylaş:
1   2   3   4   5   6   7   8   9   ...   51




Verilənlər bazası müəlliflik hüququ ilə müdafiə olunur ©muhaz.org 2024
rəhbərliyinə müraciət

gir | qeydiyyatdan keç
    Ana səhifə


yükləyin